< 2 Chronicles 13 >

1 In the eighteenth year of king Jerobo'am became Abiyah king over Judah.
A shekara ta sha takwas ta sarautar Yerobowam, Abiya ya zama sarkin Yahuda,
2 Three years he reigned in Jerusalem: and his mother's name was Michayahu the daughter of Uriel of Gib'ah. And there was war between Abiyah and Jerobo'am.
ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru uku. Sunan mahaifiyarsa Mikahiya ce,’yar Uriyel na Gibeya. Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Abiya da Yerobowam.
3 And Abiyah joined the battle with an army of valiant men of war, even of four hundred thousand chosen men: Jerobo'am also set the battle in array against him with eight hundred thousand chosen men, being mighty men of valor.
Abiya ya tafi yaƙi tare da mayaƙa dubu ɗari huɗu jarumawa, Yerobowam kuwa ya ja dāgār yaƙi a kan Abiya da mayaƙa dubu ɗari takwas jarumawa.
4 And Abiyah stood up above mount Zemarayim, which is in the mountain of Ephraim, and said, Hear me, O Jerobo'am, and all Israel;
Abiya ya tsaya a Dutsen Zemarayim, a ƙasar tudu ta Efraim ya ce, “Yerobowam da dukan Isra’ila, ku saurare ni!
5 Ought ye not to know that the Lord the God of Israel hath given the kingdom over Israel to David for eternity, yea, to him and to his sons by a covenant of salts?
Ba ku san cewa Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ba da sarautar Isra’ila ga Dawuda da zuriyarsa har abada ta wurin alkawarin gishiri ba?
6 But there rose up Jerobo'am the son of Nebat, the servant of Solomon the son of David, and rebelled against his lord.
Duk da haka Yerobowam ɗan Nebat, ma’aikacin Solomon ɗan Dawuda, ya tayar wa maigidansa,
7 And there were gathered unto him idle men, worthless persons, and put themselves in violent resistance against Rehobo'am the son of Solomon: while Rehobo'am was young and tender hearted, and could not sustain himself before them.
sai ya tara wa kansa’yan iska da mugayen mutane suka yi gāba da Rehobowam ɗan Solomon. Rehobowam lokacin kuwa ba shi da wayo, don haka bai iya tsai da su ba.
8 And now ye think to sustain yourselves before the kingdom of the Lord in the hand of the sons of David; and ye are a great multitude; and with you are golden calves, which Jerobo'am hath made for you as gods.
“Yanzu kuna shirin yin tsayayya da mulkin Ubangiji, wanda yake a hannuwan zuriyar Dawuda. Tabbatacce ku ƙasaitacciyar mayaƙa ne kuma kuna tare da ku maruƙan zinariyar da Yerobowam ya yi domin su zama allolinku.
9 Have ye not cast out the priests of the Lord, the sons of Aaron, and the Levites, and have made yourselves priests like the people of the [various] lands? so that whosoever cometh to consecrate himself with a young bullock and seven rams can become a priest to things that are no gods?
Ba ku ne kuka kori firistocin Ubangiji,’ya’yan Haruna maza, da Lawiyawa kuka kuma zaɓi firistocinku kamar yadda sauran al’ummai suke yi ba? Duk wanda ya zo ya miƙa ɗan bijimi da raguna bakwai don yă tsarkake kansa, ya zama firist na gumaka ke nan, ba na Allah ba.
10 But as for us, the Lord is our God, and we have not forsaken him; and the priests, who minister unto the Lord, are the sons of Aaron; and the Levites are at their [appointed] work;
“Gare mu kuwa, Ubangiji shi ne Allah, kuma ba mu yashe shi ba. Firistocin da suke bauta wa Ubangiji’ya’yan Haruna maza ne, Lawiyawa ne kuwa suke taimakonsu.
11 And they burn unto the Lord burnt-offerings every morning and every evening and incense of sweet spices; and the rows of the show-bread [do they place] upon the pure table; and there is the candlestick of gold with its lamps, to light the same every evening; for we keep the charge of the Lord our God, while ye have truly forsaken him.
Kowace safiya da kowace yamma sukan miƙa hadayun ƙonawa da turare mai ƙanshi ga Ubangiji. Sukan shirya burodi a tsarkaken tebur mai tsabta, sukan kuma ƙuna fitilu a alkukai kowace yamma. Muna kiyaye ƙa’idodin Ubangiji Allahnmu. Amma ku kun yashe shi.
12 And, behold, with us at our head, is the [true] God, with his priests with trumpets for blowing the alarm, to sound an alarm against you. O children of Israel, do not fight against the Lord the God of your fathers; for ye will not prosper.
Allah yana tare da mu; shi ne shugabanmu. Firistocinsa tare da ƙahoni za su busa kirarin yaƙi a kanku. Mutanen Isra’ila, kada ku yi yaƙi da Ubangiji Allah na kakanninku, gama ba za ku yi nasara ba.”
13 But Jerobo'am caused an ambush to come around behind them: so they themselves were before Judah, and the ambush was behind them.
To, fa, Yerobowam ya aiki mayaƙa su zagaya daga baya, domin yayinda yake a gaban Yahuda, sai’yan kwanto su kasance a bayansu.
14 And when Judah turned round, behold, they had the battle before and behind: and they cried unto the Lord, and the priests blew with the trumpets.
Yahuda ya juya sai ya ga cewa ana yaƙe su gaba da baya. Sai suka yi kuka ga Ubangiji. Firistoci suka busa ƙahoni
15 And then gave the men of Judah a shout: and it came to pass, as the men of Judah shouted, that God struck down Jerobo'am and all Israel before Abiyah and Judah.
mutanen Yahuda kuwa suka tā da kirarin yaƙi. Da ji kirarin yaƙi, Allah ya fatattake Yerobowam da dukan Isra’ila a gaban Abiya da Yahuda.
16 And the children of Israel fled from before Judah, and God gave them up into their hand.
Isra’ilawa suka gudu a gaban Yahuda, Allah kuwa ya bashe su a hannuwansu.
17 And Abiyah and his people smote them with a great defeat, and there fell down slain of Israel five hundred thousand chosen men.
Abiya da mutanensa suka kashe su sosai, har mutum dubu ɗari biyar suka mutu a cikin jarumawan Isra’ila.
18 Thus were the children of Israel humbled at that time: and the children of Judah became powerful, because they relied upon the Lord the God of their fathers.
Aka cinye mutanen Isra’ila a wannan lokaci, mutanen Yahuda kuwa suka yi nasara domin sun dogara ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
19 And Abiyah made pursuit after Jerobo'am, and captured cities from him, Bethel with its villages, and Jeshanah with its villages, and 'Ephrayin with its villages.
Abiya ya kori Yerobowam ya kuma ƙwace garuruwan Betel, Yeshana da Efron, tare da ƙauyukan da suke kewaye daga gare shi.
20 And Jerobo'am did not recover strength again in the days of Abiyahu: and the Lord struck him, and he died.
Yerobowam bai sāke yin ƙarfi a zamanin Abiya ba. Ubangiji ya buge shi ya kuma mutu.
21 But Abiyahu became strong, and he took himself fourteen wives, and begat twenty and two sons, and sixteen daughters.
Amma Abiya ya ƙara ƙarfi. Ya auri mata goma sha huɗu, ya kuma kasance da’ya’ya maza ashirin da biyu da kuma’ya’ya mata goma sha shida.
22 And the rest of the acts of Abiyah, and his ways, and his speeches, are written in the writing of the prophet 'Iddo.
Sauran ayyukan sauratar Abiya, abin da ya yi da abin da ya faɗa, a rubuce suke a cikin rubuce-rubucen annabi Iddo.

< 2 Chronicles 13 >