< 2 Chronicles 21 >

1 And Jehoshaphat slept with his fathers, and was buried with his fathers in the city of David. And Jehoram his son became king in his stead.
Yehoshafat ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
2 And he had brothers the sons of Jehoshaphat: 'Azaryah, and Jechiel, and Zecharyahu, and 'Azaryahu, and Michael, and Shephatyahu, all these being sons of Jehoshaphat the king of Israel.
’Yan’uwan Yehoram,’ya’yan Yehoshafat maza su ne, Azariya, Yehiyel, Zakariya, Azariyahu, Mika’ilu da Shefatiya. Dukan waɗannan su ne’ya’yan Yehoshafat sarkin Isra’ila maza.
3 And their father gave them many gifts [consisting] of silver, and of gold, and of precious things, with fortified cities in Judah; but the kingdom gave he to Jehoram; because he was the first-born.
Mahaifinsu ya ba su kyautai masu yawa na azurfa da zinariya da kayayyaki masu daraja, tare da birane masu katanga a Yahuda, amma ya ba da mulki ga Yehoram domin shi ne ɗan farinsa.
4 Now when Jehoram was risen up over the kingdom of his father, and had strengthened himself, he slew all his brothers with the sword, and also some of the princes of Israel.
Sa’ad da Yehoram ya kafa kansa sosai a bisa mulkin mahaifinsa, sai ya kashe dukan’yan’uwansa da takobi tare da waɗansu sarakunan Isra’ila.
5 Thirty and two years was Jehoram old when he became king, and eight years did he reign in Jerusalem.
Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas.
6 And he walked in the way of the kings of Israel, as had done the house of Achab; for the daughter of Achab had he for wife: and he did what is evil in the eyes of the Lord.
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, kamar yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya aikata mugayen ayyuka a idon Ubangiji.
7 Yet would the Lord not destroy the house of David, on account of the covenant which he had made with David, and as he had said to give to him a government and to his sons at all times.
Duk da haka, domin alkawarin da Ubangiji ya yi wa Dawuda, Ubangiji bai so yă hallaka gidan Dawuda ba. Ubangiji ya riga ya yi alkawari zai ci gaba da riƙe fitila domin Dawuda da zuriyarsa har abada.
8 In his days Edom revolted from under the power of Judah, and they appointed a king over themselves.
A zamanin Yehoram, Edom ya tayar wa Yahuda ya kuma naɗa sarkinsa.
9 Then did Jehoram go over with his princes, and all the chariots were with him; and he rose up by night, and smote the Edomites who compassed him about, and the captains of the chariots.
Saboda haka Yehoram ya tafi can tare da shugabannin sojojinsa da kuma dukan keken yaƙinsa. Mutanen Edom suka kewaye shi da shugabannin keken yaƙinsa, amma ya tashi ya fatattaki su da dare.
10 Yet Edom revolted from under the power of Judah even until this day: then did Libnah revolt at the same time from under his power; because he had forsaken the Lord the God of his fathers.
Har yă zuwa yau Edom na tawaye a kan Yahuda. Libna ya yi tawaye a lokaci guda, domin Yehoram ya yashe Ubangiji Allah na kakanninsa.
11 He also made high-places in the mountains of Judah, and caused the inhabitants of Jerusalem to go astray, and misled Judah.
Ya gina masujadan kan tudu a tuddan Yahuda, ya kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, ya sa Yahuda suka kauce.
12 And there came unto him a writing from Elijah the prophet, saying, Thus hath said the Lord the God of David thy father, Inasmuch as thou hast not walked in the ways of Jehoshaphat thy father, and in the ways of Assa the king of Judah,
Yehoram ya sami wasiƙa daga Iliya annabi, wadda ta ce, “Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda ya ce, ‘Ba ka yi tafiya a hanyoyin mahaifinka Yehoshafat ko Asa sarkin Yahuda ba.
13 But hast walked in the way of the kings of Israel, and hast caused Judah and the inhabitants of Jerusalem to go astray, as the house of Achab hath caused [others] to go astray, and hast also slain thy brothers of thy father's house, who were better than thyself:
Amma ka yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, ka sa Yahuda ya kauce, ka kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, kamar yadda gidan Ahab ta yi. Ka kuma kashe’yan’uwanka, membobi gidan mahaifinka, mutanen da suka fi ka kirki.
14 Behold, the Lord will inflict a great plague on thy people, and on thy children, and on thy wives, and on all thy possessions;
Saboda haka a yanzu Ubangiji yana shirin ya bugi mutanenka,’ya’yanka maza, matanka da kuma kome da yake naka, da bugu mai ƙarfi.
15 And thou shalt be [afflicted] with great diseases by a disease of thy bowels, until thy bowels pass out [from thee] by reason of the disease days upon days.
Kai kuma za ka kamu da ciwon hanji wanda zai yi ta cinka kowace rana sai har hanjinka sun fito.’”
16 And the Lord stirred up against Jehoram the spirit of the Philistines, and of the Arabians, that are alongside of the Cushim:
Ubangiji ya sa Filistiyawa da Larabawa waɗanda suke zama kusa da Kushawa su yi gāba da Yehoram
17 And they went up against Judah, and made an incursion into it, and carried away all the substance that was found in the king's house, and also his sons, and his wives; and there was not left unto him any son, save Jehoachaz, the youngest of his sons.
Suka yaƙi Yahuda, suka kai masa hari, suka kwashe dukan abubuwa masu kyau da suka samu a fadan sarki, tare da’ya’yansa maza da kuma matansa. Ba wanda aka bari, sai dai Ahaziya autansa.
18 And after all this did the Lord afflict him in his bowels with a disease which was incurable.
Bayan dukan wannan, sai Ubangiji ya sa wa Yehoram cuta marar warkarwa ta ciki.
19 And it came to pass, from days to days, and when the [fixed] time was expired, after two years, that his bowels passed out [from him] by reason of his disease: so he died of evil diseases. And his people made no burning for him, like the burning for his fathers.
Cikin lokaci, a ƙarshen shekara ta biyu, sai hanjin cikinsa suka fito saboda cutar, ya kuma mutu cikin tsananin zafi. Mutanensa suka hura wuta don girmama shi, kamar yadda suka yi wa kakanninsa.
20 Thirty and two years old was he when he became king, and eight years did he reign in Jerusalem, and departed without joy: and they buried him in the city of David, but not in the sepulchres of the kings.
Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas. Ya mutu, ba ma wanda ya kula, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda, amma ba a makabartan sarakuna ba.

< 2 Chronicles 21 >