< 2 Samuel 2 >

1 And it came to pass after this, that David asked counsel of the Lord, saying, Shall I go up into one of the cities of Judah? And the Lord said unto him, Go up. And David said, Whither shall I go up? And he said, Unto Hebron.
Bayan’yan kwanaki, sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In haura zuwa ɗaya daga cikin biranen Yahuda?” Ubangiji ya ce, “Haura.” Dawuda ya ce, “Wanne zan tafi?” Ubangiji ya ce, “Je Hebron.”
2 So David went up thither, and his two wives also, Achino'am the Yizre'elitess, and Abigayil, Nabal's wife, the Carmelite.
Saboda haka sai Dawuda ya tafi can tare da matansa biyu, Ahinowam daga Yezireyel da Abigiyel gwauruwar Nabal mutumin Karmel.
3 And his men that were with him did David bring up, every man with his household; and they dwelt in the cities of Hebron.
Dawuda kuma ya tafi tare da dukan mutanen da suke tare da shi, kowa da iyalinsa, suka zauna a Hebron da garuruwansa.
4 And then came the men of Judah, and they anointed there David as king over the house of Judah. And they told David, saying, The men of Yabesh-gil'ad were those that buried Saul.
Sa’an nan mutanen Yahuda suka zo Hebron, a can kuwa suka naɗa Dawuda sarkin Yahuda. Sa’ad da aka gaya wa Dawuda cewa mutanen Yabesh Gileyad ne suka binne Shawulu,
5 And David thereupon sent messengers unto the men of Yabesh-gil'ad, and said unto them, Blessed be ye of the Lord, that ye have done this kindness unto your Lord, unto Saul, and have buried him.
sai ya aiki manzanni zuwa Yabesh Gileyad a ce musu, “Ubangiji yă albarkace ku saboda alherin da kuka nuna wa Shawulu ta wurin binne shi.
6 And now may the Lord deal with you in kindness and truth: and as for me also, I will requite you this good deed, because ye have done this thing.
Bari Ubangiji yă nuna muku ƙaunarsa da amincinsa, ni kuma zan nuna muku irin wannan alherin saboda kun yi haka.
7 And now let your hands be strengthened, and be ye valiant men; for your lord Saul is dead; and also me have the house of Judah anointed as king over them.
Yanzu fa, sai ku ƙarfafa, ku yi jaruntaka, gama Shawulu sarkinku ya mutu, gidan Yahuda kuwa sun naɗa ni sarki a kansu.”
8 But Abner, the son of Ner, the captain of the army of Saul, took Ish-bosheth the son of Saul, and brought him over to Machanayim;
Ana cikin haka, Abner ɗan Ner, komandan sojojin Shawulu, ya ɗauki Ish-Boshet ɗan Shawulu ya kawo shi Mahanayim.
9 And made him king over Gil'ad, and over the Ashurites, and over Yizre'el, and over Ephraim, and over Benjamin, and over all Israel.
Ya naɗa shi sarkin Gileyad, da na Ashuri, da na Yezireyel, da a kan Efraim, da Benyamin, da kuma na dukan Isra’ila.
10 Forty years old was Ish-bosheth the son of Saul, when he became king over Israel, and two years he reigned. But the house of Judah followed David.
Ish-Boshet ɗan Shawulu yana da shekaru arba’in sa’ad da ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi sarauta shekara biyu. Amma fa, gidan Yahuda, suka bi Dawuda.
11 And the number of days that David was king in Hebron over the house of Judah was seven years and six months.
Tsawon lokacin da Dawuda ya yi mulki a Hebron a kan gidan Yahuda, shekara bakwai ne da wata shida.
12 And there went out Abner the son of Ner, and the servants of Ish-bosheth the son of Saul, from Machanayim to Gib'on.
Abner ɗan Ner, tare da mutanen Ish-Boshet ɗan Shawulu, suka bar Mahanayim suka tafi Gibeyon.
13 And Joab the son of Zeruyah and the servants of David also went out, and they met together by the pool of Gib'on: and they sat down, these on the one side of the pool, and the others on the other side of the pool.
Yowab wanda ake ce mamarsa Zeruhiya tare da waɗansu mutanen Dawuda suka fito suka haɗu da su tafkin Gibeyon, Suka zauna, waɗannan a wannan gefe, waɗancan a wancan gefe.
14 And Abner said to Joab, Do let the young men rise up and play before us. And Joab said, They may rise up.
Sa’an nan Abner ya ce wa Yowab, “Bari mu bar waɗansu samari su tashi su yi faɗa hannu da hannu a gabanmu.” Yowab ya ce, “To, su tashi.”
15 Then they rose up and went over by number: twelve for Benjamin, and for Ish-bosheth the son of Saul, and twelve of the servants of David.
Saboda haka samarin suka tashi aka ƙidaya su, mutum sha biyu wajen Benyamin da Ish-Boshet ɗan Shawulu, sha biyu kuma wajen Dawuda.
16 And they grasped every one his fellow by the head, and thrust his sword in his fellow's side; and they fell down together: wherefore that place was called Chelkath-hazzurim, which is by Gib'on.
Sa’an nan kowannensu ya kama abokin gābansa a kā ya soki da wuƙa a jiki, sai duka suka fāɗi a ƙasa. Saboda haka ne ake kiran wannan wuri Helkat Hazzurim a Gibeyon.
17 And the battle was exceedingly fierce on that day; and Abner with the men of Israel was beaten, before the servants of David.
Faɗan ya yi zafi a ranar ƙwarai, mutanen Dawuda suka ci mutanen Abner da na Isra’ila.
18 And there were at that place three sons of Zeruyah, Joab, and Abishai, and 'Asahel: and 'Asahel was as fleet of foot as any roe in the field.
’Ya’yan Zeruhiya, maza uku sun kasance a can. Su ne, Yowab, Abishai da Asahel. To, Asahel mai gudu ne kamar barewa.
19 And 'Asahel pursued after Abner; and he turned not in going to the right hand or to the left from following Abner.
Ya fafari Abner, bai juya dama ko hagu ba, yayinda yake fafararsa.
20 And Abner turned round and said, Art thou 'Asahel? And he answered, I am.
Abner ya waiga, sai ya ce, “Kai ne, Asahel?” Ya ce, “Ni ne.”
21 And Abner said to him, Turn thee aside to thy right hand or to thy left, and lay hold for thyself on one of the young men, and take thyself his armor. But 'Asahel would not turn aside from following him.
Sai Abner ya ce masa, “Yi dama ko hagu ka runtumi ɗaya daga cikin samarin, ka ƙwace makamansa.” Amma Asahel bai bar fafararsa ba.
22 And Abner repeated again to say unto 'Asahel, Turn thee aside from following me: wherefore should I smite thee to the ground? and how should I then lift up my face to Joab thy brother?
Abner ya sāke gargaɗe shi ya ce, “Ka bar fafarata! Yaya zan kashe ka? Yaya zan yin ido biyu da ɗan’uwanka Yowab?”
23 But he refused to turn aside; and Abner smote him with the hinder end of the spear under the fifth rib, so that the spear came out behind him; and he fell down there, and died on the spot: and it came to pass, that all who came to the place where 'Asahel had fallen down and died remained standing still.
Amma Asahel ya ƙi yă bar fafararsa; saboda haka Abner ya soki Asahel da māshinsa a ciki; har māshin ya fita ta bayansa. Nan take ya fāɗi, ya mutu. Kowa da ya zo wurin da Asahel ya fāɗi, ya mutu, sai yă tsaya.
24 But Joab and Abishai pursued after Abner: and the sun went down when they were come to the hill of Ammah, that lieth before Giach on the way to the wilderness of Gib'on.
Amma Yowab da Abishai suka fafari Abner, kuma da rana tana fāɗuwa sai suka iso tudun Amma, kusa da Giya, a hanyar zuwa jejin Gibeyon.
25 And the children of Benjamin assembled themselves together behind Abner, and formed one solid body, and posted themselves on the top of a certain hill.
Sa’an nan mutanen Benyamin suka haɗa kansu suka koyi bayan Abner. Suka zama ƙungiya guda, suka tsaya daram a kan tudu.
26 And Abner called to Joab, and said, Shall for everlasting the sword devour? knowest thou not that it will be bitter in the end? and how long shall it be, ere thou wilt bid the people to return from pursuing their brethren?
Sai Abner ya kira Yowab ya ce, har abada ne māshi zai yi ta hallakarwa? Ba ka sani cewa ƙarshen zai zama da ɗaci ba. Sai yaushe za ka umarci mutanenka su daina fafaran’yan’uwansu?
27 And Joab said, As God liveth, unless thou hadst spoken, surely then already in the morning would the people have gone away every one from pursuing his brother.
Yowab ya ce, “Muddin Allah yana a raye, da ba a ce ka yi magana ba, da mutanen za su ci gaba da fafaran’yan’uwansu har gari yă waye.”
28 So Joab blew the cornet, and all the people remained standing still, and pursued no more after Israel, and they continued no more to fight.
Sai Yowab ya busa ƙaho, dukan mutane kuwa suka tsaya; suka daina fafaran Isra’ila. Nan take faɗan ya tsaya.
29 And Abner and his men walked through the plain all that night, and they passed over the Jordan, and went through all Bithron, and they came to Machanayim.
Abner da mutanensa suka ratsa kwarin Urdun dukan dare. Sa’an nan suka haye kogin, suka kuwa ci gaba dukan safe har suka zo Mahanayim.
30 And Joab returned from pursuing Abner; and he gathered all the people together; and there were missed of David's servants nineteen men and 'Asahel.
Da Yowab ya dawo daga fafaran Abner, sai ya tattara dukan mutanensa. Ban da Asahel, sai ya gane an rasa mutum goma sha tara na Dawuda.
31 But the servants of David had smitten [many] of Benjamin, and of Abner's men: three hundred and sixty men died.
Amma mutanen Dawuda sun kashe mutum ɗari uku da sittin daga kabilar Benyamin da suke tare da Abner.
32 And they took up 'Asahel, and buried him in the sepulchre of his father, which was in Beth-lechem. And Joab and his men went all that night, and the day broke on them at Hebron.
Suka ɗauki gawar Asahel suka binne a kabarin mahaifinsa a Betlehem. Sa’an nan Yowab da mutanensa suka bi dare har suka iso Hebron da safe.

< 2 Samuel 2 >