< 2 Chronicles 11 >

1 And when Rehobo'am was come to Jerusalem, he assembled the house of Judah and Benjamin a hundred and eighty thousand chosen men, warriors, to fight against Israel, to bring back the kingdom again to Rehobo'am.
Sa’ad da Rehobowam ya iso Urushalima, ya tattara mayaƙa dubu ɗari takwas daga gidan Yahuda da Benyamin, don su yi yaƙi da Isra’ila su sāke mai da mulki wa Rehobowam.
2 But the word of the Lord came unto Shema'yahu the man of God, saying,
Amma wannan maganar Ubangiji ta zo ga Shemahiya mutumin Allah.
3 Say unto Rehobo'am the son of Solomon, the king of Judah and Benjamin, saying,
“Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon sarkin Yahuda da kuma dukan Isra’ilawan da suke a Yahuda da Benyamin,
4 Thus hath said the Lord, Ye shall not go up, nor fight with your brethren: return every man to his house; for from me hath this thing been brought about. And they hearkened to the words of the Lord, and returned from going against Jerobo'am.
‘Ga abin da Ubangiji ya ce kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku. Ku tafi gida kowannenku, gama wannan yi na ne.’” Saboda haka suka yi biyayya ga maganar Ubangiji suka kuma koma daga takawa don yaƙi da Yerobowam.
5 And Rehobo'am dwelt in Jerusalem, and built cities as fortresses in Judah.
Rehobowam ya zauna a Urushalima ya kuma gina garuruwa don kāriya a cikin Yahuda.
6 He built, namely, Beth-lechem, and 'Etam, and Thekoa'.
Betlehem, Etam, Tekowa,
7 And Beth-zur, and Socho, and 'Adullam,
Bet-Zur, Soko, Adullam,
8 And Gath, and Mareshah, and Ziph,
Gat, Maresha, Zif,
9 And Adorayim and Lachish, and 'Azekah,
Adorayim, Lakish, Azeka,
10 And Zor'ah, and Ayalon, and Hebron, which are in Judah and in Benjamin, fortified cities.
Zora, Aiyalon da Hebron. Waɗannan su ne garuruwan katanga a cikin Yahuda da Benyamin.
11 And he strengthened the strong-holds, and put commanders in them, and stores of food, and oil and wine;
Ya ƙarfafa kāriyarsu ya kuma sa shugabannin mayaƙa a cikinsu, tare da tanadin abinci, man zaitun da kuma ruwan inabi.
12 And in each and every city [he placed] shields and spears, and made them exceedingly strong: and thus remained with him Judah and Benjamin.
Ya sa garkuwoyi da māsu a cikin dukan biranen, ya kuma sa suka zama da ƙarfi. Saboda haka Yahuda da Benyamin suka zama nasa.
13 And the priests and the Levites that were in all Israel presented themselves to him out of all their territory.
Firistoci da Lawiyawa daga dukan yankuna ko’ina a Isra’ila suka haɗa kai da shi.
14 For the Levites left their open districts and their possession, and went to Judah and Jerusalem; because Jerobo'am and his sons cast them off from executing the priest's office unto the Lord,
Lawiyawa suka ma bar makiyayansu da mallakarsu, suka zo Yahuda da Urushalima domin Yerobowam da’ya’yansa maza sun ƙi su a matsayin firistocin Ubangiji.
15 And [because] he ordained for himself priests for the high-places, and for the evil spirits, and for the calves which he had made.
Yerobowam ya naɗa firistocinsa domin masujadan kan tudu da kuma domin gumakan nan na akuya da maraƙin da ya yi.
16 And after them [came] out of all the tribes of Israel such as directed their heart to seek the Lord the God of Israel: these came to Jerusalem, to sacrifice unto the Lord, the God of their fathers.
Waɗanda suke daga kowane kabilar Isra’ila waɗanda suka sa zuciya a kan neman Ubangiji, Allah na Isra’ila, suka bi Lawiyawa zuwa Urushalima don su miƙa hadayu ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
17 And they strengthened the kingdom of Judah, and brought power to Rehobo'am, the son of Solomon, during three years; for they walked in the way of David and Solomon during three years.
Suka ƙarfafa mulkin Yahuda suka kuma goyi bayan Rehobowam ɗan Solomon shekaru uku, suna tafiya a hanyoyin Dawuda da Solomon a wannan lokaci.
18 And Rehobo'am took himself as wife Machalath the daughter of Jerimoth the son of David, [and] Abichayil the daughter of Eliab the son of Jesse;
Rehobowam ya auri Mahalat,’yar Yerimot ɗan Dawuda wadda Abihayil’yar Eliyab ɗan Yesse ta haifa.
19 And she bore to him sons: Je'ush, and Shamaryah, and Zaham.
Ta haifa masa’ya’ya maza. Yewush, Shemariya da Zaham.
20 And after her did he take Ma'achah the daughter of Abshalom; and she bore to him Abiyah, and 'Attai, and Ziza, and Shelomith.
Sa’an nan ya auri Ma’aka’yar Absalom, wadda ta haifa masa Abiya, Attai, Ziza da kuma Shelomit.
21 And Rehobo'am loved Ma'achah the daughter of Abshalom more than all his wives and his concubines; for he had taken eighteen wives and sixty concubines; and he begat twenty and eight sons, and sixty daughters.
Rehobowam ya ƙaunaci Ma’aka’yar Absalom fiye da sauran matansa da ƙwarƙwaransa. Duka-duka dai ya auri mata goma sha takwas da ƙwarƙwarai sittin, yana da’ya’ya maza ashirin da takwas da’ya’ya mata sittin.
22 And Rehobo'am appointed Abiyah the son of Ma'achah to be the chief, to be ruler among his brethren; because [he desired] to make him king.
Rehobowam ya naɗa Abiya ɗan Ma’aka yă zama babba yerima a cikin’yan’uwansa, don dai yă naɗa shi sarki.
23 And he dealt understandingly, and dispersed all his children throughout all the countries of Judah and Benjamin, unto all the fortified cities; and he gave them food in abundance and he required [for them] a multitude of wives.
Ya yi hikima, ya watsar da waɗansu’ya’yansa a dukan yankunan Yahuda da Benyamin, da kuma a dukan birane masu katanga. Ya ba su tanadi mai yawa ya kuma aurar musu mata masu yawa.

< 2 Chronicles 11 >