< 2 Kings 6 >

1 And the sons of the prophets said unto Elisha', Behold now, the place where we dwell before thee is too narrow for us.
Sai ƙungiyar annabawa suka ce wa Elisha, “Duba, wurin da muke taruwa ya kāsa mana.
2 Let us go, we pray thee, as far as the Jordan, and take thence every man one beam, and let us prepare for us there a place to dwell therein. And he said, Go.
Bari mu je Urdun, inda kowannenmu zai saro itace; mu gina inda za mu zauna.” Sai ya ce musu, “Ku je.”
3 And one said, Give thy assent, I pray thee, and go with thy servants. And he said, I will indeed go.
Sai ɗayansu ya ce, “Ba za ka zo tare da bayinka ba?” Sai Elisha ya ce “Zan zo.”
4 So he went with them; and they came to the Jordan, and they cut down trees.
Ya kuma tafi tare da su. Suka tafi Urdun suka fara saran itatuwa.
5 But as one was felling a beam, the axe-head fell into the water: and he cried, and said, Alas, my Lord! it was also borrowed.
Yayinda ɗayansu yake cikin saran itace, sai kan gatarin ya fāɗi a ruwa, sai ya ce, “Kash, ranka yă daɗe, kayan aro ne fa!”
6 And the man of God said, Where did it fall? And he showed him the place. And he cut down a stick, and cast it in thither, and he caused the iron to swim.
Sai mutumin Allah ya ce, “Daidai ina ya fāɗa?” Da ya nuna masa wurin, sai Elisha ya yanka ɗan sanda ya jefa a wurin, ya sa kan gatarin ya taso sama.
7 And then said he, Lift it up to thee. And he stretched out his hand, and took it.
Sai ya ce masa, “Ka ɗauko.” Sai mutumin ya miƙa hannu ya ɗauka.
8 And the king of Syria made war against Israel, and took counsel with his servants, saying, In such and such a place shall be my camp.
To, fa, sarkin Aram yana yaƙi da Isra’ila. Bayan ya tattauna da hafsoshinsa, sai ya ce, “Zan kafa sansanina a wurin kaza da kaza.”
9 And the man of God sent unto the king of Israel, saying, Beware that thou pass not that place; for thither the Syrians are come down.
Sai mutumin Allah ya aika wa sarkin Isra’ila cewa, “Ka yi hankali da wuce wuri kaza, domin Arameyawa za su gangara can.”
10 And the king of Israel sent to the place, which the man of God had told him and warned him of, and he took care of himself there: not once nor twice.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya lura da inda mutumin Allah ya ambata. Sau da sau Elisha yakan yi wa sarki kashedi, don haka ya riƙa taka yi tsantsan a wuraren nan.
11 Therefore the heart of the king of Syria was sorely troubled concerning this thing; and he called for his servants, and said unto them, Can ye not tell me who of us is for the king of Israel?
Wannan ya husata sarkin Aram. Ya kira hafsoshinsa ya tambaye su ya ce, “Ku faɗa mini, wane ne a cikinmu yake gefen sarkin Isra’ila?”
12 And one of his servants said, Not so, my Lord, O king; but Elisha', the prophet that is in Israel, can tell unto the king of Israel the words that thou mayest speak in thy sleeping-chamber.
Sai ɗaya daga cikin hafsoshinsa ya ce, “Babu waninmu, ranka yă daɗe; Elisha, annabin da yake a Isra’ila ne, yake faɗa wa sarkin Isra’ila dukan zancen da ka yi a ɗakinka.”
13 And he said, Go and see where he is, that I may send and fetch him. And it was told unto him, saying, Behold, he is in Dothan.
Sai sarki ya ba da umarni ya ce, “Ku je ku tabbatar da inda yake don in aika mutane a kamo shi.” Sai ya sami rahoto cewa, “Yana a Dotan.”
14 And he sent thither horses, and chariots, and a strong army: and they came by night, and surrounded the city.
Sai ya aika da dawakai da kekunan yaƙi da babban rukunin soja zuwa can. Suka bi dare, suka kewaye birnin.
15 And the servant of the man of God rose early, and went forth, when, behold, an army compassed the city both with horses and chariots. And his servant said unto him, Alas, my master! how shall we do?
Sa’ad da bawan mutumin Allah ya farka ya kuma fita kashegari da sassafe, sai ga mayaƙa tare da dawakai da kekunan yaƙi sun kewaye birni. Sai bawan ya ce, “Ranka yă daɗe! Me za mu yi?”
16 And he said, Fear not: for those that are with us are more than those that are with them.
Sai annabin ya ce, “Kada ka ji tsoro, waɗanda suke tare da mu sun fi waɗanda suke tare da su.”
17 And Elisha' prayed, and said, O Lord, open, I pray thee, his eyes, that he may see. And the Lord opened the eyes of the young man: and he saw, and behold, the mountain was full of horses and chariots of fire round about Elisha'.
Sa’an nan Elisha ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji, ka buɗe idanunsa yă gani!” Sai Ubangiji ya buɗe idanun bawan, ya duba, ya ga tuddai cike da dawakai da keken yaƙin wuta kewaye da Elisha.
18 And when they came down to him, Elisha' prayed unto the Lord, and said, Smite, I pray thee, this people with blindness. And he smote them with blindness according to the word of Elisha'.
Yayinda abokan gāba suka gangaro wajensa, sai Elisha ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ka sa mutanen nan su zama makafi.” Sai Ubangiji ya buge su da makanta kamar yadda Elisha ya roƙa.
19 And Elisha' said unto them, This is not the way, neither is this the city: follow me, and I will lead you to the man whom ye wish to seek. And he led them thus to Samaria.
Elisha ya ce musu, “Wannan ba ita ce hanyar ba, ba kuma gari ke nan ba, ku bi ni, zan kuwa kai ku wurin mutumin da kuke nema!” Sai ya kai su Samariya.
20 And it came to pass, when they were come into Samaria, that Elisha' said, Lord, open the eyes of these, that they may see. And the Lord opened their eyes, and they saw, and, behold, they were in the midst of Samaria.
Bayan suka shiga birnin, sai Elisha ya ce, “Ubangiji, ka buɗe idanun mutanen nan don su gani.” Sa’an nan Ubangiji ya buɗe idanunsu suka ga kansu a tsakiyar Samariya.
21 And the king of Israel said unto Elisha', when he saw them, Shall I smite them? Shall I smite them, my father?
Da sarkin Isra’ila ya gan su, sai ya tambayi Elisha ya ce, “In kashe su ne, mahaifina? In kashe su?”
22 But he said, Thou shalt not smite them: wouldst thou smite those whom thou hast taken captive with thy sword and with thy bow? set bread and water before them, that they may eat and drink, and go [back] to their master.
Elisha ya ce, “Kada ka kashe su. Za ka kashe mutanen da ka kame da takobi ko bakanka? Ka ba su abinci da ruwa su ci, su sha, sa’an nan su koma wurin maigidansu.”
23 And he prepared for them a great meal; and they ate and drank, and he sent them away, and they went [back] to their master. And the predatory bands of Syria came no more into the land of Israel.
Saboda haka aka shirya musu babban liyafa, bayan sun ci, suka kuma sha, sai ya tura su zuwa wurin maigidansu. Ta haka’yan harin Aram suka daina kai hari a yankin Isra’ila.
24 And it came to pass after this, that Ben-hadad the king of Syria assembled all his camp, and went up, and besieged Samaria.
Bayan wani lokaci, Ben-Hadad sarkin Aram ya tattara dukan rundunarsa, ya je ya kewaye Samariya da yaƙi.
25 And there was a great famine in Samaria; and, behold, they besieged it, until an ass's head was sold for eighty pieces of silver, and the fourth part of a kab of dove's dung for five pieces of silver.
Aka yi babban yunwa a cikin birnin. Saboda daɗewar wannan kewayewar da aka yi wa birnin, sai yunwa ta ɓarke a birnin, har ana sayar da kan jaki a kan shekel tamanin, kashin kurciya kuma a kan shekel biyar.
26 And it happened as the king of Israel was passing along upon the wall, that a woman cried unto him, saying, Help, my Lord, O king.
Yayinda sarkin Isra’ila yake wucewa kusa da katanga, sai wata mace ta yi masa kuka ta ce, “Ka taimake ni, ranka yă daɗe, sarki!”
27 And he said, If the Lord do not help thee, whence shall I help thee? shall it be out of the threshing-floor, or out of the wine-press?
Sai sarki ya amsa ya ce, “In Ubangiji bai taimake ki ba, me zan iya yi? Ina da hatsi ko ruwan inabin da zan ba ki ne?”
28 And the king said unto her, What aileth thee? And she said, This woman said unto me, Give up thy son, that we may eat him today, and my son we will eat tomorrow.
Sa’an nan ya tambaye ta ya ce, “Me ya faru?” Sai ta amsa ta ce, “Wannan mace ta ce mini, ‘Kawo ɗanki mu ci yau, gobe kuwa mu ci ɗana.’
29 So we boiled my son, and ate him; but when I said unto her on the next day, Give up thy son, that we may eat him: she hid her son.
Saboda haka muka dafa ɗana muka ci. Kashegari na ce mata, ‘Kawo ɗanki mu ci,’ amma ta ɓoye shi.”
30 And it came to pass, when the king heard the words of the woman, that he rent his clothes, as he was passing along upon the wall: and the people looked, and, behold, he had sackcloth beneath upon his flesh.
Da sarki ya ji maganar macen sai ya yage rigunansa. Sa’ad da sarki yake wucewa a kan katangar birnin, sai mutane suka gan yana saye da rigar makoki a ciki.
31 Then said he, May God do so unto me and continue so yet farther, if the head of Elisha' the son of Shaphat shall remain on him this day.
Ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani har ma fiye da haka, idan ban cire kan Elisha ɗan Shafat yau ba!”
32 But Elisha' was sitting in his house, and the elders were sitting with him; and he sent a man from before him; but before the messenger could yet come to him, he said to the elders, See ye how this son of the murderer hath sent to remove my head? look, when the messenger cometh, shut the door, and hold him back with the door: is not the sound of his master's feet behind him?
To, Elisha yana zaune a cikin gidansa, dattawa kuwa suna zaune tare da shi. Sai sarki ya aiki ɗan aika yă ci gaba, amma kafin ɗan aikan yă isa, Elisha ya ce wa dattawan, “Kun gani ko? Wannan mai kisa ya aiko a cire mini kai! To, idan ɗan aikan ya iso, sai ku rufe ƙofar da ƙarfi, ku bar shi a waje. Ba da jimawa ba, maigidansa zai bi bayansa?”
33 And while he was yet speaking with them, behold, the messenger came down unto him: and he said, Behold, this evil is of the Lord; what shall I hope for in the Lord any longer?
Yana magana da su ke nan, sai ga ɗan aikan ya gangaro wajensa. Sarki kuma ya ce, “Wannan bala’in daga wurin Ubangiji ya fito. Don me zan sa zuciya ga Ubangiji kuma?”

< 2 Kings 6 >