< 1 Chronicles 15 >

1 And [David] made himself houses in the city of David, and he prepared a place for the ark of God, and pitched for it a tent.
Bayan Dawuda ya yi gine-gine wa kansa a Birnin Dawuda, sai ya shirya wuri domin akwatin alkawarin Allah, ya kuma kafa tenti dominsa.
2 Then said David, None shall carry the ark of God but the Levites; for of them hath the Lord made choice to carry the ark of God, and to minister unto him for ever.
Sa’an nan Dawuda ya ce, “Babu wani sai ko Lawiyawa kaɗai za su ɗauka akwatin alkawarin Allah, gama Ubangiji ya zaɓe su su ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji su kuma yi hidima a gabansa har abada.”
3 And David assembled all Israel to Jerusalem, to bring up the ark of the Lord unto its place, which he had prepared for it.
Dawuda ya tattara dukan Isra’ila a Urushalima don su haura da akwatin alkawarin Ubangiji zuwa wurin da aka shirya dominsa.
4 And David gathered together the children of Aaron, and the Levites.
Ya tattara zuriyar Haruna a wuri ɗaya da kuma Lawiyawa.
5 Of the sons of Kehath: Uriel the chief, and his brethren one hundred and twenty.
Daga zuriyar Kohat, Uriyel shugaba da dangi 120;
6 Of the sons of Merari: 'Assayah the chief, and his brethren two hundred and twenty.
daga zuriyar Merari Asahiya shugaba da dangi 220;
7 Of the sons of Gershom: Joel the chief, and his brethren one hundred and thirty.
daga zuriyar Gershom, Yowel shugaba da dangi 130;
8 Of the sons of Elizaphan: Shema'yah the chief, and his brethren two hundred.
daga zuriyar Elizafan, Shemahiya shugaba da dangi 200;
9 Of the sons of Hebron: Eliel the chief, and his brethren eighty.
daga zuriyar Hebron, Eliyel shugaba da dangi 80;
10 Of the sons of 'Uzziel: 'Amminadab the chief, and his brethren one hundred and twelve.
daga zuriyar Uzziyel, Amminadab shugaba da dangi 112.
11 And David called for Zadok and Ebyathar the priests, and for the Levites, for Uriel, 'Assayah, and Joel, Shema'yah, and Eliel, and 'Amminadab,
Sa’an nan Dawuda ya kira Zadok da Abiyatar, firistoci, tare da Uriyel, Asahiya, Yowel, Shemahiya, Eliyel da Amminadab, Lawiyawa.
12 And he said unto them, Ye are the chiefs of the family divisions of the Levites: sanctify yourselves, ye and your brethren, and bring up the ark of the Lord the God of Israel unto [the place which] I have prepared for it.
Ya ce musu, “Ku ne kawunan iyalan Lawiyawa; ku da’yan’uwanku Lawiyawa, sai ku tsarkake kanku ku hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila, zuwa wurin da na shirya dominsa.
13 For, because ye [did] it not at the first, the Lord our God made a breach among us; because we had not sought him after the prescribed manner.
Domin ku, Lawiyawa ba ku haura da shi da farko ba ne ya sa Ubangiji Allahnmu ya husata a kanmu. Ba mu tambaye shi game da yadda za mu yi shi a hanyar da aka ƙayyade ba.”
14 So the priests and the Levites sanctified themselves to bring up the ark of the Lord the God of Israel.
Saboda haka firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu don su hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
15 And the children of the Levites bore the ark of God, as Moses had commanded according to the word of the Lord, on their shoulders, by means of barrows placed upon them.
Sai Lawiyawa suka ɗauki akwatin alkawarin Allah da sanduna a kafaɗunsu, kamar yadda Musa ya umarta bisa ga maganar Ubangiji.
16 And David said to the chiefs of the Levites to appoint their brethren the singers with instruments of music, psalteries and harps and cymbals, to sing aloud, by lifting up the voice for joy.
Dawuda ya faɗa wa shugabannin Lawiyawa su sa’yan’uwansu su zama mawaƙa don su rera waƙoƙi masu farin ciki, da kayayyakin bushe-bushe, da kaɗe-kaɗe, molaye, garayu da ganguna.
17 So the Levites appointed Heman the son of Joel, and of his brethren, Assaph the son of Berechyahu, and of the sons of Merari their brethren, Ethan the son of Kushayahu;
Saboda haka Lawiyawa suka zaɓi Heman ɗan Yowel, da Asaf ɗan Berekiya daga cikin’yan’uwansu. Daga iyalin Merari kuma aka zaɓi Etan ɗan Kushahiya.
18 And with them their brethren of the second degree, Zecharyahu, Ben, and Ja'aziel, and Shemiramoth, and Jechiel, and 'Unni, Eliab, and Benayahu, and Ma'asseyahu, and Matthithyahu, and Eliphelehu, and Mikneyahu, and 'Obed-edom, and Je'iel, the gatekeepers.
Tare da su kuma’yan’uwansa da suke biye bisa ga matsayi. Wato, Zakariya, Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ben, Ma’asehiya, Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom da Yehiyel, matsaran ƙofofi.
19 Namely, the singers, Heman, Assaph, and Ethan, to play aloud with cymbals of copper;
Mawaƙan nan Heman, Asaf da Etan, ne za su buga kugen tagulla.
20 And Zechariah, and 'Aziel, and Shemiramoth, and Jechiel, and 'Unni, and Eliab, and Ma'asseyahu, and Benayahu, with psalteries on 'Alamoth;
Zakariya, Aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ma’asehiya da Benahiya, ne za su kaɗa molaye masu murya sama-sama, bisa ga alamot.
21 And Matthithyahu, and Eliphelehu, and Mikneyahu, and 'Obed-edom, and Je-iel, and 'Azazyahu, with harps on the Sheminith to play as leaders.
Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom, Yehiyel da Azaziya, ne za su ja garayu masu murya ƙasa-ƙasa bisa ga sheminit.
22 And Kenanyahu was the chief of the Levites in conducting the singing: he instructed in conducting the singing, because he was skilful.
Kenaniya, shugaban Lawiyawa, shi ne mai bi da waƙoƙi. Wannan hakkinsa ne, gama shi gwani ne a wannan fanni.
23 And Berechyah and Elkanah were gatekeepers for the ark.
Berekiya da Elkana, ne za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
24 And Shebanyahu, and Joshaphat, and Nethanel, and 'Amassai, and Zecharyahu, and Benayahu, and Eli'ezer, the priests, did blow on the trumpets before the ark of God; and 'Obed-edom and Jechiyah were gatekeepers for the ark.
Shebaniya, Yoshafat, Netanel, Amasai, Zakariya, Benahiya da Eliyezer firistoci, su ne za su busa ƙahoni a gaban akwatin alkawarin Allah. Obed-Edom da Yehiya su ma za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
25 And it was David, with the elders of Israel, and the officers over the thousands, who went to bring up the ark of the covenant of the Lord out of the house of 'Obed-edom with joy.
Sai Dawuda da dattawan Isra’ila da shugabannin ƙungiyoyi dubu suka haura don su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga gidan Obed-Edom, da farin ciki.
26 And it came to pass, when God helped the Levites who carried the ark of the covenant of the Lord, that they offered seven bullocks and seven rams.
Domin Allah ya taimaki Lawiyawan da suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, aka miƙa hadayar bijimai bakwai da raguna bakwai.
27 And David was clothed with a robe of fine linen, and [so were] all the Levites that carried the ark, and the singers, and Kenanyahu the chief in conducting the singing of the singers; but David had also upon him an ephod of linen.
To, fa, Dawuda yana saye da kyakkyawar rigar lilin, kamar yadda dukan Lawiyawa waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin suka sa, da kuma yadda mawaƙa, da Kenaniya, wanda yake bi da waƙar mawaƙan ya sa. Dawuda kuma ya sa efod lilin.
28 Thus all Israel brought up the ark of the covenant of the Lord with shouting, and with the sound of the cornet, and with trumpets, and with cymbals, playing aloud on psalteries and harps.
Sai dukan Isra’ila suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji da sowa, da ƙarar ƙahonin raguna da busan ƙahoni, da na ganguna, suna kuma kaɗa molaye da garayu.
29 And it happened, as the ark of the covenant of the Lord came as far as the city of David, that Michal the daughter of Saul looked through the window, and saw king David dancing and playing, and she despised him in her heart.
Yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yake shiga Birnin Dawuda, Mikal’yar Shawulu ta leƙa daga taga. Sa’ad da ta ga Sarki Dawuda yana rawa yana shagali, sai ta rena masa wayo a zuciyarta.

< 1 Chronicles 15 >