< 1 Chronicles 17 >

1 And it came to pass, when David dwelt in his house, that David said unto Nathan the prophet, Lo, I dwell in a house of cedar, while the ark of the covenant of the Lord is under curtains.
Bayan Dawuda ya zauna a fadansa, sai ya ce wa annabi Natan, “Ga ni, ina zama a fadar da aka yi da al’ul, yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yana a ƙarƙashin tenti.”
2 And Nathan said unto David, All that is in thy heart do; for God is with thee.
Natan ya amsa wa Dawuda ya ce, “Duk abin da kake tunani a zuciya, ka yi, gama Allah yana tare da kai.”
3 And it came to pass during that night, that the word of God came unto Nathan, saying,
A daren nan maganar Allah ta zo wa Natan cewa,
4 Go and say unto David my servant, Thus hath said the Lord, Not thou shalt build for me the house to dwell in;
“Ka tafi ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ba kai ba ne za ka gida mini gidan da zan zauna a ciki.
5 For I have not dwelt in a house since the day that I brought up Israel even until this day; but have been [moving] from tent to tent, and from [one] tabernacle [to another].
Ban taɓa zama a gida daga ranar da na fito da Isra’ila daga Masar ba har wa yau. Na yi ta yawo daga gefen da aka kafa tenti zuwa wani, daga wannan wuri zuwa wancan.
6 In all the places where I moved about among all Israel, did I speak a word to any one of the judges of Israel, whom I had ordained to feed my people, saying, Why have ye not built for me a house of cedar?
Duk inda na tafi tare da Isra’ilawa, na taɓa ce wa wani daga cikin shugabanninsu waɗanda na umarta su yi kiwon mutanena, “Don me ba ku gida mini gidan al’ul ba?”’
7 Now therefore, thus shalt thou say unto my servant, to David, Thus hath said the Lord of hosts, I took thee away from the sheepcote, from behind the flocks, to be a ruler over my people Israel;
“Yanzu, ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, na ɗauke ka daga makiyaya da kuma daga bin garke, don ka zama mai mulki a bisa mutanena Isra’ila.
8 And I have been with thee withersoever thou didst go, and I have cut off all thy enemies from thy presence, and I have made thee a name; like the name of the great men who are on the earth;
Na kasance tare da kai ko’ina ka tafi, na kuma yanke dukan abokan gābanka a gabanka. Yanzu zan sa sunanka kamar sunayen mutane mafi girma na duniya.
9 And I have procured a place for my people Israel, and I have planted them, that they may dwell in a place of their own, and be no more troubled; and that the children of wickedness shall not waste them any more, as aforetimes,
Zan kuma tanada wuri domin mutanena Isra’ila, zan kuma kafa su saboda za su kasance da gidan kansu ba kuwa za a ƙara damunsu ba. Mugayen mutane ba za su ƙara zaluntar su ba, yadda suka yi da farko
10 And [as it was] since the time that I ordained judges to be over my people Israel; and I have humbled all thy enemies; and now I tell thee that the Lord will build for thee a house.
da kuma suka yi tun lokacin da na sa shugabanni a bisa mutanen Isra’ila. Zan rinjaye dukan abokan gābanka. “‘Na furta maka cewa Ubangiji zai gina maka gida,
11 And it shall come to pass, that, when thy days will be completed that thou must go [to sleep] with thy fathers, I will set up thy seed after thee, who shall be of thy sons, and I will establish his kingdom.
sa’ad da kwanakinka suka ƙare ka kuma tafi don ka kasance da kakanninka, zan tā da ɗaya cikin’ya’yanka maza, daga zuriyarka yă gāje ka, zan kuma kafa mulkinka.
12 He it is that shall build for me a house, and I will establish his throne for ever.
Shi ne zai gina gida domina, zan kuma kafa sarautarsa har abada.
13 I too will be to him as a father, and he shall indeed be unto me as a son: and my kindness will I not cause to depart from him, as I caused it to depart from him that was before thee;
Zan zama Ubansa, zai kuma zama ɗana. Ba zan taɓa ɗauke ƙaunata daga gare shi, kamar yadda na ɗauke ta daga wanda ya riga ka ba.
14 But I will place him firmly in my house and in my kingdom for evermore; and his throne shall be established for ever.
Zan sa shi a bisa gidana da mulkina har abada; kujerar sarautarsa za tă kahu har abada.’”
15 In accordance with all these words, and in accordance with all this vision, so did Nathan speak unto David.
Natan ya faɗa wa Dawuda dukan kalmomin wahayin nan.
16 Then went king David in and sat down before the Lord, and he said, Who am I, O Lord God, and what is my house, that thou hast brought me as far as hitherward?
Sai Sarki Dawuda ya shiga ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Wane ne ni, ya Ubangiji Allah, kuma wane ne iyalina, da ka kawo ni har zuwa nan?
17 And this was [yet] too small a thing in thy eyes, O God, and thou hast spoken concerning thy servant's house for a distant time, and hast regarded me as though I belonged to the rank of a man of high degree, O Lord God.
Kuma sai ka ce wannan bai isa ba a idonka, ya Allah, ka yi magana game da nan gaba na gidan bawanka. Ka dube ni sai ka ce ni ne mafi ɗaukaka cikin mutane, ya Ubangiji Allah.
18 What can David add yet more [to speak] unto thee of the honor of thy servant? since thou knowest well thy servant.
“Me kuma Dawuda zai ce maka saboda girmamawar da ka yi wa bawanka? Gama ka san bawanka,
19 O Lord, for the sake of thy servant, and in accordance with thy own heart, hast thou done all this great thing, to make known all these great things.
Ya Ubangiji. Gama saboda bawanka da kuma bisa ga nufinka, ka yi wannan babban abu, ka kuma sanar da dukan manyan alkawura.
20 O Lord, there is none like thee, and there is no god beside thee, in accordance with all that we have heard with our ears.
“Babu wani kamar ka, ya Ubangiji, babu kuma Allah sai kai, kamar yadda muka ji da kunnuwanmu.
21 And who is like thy people Israel, the only nation on the earth which God went to redeem for himself as a people, to acquire for thyself a name for great and terrible deeds, by driving out nations from before thy people, which thou hadst redeemed out of Egypt?
Wane ne kuma yake kamar mutanenka Isra’ila, al’umma guda a duniya wadda Allahnta ya fita don yă fanshi mutane wa kansa, ya kuma yi suna wa kansa, ya kuma aikata manyan abubuwa masu banmamaki masu banrazana ta wurin korin al’ummai daga gaban mutanenka, waɗanda ka fansa daga Masar?
22 And thou hast instituted thy people Israel unto thyself as a people for ever; and thou, Lord, art indeed become their God.
Ka mai da mutanenka Isra’ila na kanka har abada, kuma kai, ya Ubangiji, ka zama Allahnsu.
23 And now, O Lord, let the thing that thou hast spoken concerning thy servant and concerning his house be verified for ever, and do as thou hast spoken.
“Yanzu kuwa, Ubangiji, bari alkawarin da ka yi game da bawanka da gidansa yă kahu har abada. Yi kamar yadda ka yi alkawari,
24 Yea, let it be verified, and let thy name be magnified unto everlasting, that men may say, The Lord of hosts is the God of Israel, even a God for Israel; and may the house of David thy servant be established before thee.
saboda zai kahu kuma sunanka zai zama mai girma har abada. Sa’an nan mutane za su ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki, Allah a bisa Isra’ila, Allahn Isra’ila ne!’ Kuma gidan bawanka Dawuda zai kahu a gabanka.
25 For thou, O my God, hast revealed to the ear of thy servant, that thou wilt build for him a house; therefore hath thy servant found himself able to pray before thee.
“Kai, Allahna, ka bayyana ga bawanka cewa za ka gina gida dominsa. Ta haka bawanka ya sami ƙarfin gwiwa ya yi addu’a gare ka.
26 And now, O Lord, thou art the [true] God, and thou hast spoken concerning thy servant this goodness:
Ya Ubangiji, kai ne Allah! Ka yi alkawari abubuwa masu kyau wa bawanka.
27 And now hast thou been pleased to bless the house of thy servant, that it may continue for ever before thee; for thou, O Lord, hast blessed, and [it will remain] blessed for ever.
Yanzu ka ji daɗi don ka albarkace gidan bawanka, don yă ci gaba har abada a gabanka; gama kai, ya Ubangiji, ka albarkace shi, ya kuma sami albarka ke nan har abada.”

< 1 Chronicles 17 >