< Psalms 112 >
1 Alleluia. Blessed is the man that fears the Lord: he will delight greatly in his commandments.
Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
2 His seed shall be mighty in the earth: the generation of the upright shall be blessed.
’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
3 Glory and riches shall be in his house; and his righteousness endures for evermore.
Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
4 To the upright light has sprung up in darkness: he is pitiful, and merciful, and righteous.
Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
5 The good man is he that pities and lends: he will direct his affairs with judgment.
Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
6 For he shall not be moved for ever; the righteous shall be in everlasting remembrance.
Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
7 He shall not be afraid of [any] evil report: his heart is ready to trust in the Lord.
Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
8 His heart is established, he shall not fear, till he shall see [his desire] upon his enemies.
Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
9 He has dispersed abroad; he has given to the poor; his righteousness endures for evermore: his horn shall be exalted with honor.
Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
10 The sinner shall see and be angry, he shall gnash his teeth, and consume away: the desire of the sinner shall perish.
Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.