< 1 Kings 1 >

1 Now king David was old, stricken in years; and they covered him with clothes, but he could not become warm.
Sa’ad da Sarki Dawuda ya tsufa ya kuma ƙara shekaru, ba ya iya jin ɗumi ko an rufe shi da abin rufuwa.
2 Wherefore his servants said unto him, Let them seek out for my lord the king a young virgin, and let her stand before the king, and let her be an attendant on him; and let her lie in thy bosom, that my lord the king may become warm.
Saboda haka bayinsa suka ce masa, “Bari mu nemi wata budurwa wadda za tă yi wa ranka yă daɗe, sarki hidima, tă kuma kula da shi. Za tă dinga kwanta kusa da ranka yă daɗe, yă ji ɗumi.”
3 So they sought for a fair maiden throughout all the territory of Israel; and they found Abishag the Shunammite, and brought her to the king.
Suka nemi kyakkyawar yarinya cikin fāɗin Isra’ila, sai suka sami Abishag, mutuniyar Shunam, suka kawo ta wa sarki.
4 And the maiden was exceedingly fair; and she became an attendant on the king, and ministered to him; but the king knew her not.
Yarinyar kuwa kyakkyawa ce ƙwarai; ta kuwa lura da sarki, ta kuma yi masa hidima, amma sarki bai yi jima’i da ita ba.
5 And Adoniyah the son of Chaggith exalted himself, saying, I shall be king: and he procured himself a chariot and horsemen, and fifty men who ran before him.
Adoniya, wanda mahaifiyarsa ce Haggit, ya fito ya ce, “Zan zama sarki.” Saboda haka ya nemi kekunan yaƙi, ya kuma shirya dawakai, tare da mutane hamsin da za su sha gabansa.
6 And his father had never grieved him in all his life by saying, Why hast thou done so? and he also was of a very goodly form; and his mother had born him after Abshalom.
(A duk rayuwarsa mahaifinsa bai taɓa tsawata masa yă ce, “Me ya sa kake yin haka ba?” Shi kuwa mai kyan gani ne ƙwarai, shi ne aka haifa bayan Absalom.)
7 And he had conferences with Joab the son of Zeruyah, and with Ebyathar the priest: and they, following Adoniyah, helped him.
Adoniya ya haɗa baƙi da Yowab ɗan Zeruhiya da kuma Abiyatar firist, suka kuma ba shi goyon baya.
8 But Zadok the priest, and Benayahu the son of Yehoyada', and Nathan the prophet, and Shim'i, and Re'i, and the mighty men that belonged to David, were not with Adoniyah.
Amma Zadok firist, Benahiya ɗan Yehohiyada, annabi Natan, Shimeyi, Reyi da kuma matsara na musamman na Dawuda ba su bi Adoniya ba.
9 And Adoniyah slaughtered sheep and oxen and fatted cattle by the stone Zocheleth, which is by 'En-rogel; and he invited all his brothers the king's sons, and all the men of Judah the king's servants;
Wata rana Adoniya ya tafi Dutsen Zohelet kusa da En Rogel, inda ya yi hadayar tumaki, da shanun noma, da shanun da ake kiwo a gida. Ya kuma gayyaci’yan’uwansa, wato, sauran’ya’yan Sarki Dawuda, tare da dukan dattawan sarki da suka fito daga Yahuda,
10 But Nathan the prophet, and Benayahu, and the mighty men, and Solomon his brother, he invited not.
amma bai gayyaci annabi Natan, ko Benahiya, ko wani daga matsara na musamman, ko kuwa ɗan’uwansa Solomon ba.
11 And Nathan spoke unto Bath-sheba' the mother of Solomon, saying, Hast thou not heard that Adoniyah the son of Chaggith is become king, and [that] David our lord knoweth it not?
Sai Natan ya ce wa Batsheba, mahaifiyar Solomon, “Ki san cewa Adoniya, ɗan Haggit, ya zama sarki ba tare da sanin ranka yă daɗe, sarkinmu Dawuda ba?
12 And now come, let me, I pray thee, give thee counsel, that thou mayest save thy own life, and the life of thy son Solomon.
Yanzu bari in ba ki shawara yadda za ki cece ranki da kuma ran ɗanki Solomon.
13 Go and get thee in unto king David, and say unto him, Didst not thou, my lord, O king, swear unto thy hand-maid, saying, Assuredly, Solomon thy son shall reign after me, and only he shall sit upon my throne? why then is Adoniyah become king?
Ki shiga wurin Sarki Dawuda ki ce masa, ‘Ranka yă daɗe sarki, ba ka rantse mini ni baiwarka cewa, “Tabbatacce Solomon ɗanka ne zai zama sarki bayana, yă kuma zauna a kujerar sarautar ba”? To, me ya sa Adoniya ya zama sarki?’
14 And, lo, while thou shalt be yet speaking there with the king, I myself will come in after thee, and confirm thy words.
Yayinda kike can kina magana da sarki, zan shiga in kuma tabbatar da abin da kika faɗa.”
15 And Bath-sheba' went in unto the king into the chamber, and the king was very old; and Abishag the Shunammite was ministering unto the king.
Saboda haka Batsheba ta je don tă ga sarki. A yanzu dai sarki ya tsufa, yana nan kuma a cikin ɗakinsa, inda Abishag mutuniya Shunam take masa hidima.
16 And Bath-sheba' bowed, and prostrated herself unto the king: and the king said, What wouldst thou?
Batsheba ta rusuna ta kuma durƙusa a gaban sarki. Sai sarki ya tambaye ta ya ce, “Me kike so?”
17 And she said unto him, My lord, thou thyself didst swear by the Lord thy God unto thy hand-maid, Assuredly, Solomon thy son shall reign after me, and only he shall sit upon my throne.
Ta ce masa, “Ranka yă daɗe, kai kanka ka rantse mini ni baiwarka da sunan Ubangiji Allahnka cewa, ‘Solomon ɗanka zai zama sarki bayana, zai kuma zauna a kujerar sarautata.’
18 And now, behold, Adoniyah is become king; and now, my lord, O king, thou knowest it not:
Amma yanzu Adoniya ya zama sarki, kai kuwa ranka yă daɗe sarki, ba ka san wani abu game da shi ba.
19 And he hath slaughtered oxen and fatted cattle and sheep in abundance, and hath invited all the sons of the king, and Ebyathar the priest, and Joab the captain of the army; but Solomon thy servant hath he not invited.
Ya miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa, ya kuma gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da Abiyatar firist, da Yowab shugaban mayaƙa, amma bai gayyaci Solomon bawanka ba.
20 And as for thee, my lord, O king, the eyes of all Israel are upon thee, to tell them, who shall sit on the throne of my lord the king after him.
Ranka yă daɗe sarki, idanun dukan Isra’ila suna a kanka, domin su san wa zai zauna a kujerar ranka yă daɗe sarkina, a bayanka.
21 Otherwise it would come to pass, when my lord the king sleepeth with his fathers, that I and my son Solomon may be counted offenders.
In ba haka, bayan an binne ranka yă daɗe sarki, tare da kakanninsa, za a wulaƙance ni da Solomon ɗana, kamar masu laifi.”
22 And, lo, while she was yet speaking with the king, Nathan the prophet also came in.
Yayinda take cikin magana tare da sarki, sai annabi Natan ya iso.
23 And they told the king, saying, Behold, here is Nathan the prophet: and when he was come in before the king, he prostrated himself before the king with his face to the ground.
Sai aka faɗa wa sarki, “Ga annabi Natan.” Da Natan ya je gaban sarki, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
24 And Nathan said, My lord, O king, hast thou then said, Adoniyah shall reign after me, and he shall sit upon my throne?
Natan ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki, ko ka furta cewa Adoniya ne zai zama sarki a bayanka, yă kuma zauna a kujerar sarautarka?
25 For he is gone down this day, and hath slaughtered oxen and fatted cattle and sheep in abundance, and hath invited all the king's sons, and the captains of the army, and Ebyathar the priest: and, behold, they are eating and drinking before him, and they say, Long live king Adoniyah.
Yau ya gangara, ya kuma miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa. Ya gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da shugaban mayaƙa, da kuma Abiyatar firist. A yanzu haka suna ci, suna sha, tare da shi, suna cewa, ‘Ran Sarki Adoniya yă daɗe!’
26 But as for me, me thy servant, and Zadok the priest, and Benayahu the son of Yehoyada', and thy servant Solomon, hath he not invited.
Amma bai gayyace ni bawanka, da Zadok firist, da Benahiya ɗan Yehohiyada, da kuma bawanka Solomon ba.
27 Can it be that this hath been done by order of my lord the king, and thou hast not informed thy servant, who should sit on the throne of my lord the king after him?
Ranka yă daɗe, sarki, ko ka tabbatar da haka, amma ba ka ko faɗa wa fadawanka, cewa ga wanda zai gāje Ranka yă daɗe, sarki ba?”
28 Then answered king David, and said, Call me Bath-sheba'; and she came into the king's presence, and stood before the king.
Sai Dawuda ya ce, “Kira Batsheba tă shiga.” Sai ta zo gaban sarki ta kuma tsaya a gabansa.
29 And the king swore and said, As the Lord liveth, that hath redeemed my soul out of all distress,
Sai sarki ya yi rantsuwa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya cece ni daga kowace damuwa,
30 Even as I have sworn unto thee by the Lord the God of Israel, saying, Assuredly Solomon thy son shall reign after me, and only he shall sit upon my throne in my stead: even so will I certainly do this day.
tabbatacce a yau zan aikata abin da na yi miki rantsuwa da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila; Solomon ɗanki zai zama sarki bayana, kuma shi zai zauna a kan kujerar sarautata a maimakona.”
31 Then did Bath-sheba' bow herself with her face to the earth, and prostrate herself unto the king; and she said, May my lord, the king David, live for ever!
Sai Batsheba ta rusuna da fuskarta har ƙasa, ta kuma durƙusa a gaban sarki ta ce, “Bari ran Sarkina Dawuda yă daɗe, har abada!”
32 And king David said, Call unto me Zadok the priest, and Nathan the prophet, and Benayahu the son of Yehoyada'. And they came before the king.
Sarki Dawuda ya ce, “Ku kira mini Zadok firist, annabi Natan, da Benahiya ɗan Yehohiyada.” Da suka zo gaban sarki,
33 And the king said unto them, Take with you the servants of your lord, and cause Solomon my son to ride upon my own mule, and conduct him down to Gichon:
sai ya ce musu, “Ku ɗauki bayin sarki tare da ku, ku kuma sa ɗana Solomon a kan dokina, ku gangara da shi zuwa Gihon.
34 And let Zadok the priest with Nathan the prophet anoint him there as king over Israel; and blow ye with the cornet, and say, Long live king Solomon.
A can ku sa Zadok firist, da annabi Natan su shafe shi sarki a bisa Isra’ila. Ku busa ƙaho, ku kuma yi ihu, kuna cewa, ‘Ran Sarki Solomon yă daɗe!’
35 Then shall ye go up after him, and he shall come and sit upon my throne; and he shall be king in my stead: and him have I ordained to be ruler over Israel and over Judah.
Sa’an nan ku haura tare da shi, zai kuwa zo yă zauna a kujera sarautata, yă yi mulki a maimakona. Na naɗa shi mai mulki a bisa Isra’ila da Yahuda.”
36 And Benayahu the son of Yehoyada' answered the king, and said, Amen: May thus say the Eternal the God of my lord the king.
Benahiya ɗan Yehohiyada ya amsa wa sarki, ya ce, “Amin! Bari Ubangiji Allah na ranka yă daɗe sarkina, yă tabbatar da haka.
37 As the Eternal hath been with my lord the king, even so may he be with Solomon, and may he make his throne greater than the throne of my lord the king David.
Kamar yadda Ubangiji ya kasance da ranka yă daɗe, sarki, haka ma bari yă kasance da Solomon, yă kuma mai da kujerar sarautarsa tă fi kujerar sarautar ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, girma!”
38 Thereupon Zadok the priest, and Nathan the prophet, and Benayahu the son of Yehoyada', and the Kerethites, and the Pelethites, went down, and caused Solomon to ride upon king David's mule, and conducted him to Gichon.
Sai Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa suka gangara, suka sa Solomon a kan dokin Sarki Dawuda, suka raka shi zuwa Gihon.
39 And Zadok the priest took the horn of oil out of the tabernacle, and anointed Solomon. And they blew with the cornet; and all the people said, Long live king Solomon.
Zadok firist ya ɗauki ƙahon mai daga tenti mai tsarki, ya shafe Solomon. Sa’an nan suka busa ƙaho, sai dukan mutane suka yi ihu, suna cewa “Ran Sarki Solomon yă daɗe!”
40 And all the people went up after him, and the people blew on flutes, and rejoiced with great joy, so that the earth was rent at their noise.
Dukan mutane kuwa suka haura suka bi shi, suna busan sarewa, suna farin ciki sosai, har ƙasa ta girgiza saboda sowa.
41 And Adoniyah and all the guests that were with him heard it as they had just finished eating: and when Joab heard the sound of the cornet, he said, Wherefore is this noise of the city in an uproar?
Adoniya tare da dukan baƙin da suke tare da shi kuwa suka ji wannan sa’ad da suke gama bikinsu. Da jin busan ƙaho, sai Yowab ya yi tambaya, ya ce, “Me ya jawo surutu haka a birni?”
42 And while he was yet speaking, behold, Jonathan the son of Ebyathar the priest came in: and Adoniyah said [unto him], Come in; for thou art a worthy man, and must bring good tidings.
Tun yana cikin magana, sai Yonatan ɗan Abiyatar ya iso. Adoniya ya ce, “Shigo! Ai, mutumin kirki irinka, lalle ka kawo labari mai daɗi ne.”
43 And Jonathan answered and said to Adoniyah, Alas, no; our lord king David hath made Solomon king;
Yonatan ya ce wa Adoniya, “A ina! Ranka yă daɗe, Sarkinmu Dawuda ya naɗa Solomon sarki.
44 And the king hath sent with him Zadok the priest, and Nathan the prophet, and Benayahu the son of Yehoyada', and the Kerethites, and the Pelethites, and they have caused him to ride upon the king's mule;
Sarki ya aika shi tare da Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa, suka sa shi a kan dokin sarki,
45 And Zadok the priest and Nathan the prophet have anointed him as king on the Gichon; and they are come up from there rejoicing, and the city hath been set in commotion. This is the noise that ye have heard.
Zadok firist kuwa da annabi Natan sun shafe shi sarki a Gihon. Daga can suka haura suna kirari, birni kuwa ta ɓarke da sowa. Surutun da kake ji ke nan.
46 And Solomon hath also sat on the kingly throne.
Ban da haka ma, Solomon ne sarki yanzu.
47 And also the king's servants are come to bless our lord king David, saying, May God make the name of Solomon more famous than thy name, and make his throne greater than thy throne: and the king hath bowed himself upon the bed.
Yanzu haka, fadawa sun zo suna wa ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, sam barka, suna cewa, ‘Bari Allahnka yă sa sunan Solomon yă zama sananne fiye da naka, bari kuma sarautarsa tă fi taka girma!’ Sarki kuwa ya rusuna, ya yi sujada a kan gadonsa
48 And also thus hath the king said, Blessed be the Lord the God of Israel, who hath given [me] this day one who sitteth on my throne, while my eyes see it.
ya ce, ‘Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bar idanuna suka ga magāji a kan kujerar sarautata a yau.’”
49 And all the guests that were with Adoniyah were terrified, and rose up, and went, every man, on his own way.
A nan fa, dukan baƙin Adoniya suka taso da rawar jiki suka watse.
50 And Adoniyah was afraid because of Solomon; and he arose, and went, and caught hold on the horns of the altar.
Amma Adoniya, don tsoron Solomon, ya je ya kama ƙahon bagade ya riƙe.
51 And it was told unto Solomon, saying, Behold, Adoniyah feareth king Solomon; and, behold, he hath caught hold on the horns of the altar, saying, Let king Solomon swear unto me today that he will not slay his servant with the sword.
Sa’ad da aka faɗa wa Solomon cewa, “Adoniya yana tsoron Sarki Solomon, kuma ya manne wa ƙahonin bagade. Yana cewa, ‘Bari Sarki Solomon yă rantse mini a yau cewa ba zai kashe bawansa da takobi ba.’”
52 And Solomon said, If he will become a worthy man, there shall not a hair of his fall to the earth; but if any wrong shall be found on him, then shall he die.
Solomon ya amsa ya ce, “In ya nuna kansa mai biyayya, ba gashin kansa da zai fāɗi ƙasa; amma in aka same mugunta a cikinsa, zai mutu.”
53 So king Solomon sent, and they brought him down from the altar; and he came and bowed himself to king Solomon; and Solomon said unto him, Go to thy house.
Sai Sarki Solomon ya aiki mutane, suka kuma sauko da shi daga bagade. Adoniya kuwa ya zo, ya rusuna wa Sarki Solomon, sai Solomon ya ce, “Tafi gidanka.”

< 1 Kings 1 >