< 1 Samuel 17 >

1 And the Philistines gathered together their camps to battle, and they gathered themselves together at Sochoh, which belongeth to Judah; and they encamped between Sochoh and 'Azekah, at Ephess-dammim.
To, fa, Filistiyawa suka tattara mayaƙansu suka haɗu a Soko cikin Yahuda domin yaƙi. Suka yi sansani a Efes-Dammim, tsakanin Soko da Azeka.
2 And Saul and the men of Israel gathered themselves together, and encamped in the valley of Elah, and put themselves in battle-array opposite to the Philistines.
Shawulu da Isra’ilawa suka taru suka yi sansani a Kwarin Ela suka ja dāgā don su yi yaƙi da Filistiyawa.
3 And the Philistines stood on a mountain on the one side, and the Israelites stood on a mountain on the other side: and the valley was between them.
Filistiyawa suka zauna a tudu guda, Isra’ilawa kuma suka zauna a ɗaya tudun. Kwari yana a tsakaninsu.
4 And there went out the champion out of the camp of the Philistines, Goliath of Gath was his name, whose height was six cubits and a span.
Wani jarumin da ake kira Goliyat wanda ya fito daga Gat, ya fita daga sansanin Filistiyawa. Tsawonsa ya fi ƙafa tara.
5 And he had a helmet of copper upon his head, and he was clothed with a scaly coat of mail; and the weight of the coat of mail was five thousand shekels of copper.
Ya sa hular kwanon da aka yi da tagulla, da rigar ƙarfe mai sulke, nauyin rigar ya kai shekel dubu biyar.
6 And he had greaves of copper upon his legs, and a javelin of copper between his shoulders.
A ƙafafunsa kuwa ya sa ƙarafar tagulla, rataye a bayansa kuma māshi ne na tagulla.
7 And the staff of his spear was like a weaver's beam; and the blade of his spear [weighed] six hundred shekels of iron: and the shield-bearer was walking before him.
Ƙotar kibiyarsa kuwa kamar sandar saƙar igiya take, ƙarfen kibiyar kuma nauyinsa ya kai shekel ɗari shida. Mai riƙe masa garkuwa yana tafe a gabansa.
8 And he stood and calleth unto the arrays of Israel, and said unto them, Why will ye come out to put yourselves in battle-array? Behold: I am the Philistine, and ye are servants to Saul! select for yourselves one man, and let him come down to me;
Goliyat ya tsaya ya tā da murya wa hafsoshin Isra’ila ya ce, “Me ya sa kuka fito kuna layi don yaƙi? Ni ba Bafilistin ba ne? Ku kuma ba bayin Shawulu ba ne? Ku zaɓi waninku yă zo nan.
9 If he be able to fight with me, and he kill me, then will we be unto you as servants; but if I prevail against him, and kill him, then shall ye be unto us as servants, and ye shall serve us.
In zai iya yin faɗa har yă kashe ni, to, za mu zama bayinku. Amma in na fi ƙarfinsa na kashe shi, to, sai ku zama bayinmu, ku kuma yi mana bauta.”
10 And the Philistine said, I have defied the arrays of Israel this day; give me a man, and let us fight together.
Sai Bafilistin ya ce, “A wannan rana, na kalubalanci sojojin Isra’ila, ku ba ni mutum ɗaya mu yi faɗa.”
11 When Saul and all Israel heard these words of the Philistine, they were disheartened, and became greatly afraid.
Da jin maganganun Bafilistin, sai Shawulu da dukan Isra’ila suka damu suka kuma ji tsoro.
12 Now David was the son of that Ephrathite of Beth-lechem-judah, whose name was Jesse; and he had eight sons: and the man was old in the days of Saul, belonging to the persons [of high esteem].
To, Dawuda dai ɗan wani mutumin Efratawa ne mai suna Yesse, shi mutumin Betlehem ne a cikin Yahudiya. Yesse yana da yara maza takwas, a zamanin Shawulu kuwa, Yesse ya riga ya tsufa.
13 And the three eldest sons of Jesse were gone following Saul to the battle: and the names of his three sons that were gone to the battle were Eliab the first-born, and the next to him Abinadab, and the third Shammah.
Manyan’ya’yansa maza uku, sun bi Shawulu wajen yaƙi. Ɗansa na fari shi ne Eliyab, na biyu shi ne Abinadab, na uku kuwa shi ne Shamma.
14 And David was the youngest: and the three eldest followed Saul.
Dawuda shi ne ɗan autansu. Manyan’yan mazan nan uku suka bi Shawulu.
15 But David kept going and returning from Saul to feed his father's flocks at Beth-lechem.
Amma Dawuda yakan tafi sansanin Shawulu lokaci-lokaci yă kuma koma Betlehem don yă yi kiwon tumakin mahaifinsa.
16 And the Philistine drew near morning and evening, and presented himself forty days.
Kwana arba’in cif, Bafilistin nan ya yi ta fitowa kowane safe da kuma kowace yamma.
17 And Jesse said unto David his son, Take, I pray thee, for thy brothers an ephah of this parched corn, and these ten loaves, and run to the camp to thy brothers;
Yesse ya ce wa ɗansa Dawuda, “Ka ɗauki wannan gasasshen hatsi da waɗannan curin burodi goma, ka kai wa’yan’uwanka a sansani da sauri.
18 And these ten cheeses shalt thou bring unto the captain of the thousand, and inquire of thy brothers how they fare, and take away their pledge.
Ka haɗa da waɗannan cuku guda goma, ka kai wa komandan rundunarsu. Ka ga lafiyar’yan’uwanka, ka kawo mini labari daga wurinsu.
19 Now Saul, and they, and all the men of Israel, were in the valley of Elah, fighting with the Philistines.
Suna tare da Shawulu da kuma dukan mutanen Isra’ila a Kwarin Ela, suna can suna yaƙi da Filistiyawa.”
20 And David rose up early in the morning, and gave up the flocks to a keeper, and took, and went, as Jesse had commanded him; and he came to the entrenchment, as the host was going forth in battle-array, and shouted the battle-cry.
Kashegari da sassafe, Dawuda ya tashi ya bar tumakinsa wa wani yă lura da su, sai ya ɗauki kayansa, ya kama hanya kamar yadda Yesse ya umarce shi. Ya isa sansanin daidai sa’ad da rundunar tana fitowa zuwa bakin dāgā, suna kirarin yaƙi.
21 And the Israelites and the Philistines put themselves in battle-array, army against army.
Isra’ila da Filistiyawa suka ja dāgā suna fuskantar junansu.
22 And David left the articles which he had on him in the hand of the keeper of the baggage, and ran into the array, and came and asked of his brothers after their welfare.
Dawuda ya bar kayansa a wajen wani mai lura da kaya, sai ya ruga zuwa bakin dāgā yă gai da’yan’uwansa.
23 And as he was speaking with them, behold, there came up the champion, Goliath the Philistine, by name, of Gath, out of the battle-arrays of the Philistines, and spoke in accordance with these same words: and David heard it.
Da yana magana da su sai Goliyat, jarumin nan Bafilistin daga Gat ya fito daga rundunar Filistiyawa, ya tā da murya kamar yadda ya saba. Dawuda kuwa ya ji shi.
24 And all the men of Israel, when they saw the man, fled from before him, and were greatly afraid.
Da Isra’ilawa suka ga mutumin, sai dukansu suka gudu saboda tsananin tsoro.
25 And the men of Israel said, Have ye seen this man that is coming forth? for to defy Israel is he coming forth; and it shall be, that the man who killeth him, —him will the king enrich with great riches, and his daughter will he give him, and his father's house will he make free in Israel.
Isra’ilawa suka yi ta cewa, “Kun ga yadda wannan mutum yana ta fitowa? Yana fitowa ne don yă kalubalanci Isra’ila. Sarki zai sāka wa mutumin da ya kashe wannan da dukiya mai yawa. Zai kuma ba shi’yarsa yă aura, yă cire suna mahaifinsa daga biyan kuɗin haraji cikin Isra’ila.”
26 And David said to the men that stood by him, thus, What shall be done to the man that may smite yon Philistine, and take away the reproach from Israel? for who is this uncircumcised Philistine, that he should defy the arrays of the living God?
Dawuda ya tambayi mutanen da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Me za a yi wa wanda ya kashe Bafilistin nan, ya kuma cire wannan kunya daga Isra’ila? Wane ne wannan bafilistin marar kaciya da yake kalubalantar rundunar yaƙi na Allah mai rai?”
27 And the people spoke to him after this manner, saying, So shall it be done to the man that may smite him.
Sai suka sāke gaya masa abin da suka faɗa cewa, “Ga abin da zai faru da wanda ya kashe shi.”
28 And Eliab his eldest brother heard when he was speaking unto the men; and Eliab's anger was kindled against David, and he said, Why didst thou come down hither? and with whom hast thou left those few sheep in the wilderness? I know thy presumption, and the wickedness of thy heart; for in order to see the battle art thou come down.
Da wansa Eliyab, ya ji yana magana da mutanen, sai ransa ya ɓace ƙwarai saboda fushi, sai ya ce wa Dawuda, “Me ka zo yi a nan? Wa kuma ka bar wa’yan tumakin a jeji? Na san ka da taurinkai, da kuma mugun hali. Ka zo nan ne don ka yi kallon yaƙi kawai.”
29 And David said, What have I now done? It is nothing but a word.
Dawuda ya ce, “To, yanzu me na yi? Ba zan ma yi magana ba?”
30 And he turned from him toward another, and spoke after the same manner: and the people made him again a reply after the former manner.
Sai ya juya wajen wani kuma ya sāke kawo zancen, mutanen kuwa suka amsa masa kamar dā.
31 And the words which David had spoken were heard, and they told them in the presence of Saul, who sent for him.
Aka ji abin da Dawuda ya ce, aka kuwa gaya wa Shawulu, Shawulu kuma ya aika a kawo shi.
32 And David said to Saul, Let no man's heart fail because of him: thy servant will go and fight with this Philistine.
Da Shawulu ya tambayi Dawuda, sai Dawuda ya ce masa, “Kada kowa yă damu saboda wannan Bafilistin. Bawanka zai je yă yi faɗa da shi.”
33 And Saul said to David, Thou art not able to go unto this Philistine to fight with him; for thou art but a lad, and he [hath been] a man of war from his youth.
Shawulu ya ce, “Ba za ka iya yin faɗa da wannan Bafilistin ba, ya daɗe yana yaƙi, ya yi yaƙi tun yana saurayi. Ga shi kuwa kai ɗan yaro ne kawai.”
34 And David said unto Saul, Thy servant was feeding his father's flocks, and there came a lion, and a bear, and bore off a lamb out of the drove;
Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Bawanka yana kiwon tumakin mahaifinsa. Sa’ad da zaki ko beyar ta zo ta kama tunkiya, ta tafi da ita.
35 And I went out after him, and smote him, and delivered it out of his mouth: and when he rose up against me, I caught him by his beard, and smote him, and slew him.
Nakan bi ta a baya in buga ta in kuma ƙwato tunkiyar daga bakinta. In kuma ta taso mini, nakan cafke ta a gashinta in buga ta in kashe.
36 Both the lion and the bear did thy servant smite: and this uncircumcised Philistine shall become as one of them; because he hath defied the arrays of the living God.
Bawanka ya kashe zaki da beyar, wannan Bafilistin marar kaciya zai zama kamar ɗaya daga cikinsu, domin ya rena rundunar Allah mai rai.
37 Moreover David said, The Lord who hath delivered me out of the power of the lion, and out of the power of the bear, will also surely deliver me out of the hand of this Philistine. And Saul said unto David, Go, and may the Lord be with thee.
Ubangiji wanda ya cece ni daga kumbar zaki da kuma kumbar beyar, zai cece ni daga hannun wannan Bafilistin.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Je ka, Ubangiji yă kasance tare da kai.”
38 And Saul clothed David with his garments, and he put a helmet of copper upon his head; and he clothed him also with a coat of mail.
Sai Shawulu ya kawo kayan yaƙinsa ya sa wa Dawuda. Ya sa masa hular kwanon da aka yi da tagulla a kansa, ya kuma sa masa rigar ƙarfensa.
39 And David girded his sword over his garments, and he essayed to go; for he had not tried it. And David said unto Saul, I cannot walk in these [things]; for I have never tried it before. And David put them off from him.
Dawuda ya ɗaura māshin Shawulu a sulken, ya yi ƙoƙari yă zaga, sai ya ji ba zai iya ba saboda bai saba ba. Ya cewa Shawulu, “Ba zan iya tafiya da waɗannan ba, domin ban saba ba.” Don haka ya tuɓe su.
40 And he took his staff in his hand, and chose himself five smooth stones out of the brook, and put them in the shepherd's pouch which be had, even in a scrip, with his sling in his hand; and he approached to the Philistine.
Sai ya ɗauki sandansa, ya zaɓi duwatsu guda biyar masu sulɓi daga cikin rafi, ya sa su a’yar jakarsa ta makiyaya; ya kuma ɗauki majajjawarsa, ya tafi, yă fuskanci Bafilistin.
41 And the Philistine went and drew nearer and nearer unto David; and the man that bore the shield went before him.
Ana ciki haka, sai Bafilistin nan shi ma ya fita yana gusowa zuwa wurin Dawuda. Mai riƙe masa garkuwar yaƙi kuwa yana tafe a gabansa.
42 And when the Philistine looked about, and saw David, he disdained him; for he was but a lad, and ruddy, with a fair appearance.
Bafilistin ya dubi Dawuda daga sama har ƙasa, ya gan dai ɗan yaro ne kawai, kyakkyawa kuma mai ƙoshin lafiya, sai ya rena shi.
43 And the Philistine said unto David, Am I a dog, that thou comest unto me with sticks? And the Philistine cursed David by his gods.
Ya ce masa, “Kana tsammani ni kare ne da za ka zo mini da sanda?” Sai ya la’anci Dawuda da sunayen allolin Filistiyawa.
44 And the Philistine said to David, Come to me, and I will give thy flesh unto the fowls of the heavens, and to the beasts of the field.
Ya ce, “Zo nan, ni kuwa zan ba da naman jikinka ga tsuntsayen sama da namun jeji su ci.”
45 Then said David to the Philistine, Thou comest unto me with a sword, and with a spear, and with a javelin; but I come to thee in the name of the Lord of hosts, the God of the arrays of Israel, that thou hast defied.
Dawuda ya ce wa Bafilistin, “Kana zuwa ka yaƙe ni da māshi da takobi da kere, amma ni ina zuwa in yaƙe ka a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki, Allah na rundunar Isra’ila, wanda ka rena.
46 This day will the Lord deliver thee into my hand; and I will smite thee, and remove thy head from thee; and I will give the carcasses of the army of the Philistines this day unto the fowls of the air, and to the wild beasts of the earth; and all the earth shall know that there is a God for Israel.
Yau nan, Ubangiji zai bashe ka a hannuna, zan kuwa kashe ka, in datse kanka. Yau, zan ba da gawawwakin rundunar Filistiyawa ga tsuntsayen sama da namun jeji, da haka duniya za tă sani lalle akwai Allah a cikin Isra’ila.
47 And all this assembly shall know that the Lord saveth not through sword and spear; for the battle is the Lord's, and he will give you up into our hand.
Duk waɗanda suka taru a nan za su san cewa ba da māshi ko takobi ne Ubangiji yake ceto ba, gama yaƙin nan na Ubangiji ne, shi kuwa zai bashe ku duka a hannuwanmu.”
48 And it came to pass, when the Philistine arose, and went and drew nigh to meet David, that David hastened, and ran toward the battle-array to meet the Philistine.
Yayinda Bafilistin yana matsowa kusa domin yă fāɗa wa Dawuda, sai Dawuda ya ruga a guje zuwa bakin dāgā don yă same shi.
49 And David put his hand into the pouch, and took thence a stone, and slung it, and he struck the Philistine on his forehead, and the stone sunk into his forehead: and he fell upon his face to the ground.
Ya sa hannu a jakarsa ya ɗauki dutse, ya sa cikin majajjawa ya wurga, dutsen kuwa ya bugi Bafilistin a goshi, dutsen ya shiga cikin goshinsa, sai Bafilistin ya fāɗi rubda ciki.
50 So David prevailed over the Philistine with the sling and with the stone, and smote the Philistine, and slew him; but there was no sword in the hand of David.
Da majajjawa da dutse kawai Dawuda ya ci nasara a kan Bafilistin. Ya buge shi, ya kashe shi ba tare da takobi a hannunsa ba.
51 And David ran, and stood by the Philistine, and took his sword, and drew it out of its sheath, and slew him, and cut off his head therewith. And when the Philistines saw that their hero was dead, they fled.
Dawuda ya ruga ya tsaya a bisan Bafilistin, ya zare takobin Bafilistin daga kubensa, ya datse masa kai da shi. Da Filistiyawa suka ga jaruminsu ya mutu, sai suka juya suka gudu.
52 And then arose the men of Israel and of Judah, and shouted, and pursued the Philistines, until thou comest to the valley, and to the gates of 'Ekron. And the slain of the Philistines fell down by the way to Sha'arayim, even as far as Gath, and up to 'Ekron.
Mutanen Isra’ila da na Yahuda suka rugo gaba da babbar murya, suka fafari Filistiyawa har zuwa mashigin Gat da kuma ƙofofin Ekron. Gawawwakin Filistiyawa suka bazu a hanyar Sha’arayim zuwa Gat da kuma Ekron.
53 And the children of Israel returned from hotly pursuing after the Philistines, and they spoiled their camps.
Da Isra’ilawa suka komo daga bin Filistiyawa sai suka washe sansanin Filistiyawa.
54 And David took the head of the Philistine, and brought it to Jerusalem; but his weapons he placed in his tent.
Dawuda ya ɗauki kan Bafilistin zuwa Urushalima. Sai Dawuda ya ajiye kayan yaƙin Bafilistin a tentinsa.
55 And when Saul saw David going forth against the Philistine, he said unto Abner, the captain of the army, Abner, whose son is this lad? And Abner said, As thy soul liveth, O king, I know it not.
Yayinda Shawulu yake kallon Dawuda sa’ad da za shi yă yaƙi Bafilistin, sai ya tambayi Abner, komandan rundunarsa ya ce, “Abner, ɗan wane ne wannan saurayi?” Abner ya ce ran sarki yă daɗe, “Ban sani ba.”
56 And the king said, Ask thou whose son this youth is.
Sarki ya ce, “Ka tambaya mini ko yaron wane ne wannan saurayi.”
57 And as David returned from smiting the Philistine, Abner took him, and brought him before Saul with the head of the Philistine in his hand.
Dawuda yana dawowa daga karkashe Filistiyawa ke nan, sai Abner ya kai shi gaban Shawulu, riƙe da kan Bafilistin.
58 And Saul said to him, Whose son art thou, young man? And David answered, The son of thy servant Jesse the Beth-lechemite.
Sai Shawulu ya ce, “Kai ɗan wane ne, saurayi?” Dawuda ya ce, “Ni ɗan bawanka Yesse ne, na Betlehem.”

< 1 Samuel 17 >