< 1 Chronicles 24 >

1 And the divisions of the sons of Aaron were: The sons of Aaron were Nadab, and Abihu, El'azar, and Ithamar.
Waɗannan su ne sassan’ya’yan Haruna maza.’Ya’yan Haruna maza su ne Nadab, Abihu, Eleyazar da Itamar.
2 But Nadab and Abihu died before their father, and they had no children: and El'azar and Ithamar became priests.
Amma Nadab da Abihu sun mutu kafin mahaifinsu, ba su kuma haifi’ya’ya maza ba; saboda haka Eleyazar da Itamar suka yi hidimar firistoci.
3 And David divided them off with Zadok of the sons of El'azar', and Achimelech of the sons of Ithamar, to their office in their service.
Tare da taimakon Zadok zuriyar Eleyazar da Ahimelek wani zuriyar Itamar. Dawuda ya karkasa su zuwa ɓangarori don aikinsu bisa ga hidima.
4 And the sons of El'azar were found more numerous in the chiefs of males than the sons of Ithamar; and they divided them accordingly. Of the sons of El'azar there were sixteen chiefs of the family divisions, and of the sons of Ithamar, eight for their family divisions.
Akwai ɗumbun shugabanni a cikin zuriyar Eleyazar fiye da zuriyar Itamar, aka kuma karkasa su haka, kawuna goma sha shida daga zuriyar Eleyazar da kuma kawuna iyalai takwas daga zuriyar Itamar.
5 And they divided them off by lot, both the first and the last; for the governors of the sanctuary, and governors [of the house] of God, were from the sons of El'azar, and from the sons of Ithamar.
Aka karkasa su babu sonkai ta wurin jifa ƙuri’a, gama akwai manyan ma’aikatan wuri mai tsarki da manyan ma’aikatan Allah a cikin zuriyar Eleyazar da Itamar.
6 And Shema'yah the son of Nethanel the scribe, one of the Levites, wrote them down before the king, and the princes, and Zadok the priest, and Achimelech the son of Ebyathar, and the chiefs of the families of the priests and Levites: one family division being drawn of El'azar, and one being equally drawn of Ithamar.
Shemahiya ɗan Netanel, wani Balawe ne marubuci, ya rubuta sunayensu a gaban sarki da kuma a gaban manyan ma’aikata. Zadok firist, Ahimelek ɗan Abiyatar da kuma kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa, iyali guda daga Eleyazar, guda kuma daga Itamar.
7 And there came out the first lot for Jehoyarib, for Jeda'yah the second,
Ƙuri’a ta farko ta faɗa a kan Yehoyarib, na biyu a kan Yedahiya,
8 For Charim the third, for Se'orim the fourth,
na uku a kan Harim, na huɗu a kan Seyorim,
9 For Malkiyah the fifth, for Miyamin the sixth.
na biyar a kan Malkiya, na shida a kan Miyamin,
10 For Hakkoz the seventh, for Abiyah the eighth,
na bakwai a kan Hakkoz, na takwas a kan Abiya,
11 For Jeshua' the ninth, for Shechanyahu the tenth,
na tara a kan Yeshuwa, na goma a kan Shekaniya,
12 For Elyashib the eleventh, for Jakim the twelfth,
na goma sha ɗaya a kan Eliyashib, na goma sha biyu a kan Yakim,
13 For Chuppah the thirteenth, for Jeshehah the fourteenth,
na goma sha uku a kan Huffa, na goma sha huɗu a kan Yeshebeyab,
14 For Bilgah the fifteenth, for Immer the sixteenth,
na goma sha biyar a kan Bilga, na goma sha shida a kan Immer,
15 For Chezir the seventeenth, for Happizzez the eighteenth,
na goma sha shida a kan Hezir, na goma sha takwas a kan Haffizzez,
16 For Pethachyah the nineteenth, for Ezekiel the twentieth.
na goma sha tara a kan Fetahahiya, na ashirin a kan Ezekiyel,
17 For Jachin the one and twentieth, for Gamul the two and twentieth,
na ashirin da ɗaya wa Yakin, na ashirin da biyu a kan Gamul,
18 For Delayahu the three and twentieth, for Ma'azyahu the four and twentieth.
na ashirin da uku wa Delahiya da kuma na ashirin da huɗu a kan Ma’aziya.
19 This was their office in their service to come into the house of the Lord, according to the manner prescribed to them, under the supervision of Aaron their father, as the Lord the God of Israel had commanded him.
Ga tsarin aikinsu na hidima sa’ad da suka shiga haikalin Ubangiji, bisa ga ƙa’idar da kakansu Haruna ya kafa, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce shi.
20 And of the rest of the sons of Levi there were, of the sons of 'Amram: Shubael. Of the sons of Shubael: Jechdeyahu.
Game da sauran zuriyar Lawi kuwa, Daga’ya’yan Amram maza. Shubayel; daga’ya’yan Shubayel maza. Yedehiya.
21 Concerning Rechabyahu, of the sons of Rechabyahu the chief was Yishiyah.
Game da Rehabiya kuwa, daga’ya’yansa maza. Isshiya shi ne na fari.
22 Of the Yisharites was Shelomoth: of the sons of Shelomoth was Jachath.
Daga mutanen Izhar, Shelomot; daga’ya’yan Shelomot maza, Yahat.
23 And the sons [of Hebron]: Jeriyah, Amaryahu the second, Jachaziel the third, Jekam'am the fourth.
’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
24 [Of] the sons of 'Uzziel, Michah: of the sons of Michah, Shamir.
Ɗan Uzziyel shi ne, Mika; daga’ya’yan Mika maza, Shamir.
25 The brother of Michah was Yishiyah; of the sons of Yishiyah, Zecharyahu.
Ɗan’uwan Mika shi ne, Isshiya; daga’ya’yan Isshiya maza, Zakariya.
26 The sons of Merari were Machli and Mushi: the sons of Ja'aziyahu, Beno.
’Ya’yan Merari su ne, Mali da Mushi. Ɗan Ya’aziya shi ne, Beno.
27 The sons of Merari by Ja'aziyahu: Beno, and Shoham, and Zaccur, and 'Ibri.
’Ya’yan Merari su ne, daga Ya’aziya, Beno, Shoham, Zakkur da Ibri.
28 Of Machli: El'azar, who had no sons.
Daga Mali, Eleyazar, wanda ba shi da’ya’ya maza.
29 Of Kish: The son of Kish was Jerachmeel.
Daga Kish, ɗan Kish shi ne, Yerameyel.
30 And the sons of Mushi were Machli, and 'Eder, and Jerimoth. These were the sons of the Levites after their family divisions.
Kuma’ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yerimot. Waɗannan su ne Lawiyawa bisa ga iyalansu.
31 These likewise cast lots in the same manner as their brethren the sons of Aaron in the presence of king David, and Zadok, and Achimelech, and the chiefs of the families of the priests and Levites, even the principal of the families equally with his youngest brother.
Suka kuma jifa ƙuri’a, kamar dai yadda’yan’uwansu zuriyar Haruna suka yi, a gaban Sarki Dawuda da gaban Zadok, Ahimelek, da kuma a gaban kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa. Aka yi da iyalan wa daidai da iyalan ƙane.

< 1 Chronicles 24 >