< Obdias 1 >

1 The vision of Obdias. Thus says the Lord God to Idumea; I have heard a report from the Lord, and he has sent forth a message to the nations.
Wahayin Obadiya. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce a kan Edom. Mun ji saƙo daga wurin Ubangiji cewa, An aiki jakada zuwa ga al’ummai yă faɗa musu cewa, “Ku tashi, mu tafi mu yi yaƙi da ita.”
2 Arise you, and let us rise up against her to war.
“Duba, zan maishe ki ƙarama a cikin al’ummai; za a rena ki ƙwarai.
3 Behold, I have made you small among the Gentiles: you are greatly dishonored. The pride of your heart has elated you, dwelling [as you do] in the holes of the rocks, [as one that] exalts his habitation, saying in his heart, Who will bring me down to the ground?
Fariyar zuciyarki ta yaudare ki, ke da kike zama can bisa duwatsu kika kuma yi gidanki a kan ƙwanƙoli, ke da kike ce wa kanki, ‘Wa zai iya saukar da ni ƙasa?’
4 If you should mount up as the eagle, and if you should make your nest among the stars, thence will I bring you down, says the Lord.
Ko da yake kina firiya kamar gaggafa kin kuma yi sheƙarki a can cikin taurari, daga can zan saukar da ke,” in ji Ubangiji.
5 If thieves came in to you, or robbers by night, where would you have been cast away? would they not have stolen [just] enough for themselves? and if grape gatherers went in to you, would they not leave a gleaning?
“In ɓarayi suka zo miki, in kuma’yan fashi suka shigo gidan da dare, kash, bala’i zai jira ki ba abin da suke so ne kawai za su sata ba? In kuma masu tsinka’ya’yan inabi suka zo miki, ba sukan bar’ya’yan inabi kaɗan ba?
6 How has Esau been searched out, and [how] have his hidden things been detected?
Amma za a washe Isuwa ƙaƙaf, a kuma yaye ɓoyayyiyar dukiyarsa!
7 They sent you to your coasts: all the men of your covenant have withstood you; your allies have prevailed against you, they have set snares under you: they have no understanding.
Dukan waɗanda kike tarayya da su, za su kore ki zuwa iyaka; abokanki kuma za su yaudare ki, su kuma sha ƙarfinki; waɗanda suke cin abincinki, za su sa miki tarko, amma ba za ki gane ba.
8 In that day, says the Lord, I will destroy the wise men out of Idumea, and understanding out of the mount of Esau.
“A wannan rana,” in jin Ubangiji, “zan hallaka masu hikimar Edom, zan shafe mutane masu fahima a duwatsun Isuwa.
9 And your warriors from Thaeman shall be dismayed, to the end that man may be cut off from the mount of Esau.
Jarumawanki, ya Teman, za su razana, za a kashe kowane mutum a duwatsun Isuwa.
10 Because of the slaughter and the sin [committed against] your brother Jacob, shame shall cover you, and you shall be cut off for ever.
Saboda halin kama-karyar da kika yi wa ɗan’uwanka Yaƙub, za ki sha kunya; za a hallaka ki har abada.
11 From the day that you stood in opposition [to him], in the days when foreigners were taking captive his forces, and strangers entered into his gates, and cast lots on Jerusalem, you also was as one of them.
A ranan nan kin tsaya kawai kina zuba ido yayinda baƙi suke washe dukiyar ɗan’uwanki, baƙi kuma suka shiga ta ƙofofinsa suka jefa ƙuri’a don a rarraba Urushalima, kin tsaya kina kallo kamar ɗaya daga cikin abokan gābansa.
12 And you should not have looked on the day of your brother in the day of strangers; nor should you have rejoiced against the children of Juda in the day of their destruction; neither should you have boasted in the day of [their] affliction.
Bai kamata ki rena ɗan’uwanki a ranar masifarsa ba, ko ki yi farin ciki a kan mutanen Yahuda a ranar hallakarsu, ko ki yi fariya sosai a ranar wahalarsu.
13 Neither should you have gone into the gates of the people in the day of their troubles; nor yet should you have looked upon their gathering in the day of their destruction, nor should you have attacked their host in the day of their perishing.
Bai kamata ki bi ta ƙofofin mutanena a ranar bala’insu ba, ko ki rena su a cikin masifarsu a ranar bala’insu, ko ki ƙwace dukiyarsu a ranar bala’insu ba.
14 Neither should you have stood at the opening of their passages, to destroy utterly those of them that were escaping; neither should you have shut up his fugitives in the day of affliction.
Bai kamata ki tsaya a mararraba don ki kashe waɗanda suke ƙoƙarin tserewa ba, ko ki ba da waɗanda suka tsere ga hannun maƙiyansu a ranar wahalarsu ba.
15 For the day of the Lord is near upon all the Gentiles: as you have done, so shall it be [done] to you: your recompense shall be returned on your [own] head.
“Ranar Ubangiji ta yi kusa don dukan al’ummai. Kamar yadda kuka yi, haka za a yi muku; ayyukanku za su koma a kanku.
16 For as you have drunk upon my holy mountain, [so] shall all the nations drink wine; they shall drink, and go down, and be as if they were not.
Kamar yadda kuka sha a kan tuduna mai tsarki, haka dukan al’ummai za su yi ta sha, za su sha, su kuma sha su zama sai ka ce ba su taɓa kasancewa ba.
17 But on mount Sion there shall be deliverance, and there shall be a sanctuary; and the house of Jacob shall take for an inheritance those that took them for an inheritance.
Amma a kan Dutsen Sihiyona za a sami ceto; Dutsen zai zama mai tsarki, gidan Yaƙub kuma zai mallaki gādonsa.
18 And the house of Jacob shall be fire, and the house of Joseph a flame, and the house of Esau [shall be] for stubble; and [Israel] shall flame forth against them, and shall devour them, and there shall not be a corn-field [left] to the house of Esau; because the Lord has spoken.
Gidan Yaƙub zai zama kamar wuta, gidan Yusuf kuma kamar harshen wuta; gidan Isuwa zai zama kamar tattaka, za a kuma sa masa wuta yă ƙone. Babu wanda zai tsira daga gidan Isuwa.” Ni Ubangiji na faɗa.
19 And they [that dwell] in the south shall inherit the mount of Esau, and they in the plain the Philistines: and they shall inherit the mount of Ephraim, and the plain of Samaria, and Benjamin, and the land of Galaad.
Mutane daga Negeb za su mamaye duwatsun Isuwa, mutane kuma daga gindin tuddai za su mallaki ƙasar Filistiyawa. Za su mamaye filayen Efraim da Samariya, Benyamin kuwa zai mallaki Gileyad.
20 And this [shall be] the domain of the captivity of the children of Israel, the land of the Chananites as far as Sarepta; and the captives of Jerusalem [shall inherit] as far as Ephratha; they shall inherit the cities of the south.
Wannan ƙungiyar Isra’ilawan da aka kwashe zuwa bauta da suke a Kan’ana za su mallaki ƙasar har zuwa Zarefat; waɗannan da aka kwashe zuwa bauta daga Urushalima da suke a Sefarad za su mallaki garuruwan Negeb.
21 And they that escape shall come up from mount Sion, to take vengeance on the mount of Esau; and the kingdom shall be the Lord's.
Masu kawo ceto za su haura zuwa Dutsen Sihiyona don su yi mulkin duwatsun Isuwa. Ubangiji ne zai yi mulki.

< Obdias 1 >