< 1 Samuel 5 >

1 And the Philistines took the ark of God, and brought it from Eben-ha'ezer unto Ashdod.
Bayan Filistiyawa sun ƙwace akwatin alkawarin Allah, sai suka ɗauke shi daga Ebenezer suka kai shi Ashdod.
2 And the Philistines took the ark of God, and brought it into the house of Dagon, and set it by Dagon.
Sa’an nan suka ɗauki akwatin alkawarin suka kai shi cikin haikalin gunkinsu Dagon, suka ajiye kusa da Dagon.
3 And when the people of Ashdod arose early on the morrow, behold, Dagon was lying upon his face on the earth before the ark of the Lord. And they took Dagon, and set him again in his place.
Kashegari da safe da mutanen Ashdod suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a gaban akwatin alkawarin Ubangiji. Sai suka ɗauki Dagon suka ajiye a wurin zamansa.
4 And when they arose early on the morning of the following day, behold, Dagon was lying upon his face on the ground before the ark of the Lord; and the head of Dagon and both the palms of his hands were cut off upon the threshold; only the fish portion was left on him.
Amma kashegari kuma da safe suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a ƙasa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji! Kansa ya fashe, hannuwansa kuma sun kakkarye sun zube a madogarar ƙofa; jikinsa ne kaɗai ya rage.
5 Therefore do the priests of Dagon, and all that come into Dagon's house, not step on the threshold of Dagon in Ashdod even until this day.
Saboda haka firistocin Dagon da waɗanda suke sujada a haikalin Dagon ba sa taka bakin ƙofar Dagon a Ashdod har wa yau.
6 And the hand of the Lord became heavy upon the people of Ashdod, and he destroyed them, and smote them with hemorrhoids, even Ashdod and its territory.
Hannun Ubangiji kuwa ya yi nauyi a bisa Ashdod da kewayenta. Ya kawo hallaka ga dukansu, ya kuma buga su da marurai.
7 And when the men of Ashdod saw that it was so, they said, The ark of the God of Israel shall not remain with us; for his hand is sore upon us, and upon Dagon our God.
Da mutanen Ashdod suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Lalle Akwatin Alkawarin Allah na Isra’ila ba zai kasance da mu ba, domin hannunsa yana da nauyi a kanmu da bisan Dagon allahnmu.”
8 And they sent and gathered together all the lords of the Philistines unto them, and said, What shall we do with the ark of the God of Israel? And they answered, Let the ark of the God of Israel be removed unto Gath. And they removed the ark of the God of Israel thither.
Saboda haka suka kira duka shugabannin Filistiyawa suka tambaye su, suka ce, “Me za mu da akwatin alkawarin Allahn Isra’ila?” Sai suka amsa suka ce, “A ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila a kai shi Gat.” Sai suka ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila.
9 And it happened, after they had removed it, that the hand of the Lord was against the city with a very great confusion; and he smote the men of the city, both small and great, and they had hemorrhoids in their secret parts.
Amma bayan sun kai shi can, sai hannun Ubangiji ya yi gāba da birnin, aka jefa shi cikin wani mawuyacin hali. Ya buga mutanen birnin da marurai, babba da yaro.
10 And they sent away the ark of God to 'Ekron. And it came to pass, as the ark of God came to 'Ekron, that the 'Ekronites cried out, saying, They have removed to us the ark of the God of Israel, to slay us and our people.
Sai suka aika da akwatin alkawarin Allah zuwa Ekron. Yayinda akwatin alkawarin Allah yana shiga cikin Ekron, mutanen Ekron suka yi ihu, suka ce, “An kawo mana akwatin alkawarin Allah na Isra’ila domin yă kashe mu da mutanenmu.”
11 So they sent and gathered together all the lords of the Philistines, and said, Send away the ark of the God of Israel, that it may return to its own place, so that it may not slay us, and our people; for there was a confusion of death throughout all the city; the hand of God was very heavy there.
Saboda haka suka kira ga dukan shugabannin Filistiyawa suka ce, “Ku komar da akwatin alkawarin Allah na Isra’ila inda ya fito; in ba haka ba zai kashe mu da mutanenmu.” Gama mutuwa ta cika garin da tsoro. Hannun Allah ya yi nauyi a kansa.
12 And the people that did not die were smitten with the hemorrhoids; and the lamentation of the city went up to heaven.
Waɗanda ba su mutu ba kuwa, sun kamu da marurai. Kukan birnin kuwa ta hau har zuwa sama.

< 1 Samuel 5 >