< 1 Samuel 18 >
1 And it came to pass, when he had made an end of speaking unto Saul, that the soul of Jonathan was knit on the soul of David; and Jonathan loved him as his own soul.
Bayan da Dawuda ya gama magana da Shawulu, sai Yonatan ɗan Shawulu ya ji zuciyarsa tana son Dawuda sosai. Yonatan kuwa yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
2 And Saul took him on that day, and would not permit him to go home to his father's house.
Tun daga wannan rana Shawulu ya zaunar da Dawuda tare da shi, bai bar shi ya koma gidan mahaifinsa ba.
3 Then Jonathan and David made a covenant, because of his loving him as his own soul.
Yonatan kuma ya yi yarjejjeniya da Dawuda saboda yana ƙaunarsa kamar ransa.
4 And Jonathan stripped himself of the robe that he had upon him, and gave it to David, and likewise his garments, even to his sword, and to his bow, and to his girdle.
Yonatan ya tuɓe doguwar taguwarsa da ya sa, ya ba wa Dawuda, tare da sulkensa, har ma da māshi da kibiyarsa, da kuma bel nasa.
5 And David went out; whithersoever Saul used to send him, he was successful; and Saul set him over the men of war; and he was accepted in the eyes of all the people, and also in the eyes of the servants of Saul.
Duk abin da Shawulu ya aiki Dawuda yă yi yakan yi shi cikin aminci, har Shawulu ya ba shi babban makami a rundunarsa. Wannan ya faranta wa dukan mutane zuciya har ma da ma’aikatan Shawulu.
6 And it came to pass as they came home, when David returned from smiting the Philistines, that the women came forth out of all the cities of Israel, singing and dancing, to meet king Saul, with tambourines, with joy, and with triangles.
Yayinda mutane suke dawowa gida bayan da Dawuda ya kashe Bafilistin, mata suka fito daga dukan biranen Isra’ila don su sadu da Sarki Shawulu, suna waƙoƙi da raye-raye masu farin ciki, da ganguna da sarewa.
7 And the women that played answered one another, and said, Saul hath slain his thousands, and David his ten thousands.
Suna rawa suna cewa, “Shawulu ya kashe dubbansa, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai.”
8 And Saul was very wroth, and this saying was displeasing in his eyes; and he said, They have given unto David ten thousands, and to me they have given the thousands: and all that he lacketh now yet is only the kingdom.
Shawulu kuwa ya ji fushi, wannan magana ba tă yi masa daɗi ba, ya yi tunani ya ce, “Suna yabon Dawuda cewa ya kashe dubun dubbai amma ni dubbai kawai. Me ya rage masa yanzu, in ba mulki ba?”
9 And Saul looked jealous on David from that day and forward.
Tun daga wannan lokaci zuwa gaba, Shawulu ya dinga kishin Dawuda.
10 And it came to pass on the morrow, that an evil spirit from God came suddenly over Saul, and he spoke foolish things in the midst of the house: while David was playing with his hand, as on previous days; and the spear was in the hand of Saul.
Kashegari, mugun ruhu daga Allah ya fāɗo wa Shawulu da tsanani. Yana annabci a gidansa, Dawuda kuwa yana bugan molo kamar yadda ya saba. Shawulu yana riƙe da māshi a hannunsa.
11 And Saul cast the spear; and he thought, I will strike David through even on the wall. And David turned aside out of his presence twice.
Da ƙarfi yana magana da kansa yana cewa, “Zan kafe Dawuda da bango.” Amma Dawuda ya bauɗe masa sau biyu.
12 And Saul was afraid of David; because the Lord was with him, and from Saul he was departed.
Shawulu ya ji tsoron Dawuda don Ubangiji yana tare da shi, amma Ubangiji ya riga ya bar Shawulu.
13 Therefore Saul removed him from himself, and made him his captain over a thousand: and he went out and came in before the people.
Saboda haka Shawulu bai yarda Dawuda yă zauna tare da shi ba, amma ya maishe shi shugaban sojoji dubu. Dawuda kuwa ya riƙa bi da su yana kaiwa yana kuma da tare da su.
14 And David was successful on all his ways; and the Lord was with him.
A kome da Dawuda ya yi yakan yi nasara gama Ubangiji yana tare da shi.
15 And when Saul saw that he was very successful, he was in dread of him.
Da Shawulu ya ga yadda yake cin nasara, sai ya ji tsoronsa.
16 But all Israel and Judah loved David; because he went out and came in before them.
Amma dukan Isra’ila da Yahuda suka ƙaunaci Dawuda gama yana bin da su a yaƙe-yaƙensu.
17 And Saul said to David, Behold, here is my eldest daughter Merab, her will I give to thee for wife: only be thou unto me a man of valor, and fight the Lord's battles. And Saul thought, Let not my hand be against him, but let the hand of the Philistines be against him.
Shawulu ya ce wa Dawuda, “Ga diyata Merab zan ba ka ka aura, kai dai ka yi mini aiki da himma, ka kuma yi yaƙe-yaƙen Ubangiji.” Saboda Shawulu ya ce wa kansa, “Ba zan ɗaga hannuna a kansa ba, Filistiyawa ne za su yi wannan.”
18 And David said unto Saul, Who am I? and what is my life, [or] my father's family in Israel, that I should be a son-in-law to the king?
Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Wane ni, wa ya san iyayena ko kabilar iyayena a Isra’ila da zan zama surukin sarki?”
19 But it happened at the time when Merab, Saul's daughter should have been given to David, that she was given unto 'Adriel the Mecholathite for wife.
Da lokaci ya kai da Merab’yar Shawulu za tă yi aure da Dawuda, sai aka aurar da ita wa Adriyel na Mehola.
20 And Michal Saul's daughter loved David: and they told it to Saul, and the thing was right in his eyes.
Mikal’yar Shawulu kuwa tana ƙaunar Dawuda sosai. Da aka gaya wa Shawulu labarin, sai ya yi farin ciki, ya yi tunani ya ce,
21 And Saul said, I will give her to him, that she may become unto him a snare, and that the hand of the Philistines may be against him. Wherefore Saul said to David, Through the second shalt thou this day become my son-in-law.
“Zan ba shi ita tă zama masa tarko, da haka Filistiyawa za su same shi.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Yanzu kana da dama sau na biyu ka zama surukina.”
22 And Saul commanded his servants, Speak to David secretly, saying, Behold, the king hath delight in thee, and all his servants love thee; and now thou must become the king's son-in-law.
Sai Shawulu ya umarci ma’aikatansa cewa, “Ku yi magana da Dawuda asirce ku ce, ‘Duba, sarki yana farin ciki da kai, dukan ma’aikatansa kuma suna sonka, ka yarda ka zama surukinsa.’”
23 And the servants of Saul spoke in the ears of David these words. And David said, Doth it seem so light in your eyes to become the king's son-in-law, seeing that I am a poor man, and of light esteem?
Suka sāke yi wa Dawuda wannan magana amma Dawuda ya ce, “Kuna tsammani abu mai sauƙi ne mutum yă zama surukin sarki? Ni talaka ne, kuma ba sananne ba.”
24 And the servants of Saul told him, saying, Words such as these David hath spoken.
Da ma’aikatan Shawulu suka gaya masa abin da Dawuda ya faɗa.
25 And Saul said, Thus shall ye say to David, The king desireth not any dowry, but a hundred foreskins of the Philistines, to be avenged on the king's enemies. But Saul thought to cause David to fall by the hand of the Philistines.
Sai Shawulu ya ce, “Ku gaya wa Dawuda, ‘Sarki ba ya bukatan kuɗin auren’yarsa, sai dai loɓar Filistiyawa domin ramako a kan abokan gābansa.’” Shawulu yana shiri ne domin Dawuda yă fāɗa a hannun Filistiyawa.
26 And when his servants told David these words, the thing was pleasing in the eyes of David to become the king's son-in-law: and the days were not complete,
Da ma’aikatan suka gaya wa Dawuda waɗannan abubuwa, sai ya yi murna don zai zama surukin sarki. Amma kafin lokacin yă cika,
27 When David arose and went, he and his men, and smote of the Philistines two hundred men; and David brought their foreskins, and they counted them out in full to the king, that he might become the king's son-in-law. And Saul gave him Michal his daughter for wife.
Dawuda da mutanensa suka fita suka kashe Filistiyawa ɗari biyu, suka kawo loɓar suka miƙa wa sarki, domin yă zama surukin sarki. Sai Shawulu ya ba da’yarsa Mikal aure ga Dawuda.
28 And Saul saw and understood that the Lord was with David: and Michal, Saul's daughter, loved him.
Da Shawulu ya gane Ubangiji yana tare da Dawuda,’yarsa Mikal kuma tana ƙaunarsa,
29 And Saul was yet the more afraid of David; and Saul was David's enemy all the time.
sai Shawulu ya ƙara jin tsoron Dawuda har ya zama maƙiyinsa a dukan sauran rayuwarsa.
30 And the princes of the Philistines went forth; and it came to pass, whenever they went forth, that David was more successful than all the servants of Saul; so that his name was highly prized.
Manyan sojojin Filistiyawa suka yi ta fita suna yaƙi da Isra’ilawa, amma kullum Dawuda yakan sami nasara fiye da sauran manyan sojojin Shawulu. Ta haka ya yi suna ƙwarai.