< Psalms 27 >

1 [A Psalm] of David, before he was anointed. The Lord is my light and my Saviour; whom shall I fear? the Lord is the defender of my life; of whom shall I be afraid?
Ta Dawuda. Ubangiji ne haskena da cetona, wa zan ji tsoro? Ubangiji ne mafakar raina, wane ne zan ji tsoro?
2 When evil-doers drew near against me to eat up my flesh, my persecutors and mine enemies, they fainted and fell.
Sa’ad da mugaye suka tasar mini don su cinye ni, sa’ad da abokan gābana da maƙiyina suka kawo mini hari, sun yi tuntuɓe suka fāɗi.
3 Though an army should set itself in array against me, my heart shall not be afraid: though war should rise up against me, in this am I confident.
Ko da yake mayaƙa sun kewaye ni, zuciyata ba za tă ji tsoro ba; ko da yake ya ɓarke a kaina, duk da haka zan ƙarfafa.
4 One thing have I asked of the Lord, this will I earnestly seek: that I should dwell in the house of the Lord, all the days of my life, that I should behold the fair beauty of the Lord, and survey his temple.
Abu guda na roƙi Ubangiji, wannan shi ne na nema, cewa in zauna a gidan Ubangiji dukan kwanakin raina, in dubi kyan Ubangiji in kuma neme shi a cikin haikalinsa.
5 For in the day of mine afflictions he hid me in his tabernacle: he sheltered me in the secret of his tabernacle; he set me up on a rock.
Gama a lokacin wahala, zai kiyaye ni lafiya a wurin zamansa; zai ɓoye ni cikin inuwar tabanakul nasa ya kuma sa ni can a bisa dutse.
6 And now, behold, he has lifted up mine head over mine enemies: I went round and offered in his tabernacle the sacrifice of joy; I will sing even sing psalms to the Lord.
Sa’an nan kaina zai ɗaukaka a bisa abokan gābana waɗanda suka kewaye ni; a tabanakul nasa zan miƙa hadaya da sowa ta farin ciki; zan rera in kuma yi kiɗi ga Ubangiji.
7 Hear, O Lord, my voice which I have uttered aloud: pity me, and listen to me.
Ka ji muryata sa’ad da na yi kira, ya Ubangiji; ka yi mini jinƙai ka kuma amsa mini.
8 My heart said to you, I have diligently sought your face: your face, O Lord, I will seek.
Zuciyata kan faɗa game da kai, “Nemi fuskarsa!” Fuskarka, Ubangiji, zan nema.
9 Turn not your face away from me, turn not you away from your servant in anger: be you my helper, forsake me not; and, O God my Saviour, overlook me not.
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni, kada ka kore bawanka daga gare ka cikin fushi; kai ne ka kasance mai taimakona. Kada ka ƙi ni ko ka yashe ni, Ya Allah Mai cetona.
10 For my father and my mother have forsaken me, but the Lord has taken me to himself.
Ko da mahaifina da mahaifiyata sun yashe ni, Ubangiji zai karɓe ni.
11 Teach me, O Lord, in your way, and guide me in a right path, because of mine enemies.
Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji; ka bi da ni a miƙaƙƙiyar hanya saboda masu danne ni.
12 Deliver me not over to the desire of them that afflict me; for unjust witnesses have risen up against me, and injustice has lied within herself.
Kada ka ba da ni da sha’awar maƙiyina, gama masu shaidar ƙarya sun taso a kaina, suna numfasa tashin hankali.
13 I believe that I shall see the goodness of the Lord in the land of the living.
Har yanzu ina da ƙarfin gwiwa a wannan cewa zan ga alherin Ubangiji; a ƙasar masu rai.
14 Wait on the Lord: be of good courage, and let your heart be strengthened: yes wait on the Lord.
Ka dogara ga Ubangiji, ka yi ƙarfin hali ka yi ƙarfin zuciya ka kuma dogara ga Ubangiji.

< Psalms 27 >