< 2 Samuel 20 >

1 And there happened to be a worthless man, whose name was Sheba', the son of Bichri, a Benjamite; and he blew the cornet, and said, We have no part in David, nor have we any inheritance in the son of Jesse: every man to his tents, O Israel!
Akwai wani mai tā-da-na-zaune-tsaye, sunansa Sheba, ɗan Bikri, daga kabilar Benyamin, a wurin. Sai ya busa ƙaho, ya yi ihu ya ce, “Ba mu da rabo a wurin Dawuda, ba mu da sashe a wurin ɗan Yesse! Kowa yă nufi tentinsa, ya Isra’ila!”
2 So every man of Israel went off from David, following Sheba' the son of Bichri; but the men of Judah adhered unto their king, from the Jordan even to Jerusalem.
Saboda haka dukan mutane Isra’ila suka bar Dawuda don su bi Sheba ɗan Bikri. Amma mutanen Yahuda suka kasance a wurin sarki tun daga Urdun har zuwa Urushalima.
3 And David came to his house at Jerusalem; and the king took the ten women, the concubines, whom he had left to guard the house, and put them in a guard-house, and provided for them, but went not in unto them. So they were confined until the day of their death, living in widowhood.
Da Dawuda ya komo fadarsa a Urushalima, sai ya ɗauko ƙwarƙwaran goma nan da ya bari su lura da fada, ya keɓe su a wani gida inda za a yi tsaronsu. Ya tanada musu, amma bai kwana da su ba. Aka sa su a keɓe har iyakar rayuwarsu, suka yi zama kamar gwauraye.
4 Then said the king to 'Amassa, Call together for me the men of Judah within three days, and thou present thyself here [then].
Sa’an nan sarki ya ce wa Amasa, “Ka tattaro mutanen Yahuda su zo wurina cikin kwana uku, kai kuwa ka kasance a can kai kanka.”
5 So 'Amassa went to call Judah together; but he remained out longer than the set time which he had appointed him.
Amma da Amasa ya tafi kiran mutanen Yahuda, ya ɗauki lokaci fiye da lokacin da sarki ya ba shi.
6 And David said to Abishai, Now will Sheba' the son of Bichri do us more harm than [did] Abshalom: take thou the servants of thy Lord, and pursue after him, lest he succeed in reaching fortified cities, and withdraw himself from our eyes.
Dawuda ya ce wa Abishai, “Ina gani Sheba ɗan Bikri zai ba mu wuya fiye da Absalom. Ka ɗauki mutanen maigidanka ka fafare shi, don kada yă sami garuruwa masu katanga yă tsere mana.”
7 And there went out after him Joab's men, and the Kerethites, and the Pelethites, and all the mighty men: and they went forth out of Jerusalem, to pursue after Sheba' the son of Bichri.
Saboda haka mutanen Yowab da Keretawa da Feletiyawa da dukan jarumawa suka fita a ƙarƙashin Abishai. Suka fita daga Urushalima don su fafari Sheba ɗan Bikri.
8 They were close by the great stone which is at Gib'on, as 'Amassa came before them. And Joab was girded with his coat, his [usual] garment, and upon it the girdle of the sword which was fastened upon his loins in its sheath; and as he went forth it fell out.
Yayinda suke a babban dutse a Gibeyon, Amasa ya zo don yă tarye su. Yowab kuwa yana sanye da doguwar rigar soja, a ɗamarar da ya sha kuwa akwai wuƙa a cikin kube. Da ya zo gaba sai wuƙar ta zāre daga kube ta fāɗi.
9 And Joab said to 'Amassa, Art thou in health, my brother? And Joab's right hand took hold of 'Amassa's beard to kiss him.
Yowab ya ce wa Amasa, “Yaya kake, ɗan’uwana?” Sai Yowab ya kama gemun Amasa da hannun dama don yă yi masa sumba.
10 And 'Amassa did not guard himself against the sword that was in Joab's hand: so he smote him therewith in the fifth rib and shed out his bowels to the ground, and struck him not again; and he died. But Joab and Abishai his brother pursued after Sheba' the son of Bichri.
Amasa kuwa bai lura da wuƙar da take hannun Yowab ba, Yowab kuwa ya soke shi da wuƙar a ciki, hanjinsa suka zube ƙasa. Ba tare da ƙarin suƙa ba, Amasa ya mutu. Sa’an nan Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka fafari Sheba ɗan Bikri.
11 And one man of Joab's people remained standing by him, and said, He that favoreth Joab, and he that is for David, follow Joab.
Ɗaya daga cikin mutanen Yowab ya tsaya kusa da Amasa ya ce, “Duk mai son Yowab, kuma duk mai son Dawuda, yă bi Yowab!”
12 And 'Amassa was wallowing in his blood in the midst of the highway. And when the man saw that all the people stood still, he put 'Amassa aside out of the highway into the field, and threw a garment over him, when he saw that every one that came by him stood still.
Amasa kuwa yana kwance cikin tafkin jininsa a kan hanya, sai mutumin ya ga dukan sojoji suka zo suka tsaya cik a can. Da ya gane cewa duk wanda ya haura zuwa wurin Amasa sai ya tsaya, sai ya ja gawar Amasa daga hanyar ya kai can cikin wani fili ya rufe shi da zane.
13 When he was removed out of the highway, every man passed on after Joab, to pursue after Sheba' the son of Bichri.
Bayan an ɗauke Amasa daga hanya, sai dukan mutane suka bi Yowab don fafaran Sheba ɗan Bikri.
14 And this one passed through all the tribes of Israel unto Abel, which is of Beth-ma'achah, and all the Berim: and they assembled themselves together, and went also after him.
Sheba ya bi ta dukan kabilan Isra’ila zuwa Abel da kuma ta dukan yankin Beriyawa, waɗanda suka taru suka bi shi.
15 And they came and besieged him in Abel of Beth-ma'achah, and they cast up a trench against the city, and it stood enclosed by the troops: and all the people that were with Joab were battering to throw down the wall.
Sai dukan rundunonin da suke tare da Yowab suka zo suka yi wa Sheba kwanton ɓauna a Abel-Bet-Ma’aka. Suka tara ƙasa kewaye da jikin katangar birnin daidai da tsayinta. Sa’an nan waɗansu kuma suna ƙoƙarin rushe katangar.
16 Then called a wise woman out of the city, Hear, hear: say, I pray you, unto Joab, Come near as far as hither, that I may speak with thee.
Sai wata mata mai hikima ta yi kira daga ciki birnin ta ce, “Ku saurara! Ku saurara! Ku gaya wa Yowab yă zo nan ina so in yi magana da shi.”
17 And when he was come near unto her, the woman said, Art thou Joab? And he said, I am. Then said she unto him, Hear the words of thy hand-maid. And he said, I do hear.
Ya tafi wurinta, sai ta ce, “Kai ne Yowab?” Ya ce, “Ni ne”. Ta ce, “Ka ji abin da zan ce maka.” Ya ce, “Ina jinki.”
18 Then said she, thus, They ought surely first to have spoken, saying, “Let them ask at least in Abel:” and so would they have come to an end.
Ta ci gaba ta ce, “A dā can, akan ce, ‘Sami amsarka a Abel,’ shi ke nan an gama.
19 I am one of the peaceful and faithful [cities] in Israel; thou seekest to overthrow a city and a metropolis in Israel: why wilt thou destroy the inheritance of the Lord?
Mu ne masu salama da kuma amintattu na Isra’ila. Kana ƙoƙari ka hallaka birnin da yake uwa a Isra’ila. Don me kake so ka hallakar da gādon Ubangiji?”
20 And Joab answered and said, Far be it, far be it from me, that I should destroy or ruin.
Yowab ya ce, “Allah yă sawwaƙe! Allah yă sawwaƙe in hallaka, ko in lalace gādon Ubangiji.
21 The matter is not so; but a man from the mountains of Ephraim, Sheba' the son of Bichri is his name, hath lifted up his hand against the king, against David: give him up alone, and I will withdraw from the city. And the woman said unto Joab, Behold, his head shall be cast down to thee over the wall.
Ba haka ba ne batun. Wani mai suna Sheba ɗan Bikri ne, daga ƙasar tudun Efraim, ya tayar wa sarki, yana gāba da Dawuda. Ki ba mu wannan mutum, zan kuwa janye daga birnin.” Matar ta ce wa Yowab, “Za a jefa maka kansa daga katanga.”
22 And the woman came unto all the people with her wisdom; and they cut off the head of Sheba' the son of Bichri, and cast it down to Joab: and he blew the cornet, and they scattered themselves from the city, every man to his tents. And Joab returned to Jerusalem unto the king.
Sa’an nan matar ta tafi wurin dukan mutane da shawararta mai hikima, sai suka datse kan Sheba ɗan Bikri suka jefa wa Yowab. Saboda haka sai ya busa ƙaho, mutanensa kuwa suka watse daga birnin, kowa ya koma gidansa. Yowab kuma ya koma wurin sarki a Urushalima.
23 Now Joab was over all the army of Israel; and Benayah the son of Yehoyada' was over the Kerethites and over the Pelethites;
Yowab ne yake shugabancin dukan rundunoni; Benahiya ɗan Yehohiyada ne yake shugabancin Keretawa da Feletiyawa;
24 And Adoram was over the tribute; and Jehoshaphat the son of Achilud was recorder;
Adoniram kuwa shi ne shugaban aikin gandu; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubucin tarihi;
25 And Sheva was scribe; and Zadok and Ebyathar were priests;
Shewa kuwa magatakarda; Zadok da Abiyatar su ne firistoci;
26 And 'Ira also the Yairite was an officer of state unto David.
Ira mutumin Yayir kuwa shi ne firist na Dawuda.

< 2 Samuel 20 >