< Psalms 28 >

1 [A Psalm] of David. To you, O Lord, have I cried; my God, be not silent toward me: lest you be silent toward me, and so I should be likened to them that go down to the pit.
Ta Dawuda. A gare ka nake kira, ya Ubangiji Dutsena; kada ka yi mini kunnen ƙashi. Gama in ka yi shiru, zan zama kamar waɗanda suka gangara rami.
2 Listen to the voice of my supplication, when I pray to you, when I lift up my hands toward your holy temple.
Ka ji kukata ta neman jinƙai yayinda nake kira ka don neman taimako, yayinda nake daga hannuwana wajen Wurinka Mafi Tsarki.
3 Draw not away my soul with sinners, and destroy me not with the workers of iniquity, who speak peace with their neighbors, but evils are in their hearts.
Kada ka ja ni tare da mugaye, tare da masu yin mugunta, masu magana kamar ta alheri ce da maƙwabtansu amma suna riƙe da su a zukatansu.
4 Give them according to their works, and according to the wickedness of their devices: give them according to the works of their hands; render their recompense to them.
Ka sāka musu da ayyukansu da kuma don mugun aikinsu; ka sāka musu saboda abin da hannuwansu suka yi ka kuma mayar musu abin da ya dace da su.
5 Because they have not attended to the works of the Lord, even to the works of his hands, you shall pull them down, and shall not build them up.
Da yake ba su kula da ayyukan Ubangiji da abin da hannuwansa suka yi ba, zai rushe su ba kuwa zai ƙara gina su ba.
6 Blessed be the Lord, for he has listened to the voice of my petition.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya ji kukata na neman jinƙai.
7 The Lord is my helper and my defender; my heart has hoped in him, and I am helped: my flesh has revived, and willingly will I give praise to him.
Ubangiji shi ne ƙarfina da garkuwata; zuciyata ta amince da shi, kuma na sami taimako. Zuciyata ta yi tsalle don farin ciki zan kuwa yi godiya gare shi cikin waƙa.
8 The Lord is the strength of his people, and the saving defender of his anointed.
Ubangiji shi ne ƙarfin mutanensa, kagarar ceto domin shafaffensa.
9 Save your people, and bless your inheritance: and take care of them, and lift them up for ever.
Ka cece mutanenka ka kuma albarkace gādonka; ka zama mai kiwonsu ka kuma riƙe su har abada.

< Psalms 28 >