< 1 Chronicles 14 >

1 And Churam the king of Tyre sent messengers to David, and trees of cedars, and masons and carpenters, to build him a house.
To, fa, Hiram sarkin Taya ya aika da’yan aika zuwa wurin Dawuda, tare da gumaguman al’ul, maginan duwatsu da kafintoci, don su gina wa Dawuda fada.
2 And David felt conscious that the Lord had established him as king over Israel; for his kingdom was exalted on high, because of his people Israel.
Dawuda kuwa ya san cewa Ubangiji ya kafa shi a matsayin sarki a bisa Isra’ila kuma cewa an ɗaukaka mulkinsa saboda mutanensa Isra’ila.
3 And David took yet more wives at Jerusalem; and David begat more sons and daughters.
A Urushalima, Dawuda ya ƙara auren waɗansu mata, ya kuma zama mahaifin ƙarin’ya’yan maza da mata.
4 And these are the names of the children that he had in Jerusalem: Shammua', and Shobab, Nathan, and Solomon,
Ga sunayen yaran da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
5 And Yibchar, and Elishua', and Elpalet,
Ibhar, Elishuwa, Elfelet,
6 And Nogah, and Nepheg, and Yaphia',
Noga, Nefeg, Yafiya,
7 And Elishama', and Be'elyada', and Eliphalet.
Elishama, Beyeliyada da Elifelet.
8 But when the Philistines heard that David had been anointed as king over all Israel, all the Philistines came up to seek David: and David heard of it, and went out against them.
Sa’ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila, sai suka haura da cikakken mayaƙa don su neme shi, amma Dawuda ya ji game da wannan ya kuwa fita don yă ƙara da su.
9 And the Philistines came and spread themselves out in the valley of Rephaim.
To, fa, Filistiyawa suka zo suka kai wa Kwarin Refayim hari;
10 And David asked counsel of God, saying, Shall I go up against the Philistines? and wilt thou deliver them into my hand? And the Lord said unto him, Go up; and I will deliver them into thy hand.
sai Dawuda ya roƙi Allah ya ce, “In tafi in yaƙi Filistiyawa? Za ka ba da su gare ni?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Ka tafi, zan ba da su gare ka.”
11 And they came up to Ba'al-perazim; and David smote them there. Then David said, God hath broken down my enemies through my hand as a breach [is made] by water: therefore they called the name of that place Ba'al-perazim.
Saboda haka Dawuda da mutanensa suka haura zuwa Ba’al-Ferazim, a can kuwa suka ci Filistiyawa da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa kan raraki ƙasa, haka Allah ya raraki abokan gābana ta wurin hannuna.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
12 And they left behind there their gods, and David gave the order, and they were burnt with fire.
Filistiyawa suka yashe allolinsu, Dawuda kuma ya ba da umarnai a ƙone su a wuta.
13 And the Philistines [came] once again, and spread themselves out in the valley.
Filistiyawa suka sāke kai hari wa kwarin;
14 And David asked again counsel of God; and God said unto him, Thou shalt not go up after them: turn about from them, and come upon them opposite the mulberry-trees,
sai Dawuda ya sāke roƙi Allah, Allah kuwa ya amsa masa, “Kada ka tafi kai tsaye, amma ka yi zobe kewaye da su, ka kuma fāɗa musu a gaban itatuwan tsamiya.
15 And it shall be, when thou hearest the sound of walking on the tops of the mulberry-trees, that then thou shalt go out to battle; for God will be gone forth before thee to smite the camp of the Philistines.
Da zarar ka ji motsin takawa a sama itatuwan tsamiya, ka fita don yaƙi, domin wannan zai nuna cewa Allah ya fita a gabanka don yă bugi mayaƙan Filistiyawa.”
16 And David did as God had commanded him; and they smote the camp of the Philistines from Gib'on as far as Gezer.
Saboda haka Dawuda ya yi kamar yadda Allah ya umarce shi, suka kuma bugi mayaƙan Filistiyawa, tun daga Gibeyon har zuwa Gezer.
17 And the fame of David went out into all the lands; and the Lord laid the dread of him upon all the nations.
Sai sunan Dawuda ya bazu ko’ina a ƙasar, Ubangiji kuwa ya sa dukan al’ummai suka ji tsoronsa.

< 1 Chronicles 14 >