< Ruth 3 >

1 And she lodged with her mother-in-law: and Noemin her mother-in-law said to her, My daughter, shall I not seek rest for you, that it may be well with you?
Wata rana Na’omi surukar Rut ta ce mata, “’Yata, bai kamata in nema miki gida, inda za a tanada miki da kyau?
2 And now [is] not Booz our kinsman, with whose damsels you were? behold, he winnows barley this night in the floor.
Bowaz wanda kike aiki da bayinsa’yan mata ba danginmu ne na kusa ba? Da daren yau zai sussuka sha’ir nasa a masussuka.
3 But do you wash, and anoint yourself, and put your raiment upon you, and go up to the threshing floor: do not discover yourself to the man until he has done eating and drinking.
Ki yi wanka ki fesa turare, ki kuma sa tufafinki mafi kyau. Sa’an nan ki gangara zuwa masussuka, amma kada ki bari yă san cewa kina a can sai ya gama ci da sha.
4 And it shall come to pass when he lies down, that you shall mark the place where he lies down, and shall come and lift up the covering of his feet, and shall lie down; and he shall tell you what you shall do.
Sa’ad da ya kwanta, ki lura da inda yake kwance. Sa’an nan ki tafi ki buɗe ƙafafunsa ki kwanta. Zai faɗa miki abin da za ki yi.”
5 And Ruth said to her, All that you shall say, I will do.
Rut ta amsa ta ce “Zan yi abin da kika faɗa.”
6 And she went down to the threshing floor, and did according to all that her mother-in-law enjoined her.
Saboda haka ta gangara zuwa masussuka ta kuma yi dukan abin da surukarta ta ce ta yi.
7 And Booz ate and drank, and his heart was glad, and he came to lie down by the side of the heap of corn; and she came secretly, and lifted up the covering of his feet.
Sa’ad da Bowaz ya gama ci da sha yana kuma cikin farin ciki, sai ya tafi ya kwanta a ƙarshen tarin hatsi. Rut kuwa ta sulalle ta je ta buɗe ƙafafunsa ta kwanta.
8 And it came to pass at midnight that the man was amazed, and troubled, and behold, a woman lay at his feet.
Da tsakar dare sai wani abu ya firgitar da mutumin, ya kuwa juya sai ya tarar da mace kwance a ƙafafunsa.
9 And he said, Who are you? and she said, I am your handmaid Ruth; spread therefore your skirt over your handmaid, for you are a near relation.
Sai ya yi tambaya ya ce, “Ke wace ce?” Ta amsa ta ce, “Ni ce baranyarka Rut, ka rufe ni ta mayafinka da yake kai dangi, mai fansa ne na kusa.”
10 And Booz said, Blessed [be] you of the Lord God, [my] daughter, for you have made your latter kindness greater than the former, in that you follow not after young men, whether [any be] poor or rich.
Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji yă albarkace ki’yata. Wannan alheri ya fi wannan da kika nuna da farko. Ba ki gudu kin bi saurayi, mai arziki ko matalauci ba.
11 And now fear not, my daughter, whatever you shall say I will do to you; for all the tribe of my people knows that you are a virtuous woman.
Yanzu kuwa’yata kada ki ji tsoro. Zan yi miki dukan abin da kika roƙa. Dukan’yan’uwana na gari sun san cewa ke mace ce mai halin kirki.
12 And now I am truly akin to you; nevertheless there is a kinsman nearer than I.
Ko da yake gaskiya ne ni dangi ne na kusa, amma akwai dangi mai fansa mafi kusa fiye da ni.
13 Lodge [here] for the night, and it shall be in the morning, if he will do the part of a kinsman to you, well—let him do it: but if he will not do the part of a kinsman to you, I will do the kinsman's part to you, [as] the Lord lives; lie down till the morning.
Ki kwana a nan, da safe kuwa in yana so yă fansa, to, da kyau, sai yă fansa. Amma in ba ya niyya, tabbatacce, na rantse da Ubangiji mai rai zan yi. Ki kwanta a nan sai da safe.”
14 And she lay at his feet until the morning; and she rose up before a man could know his neighbor; and Booz said, Let it not be known that a woman came into the floor.
Saboda haka ta kwanta a ƙafafunsa sai da safe, amma ta tashi kafin a gane wani, sai ya ce, “Kada ki bar wani yă san cewa mace ta zo masussuka.”
15 And he said to her, Bring the apron that is upon you: and she held it, and he measured six measures of barley, and put them upon her, and she went into the city.
Ya kuma ce, “Ki kawo gyalenki da kika yafa ki shimfiɗa shi a nan.” Sa’ad da ta yi haka, sai ya zuba mudu shida na sha’ir ya sa mata a kai. Sa’an nan ya koma gari.
16 And Ruth went in to her mother-in-law, and she said to her, [My] daughter! and [Ruth] told her all that the man had done to her.
Sa’ad da Rut ta koma wurin surukarta Na’omi ta tambaye ta “Yaya aka yi’yata?” Sai ta faɗa mata dukan abin da Bowaz ya yi mata
17 And she said to her, He gave me these six measures of barley, for he said to me, Go not empty to your mother-in-law.
ta kuma ƙara da cewa, “Ya ba ni waɗannan mudu shida na sha’ir, yana cewa, ‘Kada ki koma wurin surukarki hannu wofi.’”
18 And she said, Sit still, [my] daughter, until you shall know how the matter will fall out; for the man will not rest until the matter be accomplished this day.
Sai Na’omi ta ce, “Ki jira,’yata, sai kin ga abin da zai faru. Gama mutumin ba zai huta ba sai an warware batun a yau.”

< Ruth 3 >