< 1 Samuel 23 >

1 Then they told David, saying, Behold, the Philistines are fighting against Ke'ilah, and they are plundering the threshing-floors.
Sa’ad da aka ce wa Dawuda, “Duba ga Filistiyawa suna yaƙi da mutanen Keyila, suna kwashe musu hatsi a masussukai.”
2 Thereupon David asked counsel of the Lord, saying, Shall I go and smite among these Philistines? And the Lord said unto David, Go and smite among the Philistines, and deliver Ke'ilah.
Sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya ce, “In tafi in fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi?” Ubangiji kuwa ya ce masa, “Jeka ka yi yaƙi da Filistiyawa, ka ceci Keyila.”
3 And David's men said unto him, Behold, here in Judah are we afraid: how much more then if we should go to Ke'ilah against the battle-arrays of the Philistines?
Amma mutanen Dawuda suka ce masa, “Ga shi, a nan ma a Yahuda muna jin tsoro, balle mu tafi Keyila mu yi yaƙi da sojojin Filistiyawa!”
4 Then David asked yet again counsel of the Lord. And the Lord answered him and said, Arise, Go down to Ke'ilah; for I [will] deliver the Philistines into thy hand.
Dawuda ya sāke nemi nufin Ubangiji, sai Ubangiji ya ce masa, “Tashi ka gangara zuwa Keyila, gama zan ba da Filistiyawa a hannunka.”
5 So David and his men went to Ke'ilah; and he fought with the Philistines, and lead away their cattle, and smote among them a great slaughter. So David delivered the inhabitants of Ke'ilah.
Sa’an nan Dawuda da mutanensa suka tafi Keyila, suka yi yaƙi da Filistiyawa, suka kwashe musu shanunsu, suka jijji wa Filistiyawa ƙwarai, suka cece mutanen Keyila daga hannunsu.
6 And it came to pass, when Ebyathar the son of Achimelech, fled over to David, to Ke'ilah, that the ephod came down with him.
(Abiyatar ɗan Ahimelek ya zo da efod sa’ad da ya gudo zuwa wurin Dawuda a Keyila.)
7 And it was told to Saul that David was come to Ke'ilah. And Saul said, God hath delivered him into my hand; for he is shut in, by entering into a town that hath gates and bars.
Shawulu ya sami labari cewa Dawuda ya tafi Keyila, sai ya ce, “Allah ya bashe shi a hannuna, domin Dawuda ya kulle kansa ke nan da ya shiga birnin da yake da ƙofofin da ake kulle da ƙarafa.”
8 And Saul called all the people together to war, to go down to Ke'ilah, to besiege David and his men.
Shawulu ya kira dukan sojojinsa don yaƙi, su gangaro zuwa Keyila su mamaye Dawuda da mutanensa.
9 And David understood that Saul secretly devised mischief against him; and he said to Ebyathar the priest, Bring hither the ephod.
Da Dawuda ya ji labari Shawulu yana shirya hanyar da zai kashe shi, sai ya ce wa Abiyatar firist, “Kawo mini efod a nan.”
10 Then said David, O Lord, God of Israel, thy servant hath heard for certain that Saul seeketh to come to Ke'ilah, to destroy the city for my sake.
Dawuda ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bawanka ya sami labari cewa tabbatacce Shawulu yana shirin zuwa Keyila yă hallaka garin saboda ni.
11 Will the men of Ke'ilah surrender me into his hand? will Saul come down as thy servant hath heard? O Lord, God of Israel, I beseech thee, tell thy servant. And the Lord said, He will come down.
Mutanen Keyila za su bashe ni a gare shi? Shawulu zai gangaro nan kamar yadda bawanka ya sami labari? Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka gaya wa bawanka.” Ubangiji ya ce, “Zai zo.”
12 Then said David, Will the men of Ke'ilah surrender me and my men into the hand of Saul! And the Lord said, They will surrender.
Dawuda ya sāke cewa, “Mutanen Keyila za su bashe ni da mutanena ga Shawulu?” Ubangiji ya ce, “Za su yi.”
13 Then arose David and his men, about six hundred men, and departed out of Ke'ilah, and wandered about whithersoever they could go. And when it was told to Saul that David was escaped from Ke'ilah, he forbore to go forth.
Saboda haka Dawuda da mutanensa wajen mutum ɗari shida suka bar Keyila, suka yi ta tafiya daga wannan wuri zuwa wancan. Sa’ad da aka gaya wa Shawulu cewa Dawuda ya tsere daga Keyila, sai ya fasa tafiya can.
14 And David remained in the wilderness in strong-holds, and abode on the mountain in the wilderness of Ziph. And Saul sought him all the time, but God delivered him not into his hand.
Dawuda ya zauna a jeji cikin kogunan duwatsu da kuma tuddan jejin Zif. Kowace rana Shawulu ya yi ta neman Dawuda amma Allah bai bashe Dawuda a hannunsa ba.
15 And David saw that Saul was gone forth to seek his life: and David was in the wilderness of Ziph in the forest.
A lokacin da Dawuda yana zaune a Horesh cikin jejin Zif, ya sami labari cewa Shawulu ya fito don yă kashe shi.
16 And Jonathan, the son of Saul, arose and went to David into the forest, and strengthened his hand in God.
Yonatan ɗan Shawulu kuwa ya tafi wurin Dawuda a Horesh, ya ƙarfafa shi yă dogara ga Allah.
17 And he said unto him, Fear not; for the hand of Saul my father will not find thee; and thou wilt be king over Israel, and I will be next unto thee; and also Saul my father knoweth this.
Ya ce, “Kada ka ji tsoro, mahaifina Shawulu ba zai taɓa sa hannu a kanka ba. Za ka zama sarki a Isra’ila, ni kuma in zama na biyu gare ka. Kai, ko mahaifina Shawulu ma ya san da haka.”
18 And they made, both of them, a covenant before the Lord: and David remained in the forest; but Jonathan went to his house.
Su biyunsu kuwa suka ɗaura yarjejjeniya a gaban Ubangiji. Sai Yonatan ya koma gida amma Dawuda ya zauna Horesh.
19 Then came up the Ziphites unto Saul to Gib'ah, saying, Behold, David is hiding himself with us in the strong-holds in the forest, on the hill of Chachilah, which is on the right of the desert.
Zifawa suka tafi wurin Shawulu a Gibeya suka ce masa, “Ashe, ba Dawuda ne yake ɓuya a cikinmu a kogwannin duwatsu a Horesh a bisan tudun Hakila, kudu da Yeshimon ba?
20 And now in accordance with all the longing of thy soul, O king, to come down, come down; and our part shall be to surrender him into the king's hand.
Yanzu, ya sarki, ka gangaro, ka zo a duk lokacin da ka ga ya yi maka, ka zo mu kuma hakkinmu ne mu bashe shi a hannun sarki.”
21 And Saul said, Blessed be ye of the Lord; for ye have pity on me.
Shawulu ya ce, “Ubangiji ya yi muku albarka, gama kun damu da ni.
22 Go, I pray you, make yet more preparations, and remark and see his place where his foot may be, who hath seen him there; for I am told that he dealeth with great subtilty.
Ku tafi ku ƙara shiri. Ku san inda yakan tafi, wane ne kuma ya gan shi a can. An gaya mini cewa shi mai wayo ne sosai.
23 See therefore, and remark every one of all the lurking-places where he usually hideth himself, and come ye again to me with the certainty, and I will go with you; and it shall come to pass, if he be in the land, that I will search him out throughout all the thousands of Judah.
Ku binciko duk wuraren da yakan ɓuya, sai ku dawo ku gaya mini tabbataccen labari. Sa’an nan zan tafi tare da ku in yana can. Zan nemi shi ko’ina cikin dukan kabilar Yahuda.”
24 And they arose, and went to Ziph before Saul; but David and his men were in the wilderness of Ma'on, in the plain on the right of the desert.
Sai suka tashi suka koma Zif, suka sha gaban Shawulu. Dawuda da mutanensa kuwa suna jejin Mawon cikin Araba, kudu da Yeshimon.
25 And Saul and his men went to make a search. And they told it to David: wherefore he came down to the rock, and abode in the wilderness of Ma'on. And when Saul heard this, he pursued after David into the wilderness of Ma'on.
Shawulu da mutanensa suka tafi neman Dawuda. Da Dawuda ya ji labari, sai ya gangara cikin duwatsu ya zauna a cikin jejin Mawon. Sa’ad da Shawulu ya ji haka, sai ya tafi jejin Mawon yana fafaran Dawuda.
26 And Saul went on this side of the mountain, and David and his men on that side of the mountain; and David made haste to get away from before Saul; and Saul and his men were compassing David and his men to seize them.
Shawulu yana tafiya a gefe ɗaya na dutsen, Dawuda da mutanensa kuma suna a wancan gefe, suna hanzari su ɓace wa Shawulu. Sa’ad da Shawulu da sojojinsa suka kusa cimma Dawuda da mutanensa don su kama su,
27 But a messenger came unto Saul, saying, Haste thee, and come; for the Philistines have invaded the land.
sai wani manzo ya zo wurin Shawulu yana cewa, “Ka koma da sauri, Filistiyawa sun kawo wa ƙasar hari.”
28 Wherefore Saul returned from pursuing after David, and went against the Philistines: therefore they called that place Sela-hammachlekoth.
Shawulu kuwa ya janye daga fafaran Dawuda, ya tafi yă ƙara da Filistiyawa. Dalilin ke nan da ake kiran wannan wuri Sela Hammalekot, wato, dutsen tserewa.
29 And David went up from there, and dwelt in strong-holds of 'En-gedi.
Dawuda kuwa ya haura daga can ya zauna a kogwannin duwatsun En Gedi.

< 1 Samuel 23 >