< 2 Chronicles 20 >

1 And it came to pass after this, that the children of Moab, and the children of 'Ammon, and with them some of the 'Ammonim, came against Jehoshaphat to battle.
Bayan wannan, Mowabawa da Ammonawa tare da waɗansu Meyunawa suka zo su yaƙi Yehoshafat.
2 And there came some and told unto Jehoshaphat, saying, There is coming against thee a great multitude from beyond the sea, from Syria; and, behold, they are in Chazazon-thamar, which is 'En-gedi.
Sai waɗansu mutane suka zo suka faɗa wa Yehoshafat, “Ga babban runduna tana zuwa a kanka daga Edom, daga ƙetaren Teku, daga Aram. Ta ma kai Hazazon Tamar” (wato, En Gedi).
3 Then became Jehoshaphat afraid, and he directed his face to seek the Lord; and he proclaimed a fast over all Judah.
A firgice, Yehoshafat ya yanke shawara yă nemi nufin Ubangiji, ya kuma yi shelar azumi a dukan Yahuda.
4 And [the people of] Judah gathered themselves together, to ask [help] of the Lord: also out of all the cities of Judah did they come to seek the Lord.
Mutanen Yahuda suka taru gaba ɗaya don su nemi taimako daga wurin Ubangiji, tabbatacce suka fito daga kowane garin Yahuda don su neme shi.
5 And Jehoshaphat stood forward in the assembly of Judah and Jerusalem, in the house of the Lord, before the new court.
Sa’an nan Yehoshafat ya miƙe tsaye a taron Yahuda da Urushalima a haikalin Ubangiji a sabon filin
6 And he said, O Lord, the God of our fathers, thou art God in the heavens, and thou rulest over all the kingdoms of the nations; and in thy hand are the power and might, and there is none that can withstand thee.
ya ce, “Ya Ubangiji Allah na kakanninmu, ba kai ne Allah wanda yake sama ba? Kana mulki a bisa dukan mulkokin ƙasashe. Iko da girma suna a hannunka, kuma ba wanda zai iya tsayayya da kai.
7 Behold, it is thou, O our God, who hast driven out the inhabitants of this land from before thy people Israel; and thou gavest it to the seed of Abraham thy friend to eternity.
Ya Allahnmu, ba kai ba ne ka kore mazaunan wannan ƙasa a gaban mutanenka Isra’ila ka kuma ba da ita har abada ga zuriyar Ibrahim abokinka?
8 And they have dwelt therein, and have built for thee therein a sanctuary for thy name, saying,
Sun yi zama a cikinta suka kuma yi gina wuri mai tsarki a cikinta domin Sunanka cewa,
9 If there should come over us any evil, the sword, punishment, or pestilence, or famine, [then] will we stand before this house, and in thy presence, for thy name is in this house, and we will cry unto thee out of our distress, and thou wilt hear and help.
‘In masifa ta zo mana, ko takobin hukunci, ko annoba ko yunwa, za mu tsaya a gabanka a gaban wannan haikalin da yake ɗauke da Sunanka, mu kuma yi kuka gare ka cikin azaba, za ka kuwa ji mu, ka cece mu.’
10 And now, behold, the children of 'Ammon and Moab and mount Se'ir, against whom thou wouldst not suffer Israel to come, when they came out of the land of Egypt, but they turned aside from them, and destroyed them not: —
“Yanzu kuma ga mutanen Ammon, da na Mowab, da na Dutsen Seyir, waɗanda ka hana Isra’ilawa su kai musu yaƙi sa’ad da suka fito daga ƙasar Masar, su ne mutanen da Isra’ila suka ƙyale, ba su hallaka su ba.
11 And behold, they recompense us, by coming to drive us out of thy inheritance, which thou hast given us to possess.
Yau ga yadda suke so su biya mu. Su suke so su kore mu daga ƙasar da ka ba mu gādo.
12 O our God, wilt thou not execute justice on them? for there is no power in us against this great multitude that is coming against us; and we indeed know not what we are to do: but upon thee are our eyes [directed].
Ya Allahnmu, ba za ka hukunta su ba? Gama ba mu da ƙarfin fuskantar wannan babbar rundunar da take so ta yaƙe mu. Ba mu san abin da za mu yi ba, mu dai mun zuba maka ido.”
13 And all Judah were standing before the Lord, also their little ones, their wives, and their sons.
Dukan mazan Yahuda, tare da matansu da yaransu da ƙananansu, suka tsaya a gaban Ubangiji.
14 And upon Jachaziel the son of Zecharyahu, the son of Benayah, the son of Je'iel, the son of Matthanyah, the Levite, of the sons of Assaph, came the spirit of the Lord in the midst of the assembly;
Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko a kan Yahaziyel ɗan Zakariya, ɗan Benahiya, ɗan Yehiyel, ɗan Mattaniya, wani Balawe kuma zuriyar Asaf, yayinda yake tsaye a cikin taron.
15 And he said, Listen ye, all Judah, and ye inhabitants of Jerusalem, and thou king Jehoshaphat, Thus hath said the Lord unto you, Be ye not afraid and be not dismayed because of this great multitude; for not unto you belongeth the battle, but unto God.
Ya ce, “Saurara, Sarki Yehoshafat da dukan waɗanda suke zama a Yahuda da Urushalima! Ga abin da Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku ji tsoro ko ku fid da zuciya saboda wannan babbar runduna. Gama yaƙin ba naku ba ne, amma na Allah.
16 Tomorrow go ye down against them behold, they come up by the ascent of Ziz; and ye will find them at the end of the valley, in front of the wilderness of Jeruel.
Gobe ku fito ku gangara ku yaƙe su. Za su yi ta haurawa ta Mashigin Ziz, ku kuwa za ku same su a ƙarshen kwari a Hamadan Yeruwel.
17 Ye shall not need to fight in this place: stand firmly, stand still, and see the salvation of the Lord with you, O Judah and Jerusalem: fear not, and be not dismayed; tomorrow go out to meet them, and the Lord will be with you.
Ba lalle ba ne ku yi wannan yaƙi. Ku dai, ku ja dāgā, ku tsaya kurum ku ga nasarar da Ubangiji zai ba ku, ya Yahuda da Urushalima. Kada ku ji tsoro; kada ku karai. Ku fito don ku fuskance su gobe, Ubangiji kuwa zai kasance tare ku.’”
18 And Jehoshaphat bowed his head with his face to the ground: and all Judah and the inhabitants of Jerusalem fell down before the Lord, to prostrate themselves unto the Lord.
Yehoshafat ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka fāɗi rubda ciki suka yi sujada a gaban Ubangiji.
19 And then arose the Levites, of the children of the Kehathites, and of the children of the Korehites, to praise the Lord the God of Israel with a very loud voice.
Sa’an nan waɗansu Lawiyawa daga Kohatawa da Korayawa suka tashi tsaye suka yabe Ubangiji, Allah na Isra’ila, da babbar murya sosai.
20 And they rose up early in the morning, and went forth into the wilderness of Thekoa': and as they went forth, Jehoshaphat stood forward and said, Hear me, O Judah, and ye inhabitants of Jerusalem; believe in the Lord your God, and ye will have permanence; believe his prophets, and ye will prosper.
Da sassafe suka tashi suka nufi Hamadan Tekowa. Yayinda suka kama hanya, Yehoshafat ya tsaya ya ce, “Ku saurare ni, Yahuda da mutanen Urushalima! Ku amince da Ubangiji Allahnku za a kuwa kafa ku; ku amince da annabawansa za ku kuwa yi nasara.”
21 And he consulted with his people, and he appointed singers unto the Lord, and those that should praise in the holy ornaments, as they went out before the armed array, and said, Give thanks unto the Lord; for unto everlasting endureth his kindness.
Bayan suka yi shawara tare da shugabanni, sai ya zaɓi mutanen da za su ja gaban sojoji suna waƙa ga Ubangiji suna yabonsa saboda tsarkinsa suna cewa, “Ku yi godiya ga Ubangiji, gama ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
22 And at the time when they began with the song and the praise, the Lord set an ambush against the children of 'Ammon, Moab, and mount Se'ir, who were come against Judah, and they were smitten.
Da suka fara waƙa, suna kuma yabo, sai Ubangiji ya kai hari a kan mutanen Ammon da Mowab da Dutsen Seyir, waɗanda suka kawo hari a Yahuda, aka kuwa ci su da yaƙi.
23 And the children of 'Ammon and Moab stood up against the inhabitants of mount Se'ir, utterly to annihilate and to destroy them; and when they had made an end of the inhabitants of Se'ir, they helped to destroy one another.
Mutanen Ammon da Mowab suka tasar wa mazaunan Dutsen Seyir, suka hallaka su ƙaƙaf. Sa’ad da suka karkashe mazaunan Seyir sai suka fāɗa wa juna, suka yi ta hallaka juna.
24 And when Judah came toward the watchtower in the wilderness, they looked toward the multitude, and, behold, they were dead bodies fallen to the earth, and none had escaped.
Sa’ad da mutanen Yahuda suka zo wurin da yake fuskantar hamada, suka duba ta wajen babban rundunar, sai suka ga gawawwaki birjik a ƙasa; babu wani wanda ya kuɓuta.
25 And then came Jehoshaphat and his people to plunder their booty, and they found among them in abundance both riches and dead bodies, and costly vessels, which they stript off for themselves, more than they could carry away: and they were three days in plundering the booty, for it was so much.
Sa’ad da Yehoshafat da jama’arsa suka je kwasar ganima, sai suka sami shanu masu yawan gaske, da kayayyaki, da tufafi, da abubuwa masu daraja, waɗanda suka yi ta kwasa har suka gaji. Kwana uku suka yi suna kwasar ganimar saboda yawanta.
26 And on the fourth day they assembled themselves in the valley of Berachah; for there they blessed the Lord: therefore did they call the name of this place, The valley of Berachah [[Blessing]], until this day.
A rana ta huɗu sai suka taru a Kwarin Beraka, inda suka yabi Ubangiji. Wannan ne ya sa ake kiransa Kwarin Beraka har wa yau.
27 Then returned all the men of Judah and Jerusalem, and Jehoshaphat at their head, to return to Jerusalem with joy; for the Lord had caused them to rejoice over their enemies.
Sa’an nan Yehoshafat ya jagoranci dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka dawo da farin ciki zuwa Urushalima, gama Ubangiji ya ba su dalilin farin ciki a kan abokan gābansu.
28 And they came to Jerusalem with psalteries and with harps and with trumpets unto the house of the Lord.
Suka shiga Urushalima suka shiga haikalin Ubangiji da kiɗin molaye da sarewa da kuma garayu.
29 And a dread from God was on all the kingdoms of [those] countries, when they heard that the Lord had fought with the enemies of Israel.
Tsoron Allah ya kama dukan mulkokin ƙasashe sa’ad da suka ji yadda Ubangiji ya yi yaƙi a kan abokan gāban Isra’ila.
30 So the kingdom of Jehoshaphat had repose, and his God gave him rest all round about.
Mulkin Yehoshafat kuwa ya zauna lafiya, gama Allahnsa ya ba shi hutu a kowane gefe.
31 And [so] did Jehoshaphat reign over Judah; thirty and five years old was he when he became king, and twenty and five years did he reign in Jerusalem. And his mother's name was 'Azubah the daughter of Shilchi.
Ta haka Yehoshafat ya yi mulki a bisa Yahuda. Yana da shekara talatin da biyar sa’ad da ya zama sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa Azuba ce,’yar Shilhi.
32 And he walked in the way of his father Assa, and turned not aside from it, doing what is right in the eyes of the Lord.
Ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa Asa bai kuwa kauce daga gare su ba; ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
33 Nevertheless the high-places were not removed; for the people had not yet directed their heart firmly unto the God of their fathers.
Duk da haka ba a kawar da masujadai kan tudu ba, domin har yanzu mutanen ba su tsayar da zukatansu ga Allahn kakanninsu ba.
34 And the rest of the acts of Jehoshaphat, the first and the last, behold, they are written in the history of Jehu the son of Chanani, which was entered into the book of the kings of Israel.
Sauran ayyukan mulkin Yehoshafat, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a tarihin Yehu ɗan Hanani, waɗanda aka rubuta a littafin sarakunan Isra’ila.
35 And after this did Jehoshaphat the king of Judah connect himself with Achazyah the king of Israel, the same who acted very wickedly;
Daga baya, Yehoshafat sarkin Yahuda ya haɗa kai da Ahaziya sarkin Isra’ila, wanda yake da laifin mugunta.
36 And he connected himself with him to make ships to go to Tharshish: and they made ships in 'Ezyon-geber.
Ya yarda da shi su gina jiragen ruwan kasuwanci. Bayan aka gina waɗannan a Eziyon Geber,
37 Then prophesied Eli'ezer the son of Dodavahu of Mareshah against Jehoshaphat, saying, Because thou hast connected thyself with Achazyahu, the Lord hath broken down thy works. And the ships were wrecked, so that they were not able to go to Tharshish.
Eliyezer ɗan Dodabahu na Maresha ya yi annabci a kan Yehoshafat cewa, “Domin ka haɗa kai da Ahaziya, Ubangiji zai hallaka abin da ka yi.” Jiragen ruwan kuwa suka farfashe, ba a kuwa iya sa su je kasuwanci ba.

< 2 Chronicles 20 >