< Psalms 92 >

1 A Psalm of a Song for the Sabbath-day. It is a good thing to give thanks to the Lord, and to sing praises to your name, O you Most High;
Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
2 to proclaim your mercy in the morning, and your truth by night,
don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
3 on a lute of ten strings, with a song on the harp.
da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
4 For you, O Lord, have made me glad with your work: and in the operations of your hands will I exult.
Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
5 How have your works been magnified, O Lord! your thoughts are very deep.
Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
6 A foolish man will not know, and a senseless man will not understand this.
Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
7 When the sinners spring up as the grass, and all the workers of iniquity have watched; [it is] that they may be utterly destroyed for ever.
cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
8 But you, O Lord, are most high for ever.
Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
9 For, behold, your enemies shall perish; and all the workers of iniquity shall be scattered.
Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
10 But my horn shall be exalted [as the horn] of a unicorn; and mine old age with rich mercy.
Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
11 And mine eye has seen mine enemies, and mine ear shall hear the wicked that rise up against me.
Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
12 The righteous shall flourish as a palm tree: he shall be increased as the cedar in Libanus.
Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
13 They that are planted in the house of the Lord shall flourish in the courts of our God.
da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
14 Then shall they be increased in a fine old age; and they shall be prosperous; that they may declare
Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
15 that the Lord my God is righteous, and there is no iniquity in him.
suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”

< Psalms 92 >