< Psalms 74 >

1 [A Psalm] of instruction for Asaph. Therefore have you rejected [us], O God, for ever? [therefore] is your wrath kindled against the sheep of your pasture?
Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
2 Remember your congregation which you have purchased from the beginning; you did ransom the rod of your inheritance; this mount Sion wherein you have lived.
Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
3 Lift up your hands against their pride continually; [because of] all that the enemy has done wickedly in your holy places.
Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
4 And they that hate you have boasted in the midst of your feast; they have set up their standards for signs,
Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
5 ignorantly as it were in the entrance above;
Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
6 they cut down its doors at once with axes as in a wood of trees; they have broken it down with hatchet and stone cutter.
Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
7 They have burnt your sanctuary with fire to the ground; they have profaned the habitation of your name.
Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
8 They have said in their heart, [even] all their kindred together, Come, let us abolish the feasts of the Lord from the earth.
Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
9 We have not seen our signs; there is no longer a prophet; and [God] will not know us any more.
Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
10 How long, O God, shall the enemy reproach? shall the enemy provoke your name forever?
Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
11 Therefore turn you away your hand, and your right hand from the midst of your bosom for ever?
Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
12 But God is our King of old; he has wrought salvation in the midst of the earth.
Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
13 You did establish the sea, in your might, you did break to pieces the heads of the dragons in the water.
Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
14 You did break to pieces the heads of the dragon; you did give him [for] meat to the Ethiopian nations.
Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
15 You did cleave fountains and torrents; you dried up mighty rivers.
Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
16 The day is your, and the night is your; you have prepared the sun and the moon.
Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
17 You have made all the borders of the earth; you have made summer and spring.
Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
18 Remember this your creation: an enemy has reproached the Lord, and a foolish people has provoked your name.
Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
19 Deliver not to the wild beasts a soul that gives praise to you: forget not for ever the souls of your poor.
Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
20 Look upon your covenant: for the dark [places] of the earth are filled with the habitations of iniquity.
Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
21 let not the afflicted and shamed one be rejected: the poor and needy shall praise your name.
Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
22 Arise, O God, plead your cause: remember your reproaches that come from the foolish one all the day.
Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
23 Forget not the voice of your suppliants: let the pride of them that hate you continually ascend before you.
Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.

< Psalms 74 >