< 1 Chronicles 29 >

1 And king David said unto all the assembly, Solomon, the only son of mine whom God hath made choice of, is yet young and tender, and the work is great; because not for man is the palace to be, but for the Lord God.
Sa’an nan Sarki Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ɗana Solomon, wanda Allah ya zaɓa, matashi ne, kuma bai gogu ba. Aikin yana da yawa, domin wannan ƙasaitaccen ginin ba na mutum ba ne, na Ubangiji Allah ne.
2 But with all my might have I made ready for the house of my God, the gold for the things of gold, and the silver for the things of silver, and the copper for the things of copper, the iron for the things of iron, and the wood for the things of wood, onyx stones, and stones to be set, bright stones, and stones of divers colors, and all manner of precious stones, and marble stones in abundance.
Na riga na tara dukan kayayyakin da na tanada saboda haikalin Allahna, zinariya saboda dukan ayyukan zinariya, azurfa saboda ayyukan azurfa, tagulla saboda ayyukan tagulla, ƙarfe saboda ayyukan ƙarfe da kuma katako saboda ayyukan katako, da onis don ado, turkuwoyis, duwatsu masu launi dabam-dabam, da kuma dukan duwatsu masu kyau da mabul, dukan waɗannan suna nan jingim.
3 Moreover, because I have set my affection on the house of my God, have I acquired as my own property gold and silver; [and this] have I given to the house of my God, over and above all that I have prepared for the holy house:
Ban da haka ma, cikin sa zuciyata ga haikalin Allahna, yanzu na ba da ma’ajina na zinariya da azurfa saboda haikalin Allahna, fiye da kome na tanada saboda wannan haikali,
4 Three thousand talents of gold, of the gold of Ophir, and seven thousand talents of refined silver, to overlay the walls of the houses;
talenti dubu uku na zinariya (zinariyar Ofir) da tacecciyar azurfa dubu bakwai; don adon bangon gine-ginen,
5 All that is needed of gold and of silver, and for every manner of work [to be made] by the hands of artificers. And who [now] is willing to consecrate his hand this day unto the Lord?
don aikin zinariya da kuma aikin azurfa, don kuma dukan aikin da gwanaye za su yi. Yanzu fa wa yake da niyya yă miƙa kansa a yau don Ubangiji?”
6 Thereupon offered voluntarily the chiefs of the family divisions and the princes of the tribes of Israel, and the captains of the thousands and of the hundreds, with the supervisors of the king's work;
Sai shugabannin iyalai, shugabannin kabilan Isra’ila, manyan hafsoshin mayaƙa dubu-dubu da manyan hafsoshi mayaƙa ɗari-ɗari, da shugabannin lura da ayyukan sarki suka yi bayarwa da yardar rai.
7 And they gave for the service of the house of God of gold five thousand talents and ten thousand drachms, and of silver ten thousand talents, and of copper eighteen thousand talents, and of iron one hundred thousand talents.
Suka bayar talenti dubu biyar na zinariya, talenti dubu goma na azurfa, talenti dubu goma sha takwas na tagulla da talenti dubu ɗari na ƙarfe don aiki a haikalin Allah.
8 And those with whom stones were found gave them to the treasury of the house of the Lord, under the supervision of Jechiel the Gershunite.
Duk waɗanda suke da duwatsu masu daraja suka ba da su ga Yehiyel mutumin Gershon ma’ajin haikalin Ubangiji.
9 Then did the people rejoice, because they had voluntarily offered: for with an undivided heart did they offer to the Lord: and also king David rejoiced with great joy.
Mutane suka yi farin ciki ganin yadda shugabanninsu suke bayarwa da yardar rai, gama sun bayar hannu sake da kuma dukan zuciya ga Ubangiji. Dawuda sarki shi ma ya yi farin ciki ƙwarai.
10 And David blessed the Lord before the eyes of all the congregation; and David said, Blessed be thou, O Lord the God of Israel our father, from everlasting even unto everlasting.
Dawuda ya yabi Ubangiji a gaban dukan taron, yana cewa, “Yabo gare ka, ya Ubangiji, Allah na mahaifinmu Isra’ila, har abada abadin.
11 Thine, O Lord, are the greatness, and the might, and the glory, and the victory, and the majesty, yea, all that is in the heavens and on the earth: thine, O Lord, is the kingdom, and thou art exalted as the head above all.
Girma da iko da ɗaukaka, da daraja da kuma nasara naka ne, ya Ubangiji, gama kome a sama da ƙasa naka ne. Mulki kuma naka ne, ya Ubangiji; an kuma ɗaukaka ka a matsayin kai a bisa duka.
12 And riches and honor come from thee, and thou rulest over all; and in thy hand are power and might; and it is in thy hand to make great, and to give strength unto all.
Wadata da girma daga gare ka suke; kai ne mai mulkin dukan abubuwa. A hannuwanka ne ƙarfi da iko suke don ka ɗaukaka da kuma ba da ƙarfi ga duka.
13 And now, O our God, we give thanks unto thee, and praise thy glorious name.
Yanzu fa, Allahnmu, muna gode maka, muna kuma yabon ɗaukakar sunanka.
14 For who am I, and what is my people, that we should possess the power to offer voluntarily after this sort? for from thee is every thing, and out of thy own have we given unto thee.
“Amma wane ni, kuma wace ce jama’ata da za mu iya ba ka a yalwace kamar haka? Kome daga gare ka suka fito, kuma mun ba ka abin da kawai ya fito daga hannunka ne.
15 For strangers are we before thee, and sojourners, as were all our fathers: like a shadow are our days on the earth, and there is no hope [of abiding].
Mu bare ne kuma baƙi a gabanka, kamar yadda dukan kakanninmu suke. Kwanakinmu a duniya suna kamar inuwa ne, ba sa zuciya.
16 O Lord our God! all this abundant store which we have prepared to build for thee a house for thy holy name, is out of thy own hand, and thine is all.
Ya Ubangiji Allahnmu, game da dukan wannan yalwar da ka tanada saboda ginin haikali saboda Sunanka Mai Tsarki, sun fito daga hannunka ne, kuma dukan naka ne.
17 And I know, my God, that thou probest the heart, and uprightness thou receivest in favor. As for me, in the uprightness of my heart have I voluntarily offered all these things; and now thy people, that are present here, do I see with joy offering voluntarily unto thee.
Na sani, Allahna, cewa kakan gwada zuciya, kakan kuma gamsu da mutunci. Dukan waɗannan abubuwa na bayar da yardar rai da kuma kyakkyawar niyya. Yanzu kuma da farin ciki na ga yadda mutanenka waɗanda suke a nan da yardar rai suka ba ka.
18 O Lord, God of Abraham, Isaac, and of Israel, our father, preserve this for ever as the imagination of the thoughts of the heart of thy people, and direct their heart firmly unto thee.
Ya Ubangiji Allah na kakanninmu Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, ka sa wannan sha’awa a cikin zukatan mutanenka har abada, ka kuma bar zukatansu su yi maka biyayya.
19 And unto Solomon my son do thou give an undivided heart to keep thy commandments, thy testimonies, and thy statutes, and to do all, and to build the palace, for which I have made preparation.
Ka kuma ba ɗana Solomon cikakkiyar zuciya don yă kiyaye umarnanka, farillanka da ƙa’idodinka yă kuma yi kome don yă gina ƙasaitaccen gini wanda na riga na yi tanadi dominsa.”
20 And David said to all the assembly. Bless now the Lord your God. And all the assembly blessed the Lord the God of their fathers, and bent down their heads, and prostrated themselves to the Lord, and to the king.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ku yabi Ubangiji Allahnku.” Saboda haka suka yabi Ubangiji Allah na kakanninsu; suka rusuna suka kuma fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji da kuma sarki.
21 And they sacrificed sacrifices unto the Lord, and they offered burnt-offerings unto the Lord, on the morrow after that day, one thousand bullocks, a thousand rams, a thousand sheep, with their drink-offerings, and [other] sacrifices in abundance for all Israel;
Kashegari suka miƙa hadayu ga Ubangiji suka kuma miƙa hadayu bijimai dubu, raguna dubu da kuma’yan raguna dubu na ƙonawa gare shi, tare da hadayunsu na sha da sauran hadayu a yalwace saboda dukan Isra’ila.
22 And they ate and drank before the Lord on that day with great joy. And they declared the second time Solomon the son of David to be king, and they anointed him unto the Lord as chief ruler, and Zadok as priest.
Suka ci suka sha da farin ciki mai girma a gaban Ubangiji a wannan rana. Sa’an nan suka yarda da Solomon ɗan Dawuda a matsayin sarki sau na biyu, suka shafe shi a gaban Ubangiji don yă zama mai mulki, Zadok kuwa ya zama firist.
23 Then sat Solomon on the throne of the Lord as king instead of David his father, and he was prosperous; and all Israel obeyed him.
Saboda haka Solomon ya zauna a kujerar sarautar Ubangiji a matsayin sarki a maimakon mahaifinsa Dawuda. Ya yi nasara, dukan Isra’ila kuwa suka yi masa biyayya.
24 And all the princes, and the mighty men, and also all the sons of king David, submitted themselves unto king Solomon.
Dukan shugabanni da jarumawa, har ma da dukan’ya’yan Sarki Dawuda maza, suka yi alkawari za su yi wa Sarki Solomon biyayya.
25 And the Lord made Solomon exceedingly great before the eyes of all Israel; and he bestowed upon him a royal majesty such as had not been on any king over Israel before him.
Ubangiji ya ɗaukaka Solomon sosai a idon dukan Isra’ila, ya kuma ba shi darajar sarauta yadda babu sarki a Isra’ilan da ya taɓa samu.
26 Thus did David the son of Jesse reign over all Israel.
Dawuda ɗan Yesse ya zama sarki a bisa dukan Isra’ila.
27 And the time that he reigned over Israel was forty years: in Hebron he reigned seven years, and in Jerusalem he reigned thirty and three [years].
Ya yi mulki a bisa Isra’ila shekaru arba’in, shekaru bakwai a Hebron da kuma shekaru talatin da uku a Urushalima.
28 And he died in a good old age, full of days, riches, and honor: and Solomon his son became king in his stead.
Ya mutu a kyakkyawar tsufa, bayan ya more dogon rai, wadata da girma. Ɗansa Solomon ya gāje shi a matsayin sarki.
29 And the acts of king David, the first and the last, behold, they are written in the history of Samuel the seer, and in the history of Nathan the prophet, and in the history of Gad the seer,
Game da ayyukan mulkin Sarki Dawuda, daga farko har ƙarshe, an rubuta su a cikin tarihin Sama’ila mai duba, tarihin annabi Natan da kuma tarihin Gad mai duba,
30 Together with all his reign and his mighty deeds, and the times that passed over him, and over Israel, and over all the kingdoms of the [various] countries.
tare da yadda mulkinsa da ikonsa da yanayin da suka kewaye shi da Isra’ila da kuma dukan masarautai na dukan sauran ƙasashe.

< 1 Chronicles 29 >