< 1 Samuel 1 >
1 And there was a certain man of Rama-thayim-zophim, of the mountain of Ephraim, whose name was Elkanah, the son of Yerocham, the son of Elihu, the son of Tochu, the son of Zuph, an Ephrathite.
Akwai wani mutum daga Ramatayim, mutumin Zuf daga ƙasar tuddan Efraim, sunansa Elkana, ɗan Yeroham, shi jikan Elihu ɗan Tohu, tattaɓa kunnen Zuf, mutumin Efraim.
2 And he had two wives; the name of the one was Hannah, and the name of the other Peninnah: Peninnah had children, but Hannah had no children.
Yana da mata biyu, ɗaya sunanta Hannatu, ɗayan kuwa ana kiranta Feninna. Ita Feninna tana da’ya’ya, amma Hannatu ba ta da’ya’ya.
3 And this man went up out of his city from year to year to prostrate himself and to sacrifice unto the Lord of hosts in Shiloh. And at that place were the two sons of 'Eli, Chophni and Phinehas, priests of the Lord.
Shekara-shekara wannan mutum yakan haura daga garinsa zuwa Shilo domin yin sujada da miƙa hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki. A can kuwa’ya’yan Eli maza biyu, Hofni da Finehas su ne firistoci na Ubangiji.
4 And when the day was come that Elkanah offered, he gave to Peninnah his wife, and to all her sons and her daughters, portions;
Duk sa’ad da rana ta kewayo don Elkana yă miƙa hadaya, yakan ba da kashin nama ga matarsa Feninna da dukan’ya’yanta maza da mata.
5 But unto Hannah he gave a double portion; for Hannah he loved [greatly]; but the Lord had shut up her womb.
Amma Hannatu kuwa sai yă ba ta babban rabo gama yana ƙaunarta ko da yake Ubangiji ya kulle mahaifarta.
6 And her rival also provoked her continually, in order to make her fret; because the Lord had shut up her womb.
Saboda Ubangiji ya kulle mahaifarta, sai kishiyarta ta dinga tsokanarta don tă ba ta haushi.
7 And he did so year by year, as often as she went up to the house of the Lord, so did she provoke her; wherefore she wept, and did not eat.
Wannan ya ci gaba shekara da shekaru. Duk lokacin da Hannatu ta haura zuwa haikalin Ubangiji, sai kishiyarta tă tsokane ta har tă yi ta kuka tă kuma ƙi cin abinci.
8 Then said to her Elkanah her husband, Hannah, why wilt thou weep? and why wilt thou not eat? and why should thy heart be grieved? am not I better to thee than ten sons?
Elkana mijinta kuwa yakan ce mata, “Hannatu don me kike kuka? Me ya sa ba za ki ci abinci ba? Don me kika karaya? Ashe, ban fi’ya’ya goma a gare ki ba?”
9 And Hannah rose up after they had eaten in Shiloh, and after they had drunk; and 'Eli the priest was sitting upon a chair by the door-post of the temple of the Lord.
Wata rana sa’ad da suka gama ci da sha a Shilo, Hannatu ta miƙe tsaye. Eli firist kuwa yana zaune a kujera a bakin ƙofar haikalin Ubangiji.
10 But she had bitterness of soul, and prayed unto the Lord, and wept greatly.
A cikin baƙin ciki, Hannatu ta yi kuka mai zafi ta yi addu’a ga Ubangiji.
11 And she vowed a vow, and said, O Lord of hosts, if thou wilt indeed look on the affliction of thy handmaid, and remember me, and not forget thy handmaid, but wilt give unto thy handmaid a man-child: then will I give him unto the Lord all the days of his life, and no razor shall come upon his head.
Ta yi ta cewa, “Ya Ubangiji Maɗaukaki. In har ka dubi baƙin cikin baiwarka, ka tuna da ni, ba ka kuma manta da baiwarka ba, amma ka ba ta ɗa, ni ma zan miƙa shi ga Ubangiji dukan rayuwarsa, aska kuwa ba za tă taɓa kansa ba.”
12 And it came to pass, as she continued praying long before the Lord, that 'Eli watched her mouth.
Yayinda take addu’a ga Ubangiji, Eli ya lura da bakinta.
13 Now as for Hannah, she spoke in her heart; only her lips moved, but her voice could not be heard; wherefore 'Eli regarded her as a drunken woman.
Hannatu tana addu’a a zuci, ba a jin muryarta, sai leɓunanta ne kawai suna motsi. Eli kuwa ya yi tsammani ta bugu ne.
14 And 'Eli said unto her, How long wilt thou be drunken? put away thy wine from off thee.
Sai ya ce mata, “Har yaushe za ki ci gaba da maye? Ki daina shan ruwan inabi.”
15 And Hannah answered and said, No, my Lord, I am a woman of a sorrowful spirit; but neither wine nor strong drink have I drunk, and I have poured out my soul before the Lord.
Hannatu ta ce, “Ba haka ba ne, ranka yă daɗe, ni mace ce da take cikin matsala ƙwarai da gaske. Ban sha ruwan inabi ba, ko wani abu mai sa maye, ina dai faɗa wa Ubangiji abin da yake damuna ne.
16 Esteem not thy handmaid as a worthless woman; for out of the abundance of my grief and vexation have I spoken hitherto.
Kada ka yi zato baiwarka’yar iska ce. Ina addu’a a nan saboda yawan azaba da baƙin cikin da nake ciki.”
17 Then 'Eli answered and said, Go in peace; and may the God of Israel grant thy petition which thou hast asked of him.
Eli ya ce, “In haka ne, to, ki sauka lafiya, Allah na Isra’ila kuma yă ba ki abin da kika roƙa daga gare shi.”
18 And she said, Let thy handmaid find grace in thy eyes. The woman then went on her way, and did eat, and her countenance was no longer as before.
Ta ce, bari baiwarka tă sami tagomashi a idonka. Sai ta yi tafiyarta ta je ta ci wani abu, fuskarta kuwa ba tă ƙara kasance da baƙin ciki ba.
19 And they rose up early in the morning, and prostrated themselves before the Lord, and returned, and came to their house at Ramah; and Elkanah knew Hannah his wife; and the Lord remembered her.
Kashegari da sassafe suka tashi suka yi sujada a gaban Ubangiji, sai suka koma garinsu a Rama. Elkana kuwa ya kwana da matarsa Hannatu, Ubangiji kuma ya tuna da ita.
20 And it came to pass, after the lapse of some time, that Hannah conceived, and bore a son; and she called his name Samuel, saying, Because from the Lord have I asked him.
Ana nan sai Hannatu ta yi ciki, ta kuma haifi ɗa. Ta ba shi suna Sama’ila; tana cewa, “Domin na roƙe shi daga wurin Ubangiji.”
21 And the man Elkanah went up, with all his house, to offer unto the Lord the yearly sacrifice, and his vow.
Da shekara ta kewayo, sai Elkana da iyalinsa suka sāke tafi Shilo domin su yi hadaya ga Ubangiji, yă kuma cika alkawarin da ya yi.
22 But Hannah did not go up; for she said unto her husband, So soon as the child shall be weaned, then I will bring him, that he may appear before the Lord, and abide there for ever.
Hannatu kuwa ba tă bi su ba. Ta gaya wa mijinta cewa, “Sai bayan na yaye yaron, zan kai shi in miƙa shi a gaban Ubangiji, yă kuma kasance a wurin koyaushe.”
23 And Elkanah her husband said unto her, Do what seemeth good in thy eyes; tarry until thou hast weaned him; only may the Lord fulfill his word. So the woman remained behind, and gave her son suck until she weaned him.
Elkana mijinta ya ce mata, “Ki yi abin da kika ga ya fi miki kyau. Ki jira har sai bayan kin yaye shi. Ubangiji dai ya cika maganarsa.” Saboda haka matar ta tsaya a gida, ta yi ta renon ɗanta har ta yaye shi.
24 And she took him up with her, when she had weaned him, with three bullocks, and one ephah of flour, and a bottle of wine, and she brought him unto the house of the Lord at Shiloh; although the child was yet young.
Bayan ta yaye shi, sai ta ɗauki yaron tare da bijimi bana uku, da mudun gari, da salkan ruwan inabi, ta kawo su a gidan Ubangiji a Shilo.
25 And they slew a bullock, and brought the child to 'Eli.
Bayan an yanka bijimin, sai suka kawo yaron wurin Eli.
26 And she said, Pardon, my Lord, as thy soul liveth, my Lord, I am the woman that stood by thee here, to pray unto the Lord.
Sai ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ba ka gane ni ba? Ai, ni ce matar da ta taɓa tsayawa a gabanka, tana addu’a ga Ubangiji.
27 For this lad did I pray; and the Lord hath granted me my petition which I asked of him;
Wannan yaron ne na roƙa daga wurin Ubangiji, ya kuwa ba ni abin da na roƙa daga gare shi.
28 Therefore also have I lent him, for my part, to the Lord; all the days that have been assigned to him shall he be lent to the Lord. And he bowed himself there before the Lord.
Saboda haka, na ba da shi ga Ubangiji muddin ransa, zai zama na Ubangiji.” A can kuwa ya yi wa Ubangiji sujada.