< Psalms 119 >

1 Alleluia. Blessed are the blameless in the way, who walk in the law of the Lord.
Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
2 Blessed are they that search out his testimonies: they will diligently seek him with the whole heart.
Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
3 For they that work iniquity have not walked in his ways.
Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
4 You have commanded [us] diligently to keep your precepts.
Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
5 O that my ways were directed to keep your ordinances.
Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
6 Then shall I not be ashamed, when I have respect to all your commandments.
Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
7 I will give you thanks with uprightness of heart, when I have learned the judgments of your righteousness.
Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
8 I will keep your ordinances: O forsake me not greatly.
Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
9 Wherewith shall a young man direct his way? by keeping your words.
Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
10 With my whole heart have I diligently sought you: cast me not away from your commandments.
Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
11 I have hidden your oracles in my heart, that I might not sin against you.
Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
12 Blessed are you, O Lord: teach me your ordinances.
Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
13 With my lips have I declared all the judgments of your mouth.
Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
14 I have delighted in the way of your testimonies, [as much] as in all riches.
Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
15 I will meditate on your commandments, and consider your ways.
Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
16 I will meditate on your ordinances: I will not forget your words.
Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
17 Render a recompense to your servant: [so] shall I live, and keep your words.
Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
18 Unveil you mine eyes, and I shall perceive wondrous things of your law.
Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
19 I am a stranger in the earth: hide not your commandments from me.
Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
20 My soul has longed exceedingly for your judgments at all times.
Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
21 You have rebuked the proud: cursed are they that turn aside from your commandments.
Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
22 Remove from me reproach and contempt; for I have sought out your testimonies.
Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
23 For princes sat and spoke against me: but your servant was meditating on your ordinances.
Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
24 For your testimonies are my (meditation) and your ordinances are my counselors.
Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
25 My soul has cleaved to the ground; quicken you me according to your word.
An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
26 I declared my ways, and you did hear me: teach me your ordinances.
Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
27 Instruct me in the way of your ordinances; and I will meditate on your wondrous works.
Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
28 My soul has slumbered for sorrow; strengthen you me with your words.
Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
29 Remove from me the way of iniquity; and be merciful to me by your law.
Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
30 I have chosen the way of truth; and have not forgotten your judgments.
Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
31 I have cleaved to your testimonies, O Lord; put me not to shame.
Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
32 I ran the way of your commandments, when you did enlarge my heart.
Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
33 Teach me, O Lord, the way of your ordinances, and I will seek it out continually.
Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
34 Instruct me, and I will search out your law, and will keep it with my whole heart.
Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
35 Guide me in the path of your commandments; for I have delighted in it.
Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
36 Incline mine heart to your testimonies, and not to covetousness.
Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
37 Turn away mine eyes that I may not behold vanity: quicken you me in your way.
Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
38 Confirm your oracle to your servant, that he may fear you.
Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
39 Take away my reproach which I have feared: for your judgments are good.
Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
40 Behold, I have desired your commandments: quicken me in your righteousness.
Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
41 And let your mercy come upon me, O Lord; [even] your salvation, according to your word.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
42 And [so] I shall render an answer to them that reproach me: for I have trusted in your words.
sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
43 And take not the word of truth utterly out of my mouth; for I have hoped in your judgments. So shall I keep your law continually, for ever and ever.
Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
45 I walked also at large: for I sought out your commandments.
Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
46 And I spoke of your testimonies before kings, and was not ashamed.
Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
47 And I meditated on your commandments, which I loved exceedingly.
gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
48 And I lifted up my hands to your commandments which I loved; and I meditated in your ordinances.
Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
49 Remember your words to your servant, wherein you have made me hope.
Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
50 This has comforted me in mine affliction: for your oracle has quickened me.
Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
51 The proud have transgressed exceedingly; but I swerved not from your law.
Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
52 I remembered your judgments of old, O Lord; and was comforted.
Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
53 Despair took hold upon me, because of the sinners who forsake your law.
Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
54 Your ordinances were my songs in the place of my sojourning.
Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
55 I remembered your name, O Lord, in the night, and kept your law.
Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
56 This I had, because I diligently sought your ordinances.
Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
57 You are my portion, O Lord: I said that I would keep your law.
Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
58 I implored your favor with my whole heart: have mercy upon me according to your word.
Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
59 I thought on your ways, and turned my feet to your testimonies.
Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
60 I prepared myself, (and was not terrified, ) to keep your commandments.
Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
61 The snares of sinners entangled me: but I forgot not your law.
Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
62 At midnight I arose, to give thanks to you for the judgments of your righteousness.
Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
63 I am a companion of all them that fear you, and of them that keep your commandments.
Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
64 O Lord, the earth is full of your mercy: teach me your ordinances.
Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
65 You have wrought kindly with your servant, o Lord, according to your word.
Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
66 Teach me kindness, and instruction, and knowledge: for I have believed your commandments.
Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
67 Before I was afflicted, I transgressed; therefore have I kept your word.
Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
68 Good are you, O Lord; therefore in your goodness teach me your ordinances.
Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
69 The injustice of the proud has been multiplied against me: but I will search out your commandments with all my heart.
Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
70 Their heart has been curdled like milk; but I have meditated on your law.
Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
71 [It is] good for me that you have afflicted me; that I might learn your ordinances.
Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
72 The law of your mouth is better to me than thousands of gold and silver.
Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
73 Your hands have made me, and fashioned me: instruct me, that I may learn your commandments.
Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
74 They that fear you will see me and rejoice: for I have hoped in your words.
Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
75 I know, O Lord, that your judgments are righteousness, and [that] you in truthfulness have afflicted me.
Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
76 Let, I pray you, your mercy be to comfort me, according to your word to your servant.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
77 Let your compassions come to me, that I may live: for your law is my (meditation)
Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
78 Let the proud be ashamed; for they transgressed against me unjustly: but I will meditate in your commandments.
Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
79 Let those that fear you, and those that know your testimonies, turn to me.
Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
80 Let mine heart be blameless in your ordinances, that I may not be ashamed.
Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
81 My soul faints for your salvation: I have hoped in your words.
Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
82 Mine eyes failed [in waiting] for your word, saying, When will you comfort me?
Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
83 For I am become as a bottle in the frost: [yet] I have not forgotten your ordinances.
Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
84 How many are the days of your servant? when will you execute judgment for me on them that persecute me?
Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
85 Transgressors told me [idle tales]; but not according to your law, O Lord.
Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
86 All your commandments are truth; they persecuted me unjustly; help you me.
Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
87 They nearly made an end of me in the earth; but I forsook not your commandments.
Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
88 Quicken me according to your mercy; so shall I keep the testimonies of your mouth.
Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
89 Your word, O Lord, abides in heaven for ever.
Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
90 Your truth [endures] to all generations; you have founded the earth, and it abides.
Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
91 The day continues by your arrangement; for all things are your servants.
Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
92 Were it not that your law is my (meditation) then I should have perished in mine affliction.
Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
93 I will never forget your ordinances; for with them you have quickened me.
Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
94 I am your, save me; for I have sought out your ordinances.
Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
95 Sinners laid wait for me to destroy me; [but] I understood your testimonies.
Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
96 have seen an end of all perfection; [but] your commandment is very broad.
Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
97 How I have loved your law, O Lord! it is my meditation all the day.
Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
98 You have made me wiser than mine enemies [in] your commandment; for it is mine for ever.
Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
99 I have more understanding than all my teachers; for your testimonies are my medication.
Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
100 I understand more that the aged; because I have sought out your commandments.
Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
101 I have kept back my feet from every evil way, that I might keep your words.
Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
102 I have not declined from your judgments; for you have instructed me.
Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
103 How sweet are your oracles to my throat! more so than honey to my mouth!
Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
104 I gain understanding by your commandments: therefore I have hated every way of unrighteousness.
Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
105 Your law is a lamp to my feet, and a light to my paths.
Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
106 I have sworn and determined to keep the judgments of your righteousness.
Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
107 I have been very greatly afflicted, O Lord: quicken me, according to your word.
Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
108 Accept, I pray you, O Lord, the free will offerings of my mouth, and teach me your judgments.
Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
109 My soul is continually in your hands; and I have not forgotten your law.
Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
110 Sinners spread a snare for me; but I erred not from your commandments.
Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
111 I have inherited your testimonies for ever; for they are the joy of my heart.
Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
112 I have inclined my heart to perform your ordinances for ever, in return [for your mercies].
Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
113 I have hated transgressors; but I have loved your law.
Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
114 You are my helper and my supporter; I have hoped in your words.
Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
115 Depart from me, you evil-doers; for I will search out the commandments of my God.
Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
116 Uphold me according to your word, and quicken me; and make me not ashamed of my expectation.
Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
117 Help me, and I shall be saved; and I will meditate in your ordinances continually.
Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
118 You have brought to nothing all that depart from your ordinances; for their inward thought is unrighteous.
Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
119 I have reckoned all the sinners of the earth as transgressors; therefore have I loved your testimonies.
Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
120 Penetrate my flesh with your fear; for I am afraid of your judgments.
Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
121 I have done judgment and justice; deliver me not up to them that injure me.
Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
122 Receive your servant for good: let not the proud accuse me falsely.
Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
123 Mine eyes have failed for your salvation, and for the word of your righteousness.
Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
124 Deal with your servant according to your mercy, and teach me your ordinances.
Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
125 I am your servant; instruct me, and I shall know your testimonies.
Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
126 [It is] time for the Lord to work: they have utterly broken your law.
Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
127 Therefore have I loved your commandments more than gold, or the topaz.
Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
128 Therefore I directed myself [according] to all your commandments: I have hated every unjust way.
saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
129 Your testimonies are wonderful: therefore my soul has sought them out.
Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
130 The manifestation of your words will enlighten, and instruct the simple.
Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
131 I opened my mouth, and drew breath: for I earnestly longed after your commandments.
Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
132 Look upon me and have mercy upon me, after the manner of them that love your name.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
133 Order my steps according to your word: and let not any iniquity have dominion over me.
Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
134 Deliver me from the false accusation of men: so will I keep your commandments.
Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
135 Cause your face to shine upon your servant: and teach me your ordinances.
Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
136 Mine eyes have been bathed in streams of water, because I kept not your law.
Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
137 Righteous are you, O Lord, and upright are your judgments.
Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
138 You has commanded righteousness and perfect truth, [as] your testimonies.
Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
139 Your zeal has quite wasted me: because mine enemies have forgotten your words.
Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
140 Your word [has been] very fully tried; and your servant loves it.
An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
141 I am young and despised: [yet] I have not forgotten your ordinances.
Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
142 Your righteousness is an everlasting righteousness, and your law is truth.
Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
143 Afflictions and distresses found me: [but] your commandments [were] my (meditation)
Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
144 Your testimonies [are] an everlasting righteousness: instruct me, and I shall live.
Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
145 I cried with my whole heart; hear me, O Lord: I will search out your ordinances.
Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
146 I cried to you; save me, and I will keep your testimonies.
Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
147 I arose before the dawn, and cried: I hoped in your words.
Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
148 Mine eyes prevented the dawn, that I might meditate on your oracles.
Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
149 Hear my voice, O Lord, according to your mercy; quicken me according to your judgment.
Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
150 They have drawn near who persecuted me unlawfully; and they are far removed from your law.
Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
151 You are near, O Lord; and all your ways are truth.
Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
152 I have known of old concerning your testimonies, that you have founded them for ever.
Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
153 Look upon mine affliction, and rescue me; for I have not forgotten your law.
Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
154 Plead my cause, and ransom me: quicken me because of your word.
Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
155 Salvation is far from sinners: for they have not searched out your ordinances.
Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
156 Your mercies, O Lord, are many: quicken me according to your judgment.
Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
157 Many are they that persecute me and oppress me: [but] I have not declined from your testimonies.
Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
158 I saw men acting foolishly, and I pined away; for they kept not your oracles.
Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
159 Behold, I have loved your commandments, O Lord: quicken me in your mercy.
Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
160 The beginning of your words is truth; and all the judgments of your righteousness [endure] for ever.
Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
161 Princes persecuted me without a cause, but my heart feared because of your words.
Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
162 I will exult because of your oracles, as one that finds much spoil.
Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
163 I hate and abhor unrighteousness; but I love your law.
Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
164 Seven times in a day have I praised you because of the judgments of your righteousness.
Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
165 Great peace have they that love your law: and there is no stumbling block to them.
Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
166 I waited for your salvation, O Lord, and have loved your commandments.
Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
167 My soul has kept your testimonies, and loved them exceedingly.
Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
168 I have kept your commandments and your testimonies; for all my ways are before you, O Lord.
Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
169 Let my supplication come near before you, o Lord; instruct me according to your oracle.
Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
170 Let my petition come in before you, O Lord; deliver me according to your oracle.
Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
171 Let my lips utter a hymn, when you shall have taught me your ordinances.
Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
172 Let my tongue utter your oracles; for all your commandments are righteous.
Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
173 Let your hand be [prompt] to save me; for I have chosen your commandments.
Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
174 I have longed after your salvation, O Lord; and your law is my (meditation)
Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
175 My soul shall live, and shall praise you; and your judgments shall help me.
Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
176 I have gone astray like a lost sheep; seek your servant; for I have not forgotten your commandments.
Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.

< Psalms 119 >