< Zacharias 10 >

1 Ask you of the Lord rain in season, the early and the latter: the Lord has given bright signs, and will give them abundant rain, to every one grass in the field.
Ku roƙi Ubangiji yă ba ku ruwa a lokacin bazara; Ubangiji ne yake yin gizagizan hadari. Shi ne yake ba wa mutane yayyafin ruwan sama yana kuma ba da tsire-tsire na fili ga kowa.
2 For the speakers have uttered grievous things, and the diviners [have ] [seen] false visions, and they have spoken false dreams, they have given vain comfort: therefore have they fallen away like sheep, and been afflicted, because there was no healing.
Gumaka suna maganganun ruɗu, masu duba suna ganin wahayoyin ƙarya, suna faɗa mafarkan ƙarya suna ba da ta’aziyyar banza. Saboda haka mutane suna yawo kamar tumaki waɗanda suke shan wahala saboda rashin makiyayi.
3 Mine anger was kindled against the shepherds, and I will visit the lambs; and the Lord God Almighty shall visit his flock, the house of Juda, and he shall make them as his goodly horse in war.
“Ina fushi da makiyayan, zan kuma hukunta shugabannin; gama Ubangiji Maɗaukaki zai lura da garkensa, wato, gidan Yahuda, zai kuma sa su zama kamar doki mai fariya cikin yaƙi.
4 And from him he looked, and from him he set [the battle in order], and from him [came] the bow in anger, [and] from him shall come forth every oppressor together.
Daga Yahuda dutsen kusurwa zai fito, daga gare shi za a samu abin kafa tenti, daga gare shi za a sami bakan yaƙi, daga gare shi za a sami kowane mai mulki.
5 And they shall be as warriors treading clay in the ways in war; and they shall set the battle in array, because the Lord is with them, and the riders on horses shall be put to shame.
Tare za su zama kamar mutane masu ƙarfi suna tattake lakar tituna a cikin yaƙi. Domin Ubangiji yana tare da su, za su yi faɗa su kuma yi nasara a kan masu yaƙi a kan dawakai.
6 And I will strengthen the house of Juda, and save the house of Joseph, and I will settle them; because I have loved them: and they shall be as [if] I had not cast them off: for I am the Lord their God, and I will hear them.
“Zan ƙarfafa gidan Yahuda in kuma ceci gidan Yusuf. Zan maido da su domin ina jin tausayinsu. Za su zama kamar ban taɓa ƙinsu ba, gama ni ne Ubangiji Allahnsu zan kuma amsa musu.
7 And they shall be as the warriors of Ephraim, and their heart shall rejoice as with wine: and their children also shall see [it], and be glad; and their heart shall rejoice in the Lord.
Mutanen Efraim za su zama kamar mutane masu ƙarfi, zukatansu kuwa za su yi murna kamar sun sha ruwan inabi.’Ya’yansu za su gani su yi murna; zuciyarsu za tă yi farin ciki a cikin Ubangiji.
8 I will make a sign to them, and gather them in; for I will redeem them, and they shall be multiplied according to their number before.
Zan ba da alama in kuma tattara su. Ba shakka zan fanshe su; za su yi yawa kamar yadda suke a dā.
9 And I will sow them among the people; and they that are afar off shall remember me: they shall nourish their children, and they shall return.
Ko da yake na warwatsa su cikin mutane, duk da haka a can ƙasashe masu nisa za su tuna da ni. Su da’ya’yansu za su rayu, za su kuwa komo.
10 And I will bring them again from the land of Egypt, and I will gather them in from among the Assyrians; and I will bring them into the land of Galaad and to Libanus; and there shall not even one of them be left behind.
Zan komo da su daga Masar in kuma tattara su daga Assuriya. Zan kawo su Gileyad da Lebanon, har wuri yă kāsa musu.
11 And they shall pass through a narrow sea, they shall strike the waves in the sea, and all the deep places of the rivers shall be dried up: and all the pride of the Assyrians shall be taken away, and the sceptre of Egypt shall be removed.
Za su ratsa cikin tekun wahala; zan kwantar da raƙuman teku dukan zurfafan Nilu kuma za su bushe. Za a ƙasƙantar da Assuriya, sandar sarautar Masar kuma za tă rabu da ita.
12 And I will strengthen them in the Lord their God; and they shall boast in his name, says the Lord.
Zan ƙarfafa su a cikin Ubangiji kuma a cikin sunansa za su yi tafiya,” in ji Ubangiji.

< Zacharias 10 >