< 2 Kings 22 >

1 Eight years old was Josiah when he became king, and thirty and one years did he reign in Jerusalem. And his mother's name was Yedidah, the daughter of 'Adayah of Bozkath.
Yosiya yana da shekara takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara talatin da ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Yedida’yar Adahiya; mutuniyar Bozkat.
2 And he did what is right in the eyes of the Lord, and walked in all the way of David his father, and turned not aside to the right or to the left.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma bi dukan gurbin kakansa Dawuda, bai bauɗe hagu ko dama ba.
3 And it came to pass in the eighteenth year of king Josiah, that the king sent Shaphan the son of Azalyahu, the son of Meshullam, the scribe, to the house of the Lord, saying,
A shekara ta goma sha takwas ta mulkinsa, Sarki Yosiya ya aiki Shafan ɗan Azaliya, ɗan Meshullam, magatakarda, zuwa haikalin Ubangiji. Ya ce,
4 Go up to Chilkiyahu the high-priest, that he may collect up all the money which is brought into the house of the Lord, which the door-keepers have gathered from the people:
“Ka haura zuwa wurin Hilkiya babban firist ka sa yă shirya kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji, wanda masu tsaron ƙofa suka tara daga mutane.
5 And let them deliver it into the hand of those who overlook the workmen, that have been appointed as overseers of the house of the Lord; and let them give it to those who do the work who are in the house of the Lord, to repair the breaches of the house:
Ka sa su danƙa su a hannun waɗanda aka zaɓa don biyan ma’aikatan da suka yi gyara a haikalin Ubangiji,
6 Unto the carpenters, and the builders, and the masons, and to buy timber and hewn stones to repair the house.
wato, kafintoci, da magina, da masu tsara gini. Ka kuma sa su sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu don a gyara haikalin.
7 Nevertheless shall there be no reckoning made with them for the money that is delivered into their hand, because they deal faithfully.
Amma ba sa bukata su ba da bayanin kuɗin da aka danƙa musu domin suna aikinsu da aminci.”
8 And Chilkiyahu the high-priest said unto Shaphan the scribe, A book of the law have I found in the house of the Lord. And Chilkiyah gave the book to Shaphan, and he read it.
Hilkiya babban firist ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan, shi kuma ya karanta.
9 And Shaphan the scribe came to the king, and brought the king word again, and said, Thy servants have taken out all the money that was found in the house, and have delivered it into the hand of those who overlook the workmen, that have been appointed overseers of the house of the Lord.
Sa’an nan Shafan ya koma wurin sarki ya ce masa, “Hafsoshinka sun kwashe kuɗin da suke a haikalin Ubangiji, suka ba wa masu aiki da masu lura da haikalin.”
10 And Shaphan the scribe also told the king, saying, A book hath Chilkiyahu the priest given me. And Shaphan read it before the king.
Sa’an nan Shafan magatakarda ya ce wa sarki, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta shi a gaban sarki.
11 And it came to pass, when the king had heard the words of the book of the law, that he rent his clothes.
Da sarki ya ji kalmomin Littafin Doka, sai ya kece tufafinsa.
12 And the king commanded Chilkiyah the priest, and Achikam the son of Shaphan, and 'Achbor the son of Michayah, and Shaphan the scribe, and 'Assahyah a servant of the king's, saying,
Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya firist, da Ahikam ɗan Shafan, da Akbor ɗan Mikahiya, da Shafan magatakarda, da kuma Asahiya mai hidimar sarki, ya ce,
13 Go ye, inquire of the Lord in my behalf, and in behalf of the people, and in behalf of all Judah, concerning the words of this book that hath been found; for great is the wrath of the Lord that hath been kindled against us, because our fathers did not hearken unto the words of this book, to do in accordance with all that is prescribed concerning us.
“Ku je, ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da saboda jama’a da kuma saboda dukan Yahuda game da abin da wannan littafi da aka samo ya ƙunsa. Fushin Ubangiji mai girma ne a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye kalmomin littafin nan ba; ba su aikata bisa ga abin da yake a rubuce game da mu ba.”
14 And Chilkiyahu the priest, and Achikam, and 'Achbor, and Shaphan, and 'Assahyah, went unto Chuldah the prophetess, the wife of Shallum the son of Tikvah the son of Charchass, the keeper of the wardrobe; [now she dwelt in Jerusalem in the suburb; ] and they spoke unto her.
Sai Hilkiya firist, da Ahikam, Akbor, da Shafan, da kuma Asahiya suka je don su yi magana da annabiya Hulda, matan Shallum ɗan Tikba, ɗan Harhas, mai ajiyar tufafi. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
15 And she said unto them, Thus hath said the Lord the God of Israel, Say unto the man that hath sent you to me,
Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ku faɗa wa mutumin da ya aike ku wurina,
16 Thus hath said the Lord, Behold, I will bring evil upon this place, and upon its inhabitants, all the words of the book which the king of Judah hath read;
‘Ga abin da Ubangiji ya ce, zan kawo masifa wa wannan wuri da kuma wa kan mutanen wurin, bisa ga dukan abubuwan da suke a rubuce a cikin littafin da sarkin Yahuda ya karanta.
17 Because they have forsaken me, and have burnt incense unto other gods, in order to provoke me to anger with all the works of their hands: therefore is my wrath kindled against this place, and shall not be quenched.
Domin sun yashe ni suka ƙona turare wa waɗansu alloli, suka tozarta ni da dukan gumakan da hannuwansu suka sassaƙa, fushina zai yi ƙuna a kan wannan wuri, ba kuwa zai huce ba.’
18 But with respect to the king of Judah who sendeth you to inquire of the Lord, thus shall ye say to him, Thus hath said the Lord the God of Israel, Concerning the words which thou hast heard;
Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da kalmomin da ka ji.
19 Because thy heart was tender, and thou hast humbled thyself before the Lord, when thou heardest what I had spoken against this place, and against its inhabitants, that they should become an astonishment and a curse, and hast rent thy clothes, and wept before me: I also have heard it, saith the Lord.
Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Ubangiji sa’ad da ka ji abin da na faɗa game da wannan wuri da mutanen wurin, cewa za su zama la’antattu da kuma kango, domin kuma ka kece tufafinka, ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
20 Therefore, behold, I will gather thee unto thy fathers, and thou shalt be gathered unto thy graves in peace; and thy eyes shall not look on all the evil which I am bringing over this place. And they brought the king word again.
Saboda haka zan haɗa ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka kuma ba za su ga dukan wannan masifan da zan jawo wa wurin nan ba.’” Sai suka kai wa sarki abin da ta faɗa.

< 2 Kings 22 >