< Psalms 1 >

1 Blessed is the man who has not walked in the counsel of the ungodly, and has not stood in the way of sinners, and has not sat in the seat of evil men.
Mai farin ciki ne mutumin da ba ya aiki da shawarar mugaye ko yă yi abin da masu zunubi suke yi ko yă zauna tare da masu yin ba’a.
2 But his pleasure is in the law of the Lord; and in his law will he meditate day and night.
Amma yana jin daɗin bin dokar Ubangiji, kuma yana ta nazarinta dare da rana.
3 And he shall be as a tree planted by the brooks of waters, which shall yield its fruit in its season, and its leaf shall not fall off; and whatever he shall do shall be prospered.
Yana kama da itacen da aka shuka kusa da maɓulɓulan ruwa, wanda yake ba da amfani a daidai lokaci wanda kuma ganyensa ba sa bushewa. Duk abin da yake yi, yakan yi nasara.
4 Not so the ungodly; —not so: but rather as the chaff which the wind scatters away from the face of the earth.
Ba haka yake da mugaye ba! Su kamar yayi ne da iska take kwashewa.
5 Therefore the ungodly shall not rise in judgment, nor sinners in the counsel of the just.
Saboda haka mugaye ba za su iya tsayawa a shari’a ba, balle a sami masu zunubi a taron adalai.
6 For the Lord knows the way of the righteous; but the way of the ungodly shall perish.
Gama Ubangiji yana lura da yadda adalai suke yin abubuwa, amma ayyukan mugaye za su kai su ga hallaka.

< Psalms 1 >