< 2 Kings 1 >

1 Then did Moab rebel against Israel after the death of Achab.
Bayan mutuwar Ahab, Mowab ta yi wa Isra’ila tawaye.
2 And Achazyah fell down through the lattice in his upper chamber that was in Samaria, and became sick; and he sent messengers, and said unto them, Go, inquire of Ba'al-zebub the god of 'Ekron whether I shall recover from this sickness.
Ahaziya fa ya fāɗo daga tagar ɗakin samansa a Samariya ya ji rauni. Saboda haka ya aiki masinjoji, yana cewa, “Ku je ku tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron, ku ga ko zan warke daga wannan rauni.”
3 But an angel of the Lord spoke to Elijah the Tishbite, Arise, go up to meet the messengers of the king of Samaria, and say unto them, Is it because there is not a God in Israel, that ye go to inquire of Ba'al-zebub the god of 'Ekron?
Amma mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya mutumin Tishbe, “Ka haura ka taryi masinjojin sarkin Samariya, ka tambaye su, ‘Don babu Allah ne a Isra’ila da za ku tafi ku tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron?’
4 Now therefore, thus hath said the Lord, From the bed on which thou art gone up shalt thou not come down; for thou shalt surely die. And Elijah departed.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ba za ka tashi daga inda kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!’” Iliya ya yi kamar yadda Ubangiji ya umarce shi, sai ya tafi.
5 And the messengers returned unto him, and he said unto them, Why is this that ye are already returned?
Da masinjojin suka koma wurin sarki, sai sarki ya ce da su, “Don me kuka komo?”
6 And they said unto him, There came up a man to meet us, and he said unto us, Go, return unto the king that hath sent you, and speak unto him, Thus hath said the Lord, Is it because there is not a God in Israel, that thou sendest to inquire of Ba'al-zebub the god of 'Ekron? therefore from the bed on which thou art gone up shalt thou not come down; for thou shalt surely die.
Sai suka amsa, “Wani mutum ya sadu da mu ya ce mana, ‘Ku koma wurin sarkin da ya aike ku, ku ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah ne a Isra’ila da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron? Saboda haka ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba. Ba shakka za ka mutu!”’”
7 And he spoke unto them, What is the manner of the man who came up to meet you, and spoke unto you these words?
Sai Sarkin ya tambaye su ya ce, “Wanda irin mutum ne ya yi muku wannan magana?”
8 And they said unto him, He is a hairy man, with a girdle of leather girded about his loins. And he said, It is Elijah the Tishbite.
Sai suka ce, “Mutumin ya sa riga mai gashi, ya kuma yi ɗamara da fata.” Sarkin ya ce, “Ai, Iliya mutumin Tishbe nan ne.”
9 Then did he send unto him a captain of fifty with his fifty: and he went up to him, and, behold, he was sitting on the top of the mount; and he spoke unto him, O man of God, the king hath commanded, Come down.
Sai sarki ya aiki kaftin da sojojin hamsin wurin Iliya. Kaftin ya haura wajen Iliya, wanda yake zaune a kan tudu, ya ce masa, “Mutumin Allah, sarki ya ce, ‘Ka sauko, ka zo!’”
10 And Elijah answered and spoke to the captain of the fifty, And if I be a man of God, let a fire come down from heaven and consume thee and thy fifty. And there came down a fire from heaven, and consumed him and his fifty.
Iliya ya ce masa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta tă sauko daga sama tă cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wuta ta sauko daga sama ta cinye kaftin tare da sojojinsa hamsin.
11 And he sent again unto him another captain of fifty with his fifty. And he commenced and spoke unto him, O man of God, thus hath the king said, Come down quickly.
Da jin haka sai sarki ya sāke aiken wani kaftin tare da waɗansu sojojinsa hamsin wurin Iliya. Kaftin ya ce wa Iliya, “Mutumin Allah, ga abin da sarki ya ce, ‘Ka sauko, nan take ka zo!’”
12 And Elijah answered and spoke unto them, If I be a man of God, let a fire come down from heaven, and consume thee and thy fifty. And the fire of God came down from heaven and consumed him and his fifty.
Sai Iliya ya amsa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta ta sauko daga sama ta cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wutar Allah ta sauko daga sama ta cinye shi da sojojinsa hamsin.
13 And he sent again a captain of fifty the third time with his fifty. And the third captain of fifty went up, and came and bent down on his knees before Elijah, and besought him, and spoke unto him, O man of God, I pray thee, let my life and the life of these fifty thy servants be precious in thy eyes.
Saboda haka sai sarki ya aiki kaftin na uku da sojojinsa hamsin. Wannan kaftin na ukun ya haura ya durƙusa a gaban Iliya, ya roƙe shi ya ce, “Mutumin Allah, ina roƙonka ka dubi darajar raina da na waɗannan sojoji hamsin, bayinka!
14 Behold, there came down a fire from heaven, and consumed the two captains of the first fifties with their fifties; and now let my life be precious in thy eyes.
Duba, wuta ta sauko daga sama ta cinye su kaftin nan biyu waɗanda suka zo da farko da dukan sojojinsu. To, yanzu dai, ka daraja raina!”
15 And the angel of the Lord spoke unto Elijah, Go down with him: be not afraid of him, and he arose, and went down with him unto the king.
Sai mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya, “Sauka, ka tafi tare da shi; kada ka ji tsoro.” Saboda haka Iliya ya tashi ya sauko, ya tafi tare da shi wajen sarki.
16 And he spoke unto him, Thus hath said the Lord, Forasmuch as thou didst send messengers to inquire of Ba'al-zebub the God of 'Ekron, as though there were no God in Israel to inquire of his word: therefore from the bed on which thou art gone up shalt thou not come down; for thou shalt surely die.
Iliya ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah a Isra’ila ne wanda za ka tuntuɓa da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron? Domin ka yi haka, ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!”
17 And he died, according to the word of the Lord which Elijah had spoken; and Jehoram became king in his stead in the second year of Jehoram the son of Jehoshaphat the king of Judah; because he had no son.
Ya kuwa mutu yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya. Da yake Ahaziya ba shi da ɗa, sai Yoram ya gāje shi, ya zama sarki a shekara ta biyu ta mulkin Yehoram, ɗan Yehoshafat, sarkin Yahuda.
18 Now the rest of the acts of Achazyahu which he did, behold, they are written in the book of the chronicles of the kings of Israel.
Game da dukan sauran abubuwan da suka faru a zamani Ahaziya, da abin da ya yi, ba a rubuce suke a littattafan tarihin sarakuna Isra’ila ba?

< 2 Kings 1 >