< Numbers 1 >

1 And the Lord spoke to Moses in the wilderness of Sina, in the tabernacle of witness, on the first day of the second month, in the second year of their departure from the land of Egypt, saying,
Ubangiji ya yi magana da Musa a Tentin Sujada a cikin Hamadar Sinai, a rana ta fari na watan biyu a shekara ta biyu, bayan Isra’ilawa suka fito Masar ya ce,
2 Take the sum of all the congregation of Israel according to their kindred, according to the houses of their fathers' families, according to their number by their names, according to their heads: every male
“Ka yi ƙidayan dukan al’umman Isra’ilawa bisa ga iyalansu da kabilarsu, ka rubuta kowa da sunansa bi da bi.
3 from twenty years old and upwards, every one that goes forth in the forces of Israel, take account of them with their strength; you and Aaron take account of them.
Da kai da Haruna za ku lissafta dukan mazan Isra’ila bisa ga sashensu, waɗanda suka kai shekaru ashirin ko fiye, da za su iya shiga soja.
4 And with you there shall be each one of the rulers according to the tribe of each: they shall be according to the houses of their families.
Mutum ɗaya daga kowace kabila wanda yake shugaban danginsa, zai taimake ku.
5 And these are the names of the men who shall be present with you; of the tribe of Ruben, Elisur the son of Sediur.
“Ga sunayen da za su taimake ku. “Daga kabilar Ruben, Elizur ɗan Shedeyur;
6 Of Symeon, Salamiel the son of Surisadai.
daga kabilar Simeyon, Shelumiyel ɗan Zurishaddai;
7 Of Juda, Naasson the son of Aminadab.
daga kabilar Yahuda, Nashon ɗan Amminadab;
8 Of Issachar, Nathanael the son of Sogar.
daga kabilar Issakar, Netanel ɗan Zuwar;
9 Of Zabulon, Eliab the son of Chaelon.
daga kabilar Zebulun, Eliyab ɗan Helon;
10 Of the sons of Joseph, of Ephraim, Elisama the son of Emiud: of Manasses, Gamaliel the son of Phadasur.
daga kabilar’ya’yan Yusuf, daga Efraim, Elishama ɗan Ammihud; daga Manasse, Gamaliyel ɗan Fedazur;
11 Of Benjamin, Abidan the son of Gadeoni.
daga kabilar Benyamin, Abidan ɗan Gideyoni;
12 Of Dan, Achiezer the son of Amisadai.
daga kabilar Dan, Ahiyezer ɗan Ammishaddai;
13 Of Aser, Phagaiel the son of Echran.
daga kabilar Asher, Fagiyel ɗan Okran;
14 Of Gad, Elisaph the son of Raguel.
daga kabilar Gad, Eliyasaf ɗan Deyuwel;
15 Of Nephthali, Achire the son of Aenan.
daga kabilar Naftali, Ahira ɗan Enan.”
16 These were famous men of the congregation, heads of the tribes according to their families: these are heads of thousands in Israel.
Waɗannan su ne mutanen da aka naɗa daga cikin jama’a, shugabannin asalin kabilu. Su ne kuma shugabannin dangogin Isra’ila.
17 And Moses and Aaron took these men who were called by name.
Sai Musa da Haruna suka ɗauki sunayen mutanen nan da aka ba su,
18 And they assembled all the congregation on the first day of the month in the second year; and they registered them after their lineage, after their families, after the number of their names, from twenty years old and upwards, every male according to their number:
suka kira dukan al’umma wuri ɗaya a rana ta fari ga wata na biyu. Aka kuwa rubuta mutanen bisa ga asalin kabilansu da iyalansu. Aka kuma rubuta sunayen maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekaru ashirin ko fiye,
19 as the Lord commanded Moses, so they were numbered in the wilderness of Sina.
yadda Ubangiji ya umarci Musa. Da haka ya ƙidaya su a Hamadar Sinai.
20 And the sons of Ruben the firstborn of Israel according to their kindred, according to their divisions, according to the houses of their families, according to the number of their names, according to their heads, were—all males from twenty years old and upward, every one that went out with the host—
Daga zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
21 the numbering of them of the tribe of Ruben, was forty-six thousand and four hundred.
Jimillar maza daga mutanen Ruben 46,500 ne.
22 For the children of Symeon according to their kindred, according to their divisions, according to the houses of their families, according to the number of their names, according to their polls, all males from twenty years old and upward, every one that goes out with the host,
Daga zuriyar Simeyon. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
23 the numbering of them of the tribe of Symeon, was fifty-nine thousand and three hundred.
Jimillar maza daga mutanen Simeyon 59,300 ne.
24 For the sons of Juda according to their kindred, according to their divisions, according to the houses of their families, according to the number of their names, according to their polls, all males from twenty years old and upward, every one that goes forth with the host,
Daga zuriyar Gad. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
25 the numbering of them of the tribe of Juda, was seventy-four thousand and six hundred.
Jimillar maza daga mutanen Gad 45,650 ne.
26 For the sons of Issachar according to their kindred, according to their divisions, according to the houses of their families, according to the number of their names, according to their polls, all males from twenty years old and upward, every one that goes forth with the host,
Daga zuriyar Yahuda. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
27 the numbering of them of the tribe of Issachar, was fifty-four thousand and four hundred.
Jimillar maza daga mutanen Yahuda 74,600 ne.
28 For the sons of Zabulon according to their kindred, according to their divisions, according to the houses of their families, according to the number of their names, according to their polls, all males from twenty years old and upward, every one that goes out with the host,
Daga zuriyar Issakar. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
29 the numbering of them of the tribe of Zabulon, was fifty-seven thousand and four hundred.
Jimillar maza daga mutanen Issakar 54,400 ne.
30 For the sons of Joseph, the sons of Ephraim, according to their kindred, according to their divisions, according to the houses of their families, according to the number of their names, according to their polls, all males from twenty years old and upward, every one that goes out with the host,
Daga zuriyar Zebulun. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
31 the numbering of them of the tribe of Ephraim, was forty thousand and five hundred.
Jimillar maza daga mutanen Zebulun 57,400 ne.
32 For the sons of Manasse according to their kindred, according to their divisions, according to the houses of their families, according to the number of their names, according to their polls, all males from twenty years old and upward, every one that goes out with the host,
Daga’ya’yan Yusuf. Daga zuriyar Efraim. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
33 the numbering of them of the tribe of Manasse, was thirty-two thousand and two hundred.
Jimillar maza daga mutanen Efraim 40,500 ne.
34 For the sons of Benjamin according to their kindred, according to their divisions, according to the houses of their families, according to the number of their names, according to their polls, every male from twenty years old and upward, every one that goes forth with the host,
Daga zuriyar Manasse. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
35 the numbering of them of the tribe of Benjamin, was thirty-five thousand and four hundred.
Jimillar maza daga mutanen Manasse 32,200 ne.
36 For the sons of Gad according to their kindred, according to their divisions, according to the houses of their families, according to the number of their names, according to their polls, all males from twenty years old and upward, every one that goes forth with the host,
Daga zuriyar Benyamin. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
37 the numbering of them of the tribe of Gad, was forty and five thousand and six hundred and fifty.
Jimillar maza daga mutanen Benyamin 35,400 ne.
38 For the sons of Dan according to their kindred, according to their divisions, according to the houses of their families, according to the number of their names, according to their polls, all males from twenty years old and upward, every one that goes forth with the host,
Daga zuriyar Dan. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
39 the numbering of them of the tribe of Dan, was sixty and two thousand and seven hundred.
Jimillar maza daga mutanen Dan 62,700 ne.
40 For the sons of Aser according to their kindred, according to their divisions, according to the houses of their families, according to the number of their names, according to their polls, every male from twenty years old and upward, every one that goes forth with the host,
Daga zuriyar Asher. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
41 the numbering of them of the tribe of Aser, was forty and one thousand and five hundred.
Jimillar maza daga mutanen Asher 41,500 ne.
42 For the sons of Nephthali according to their kindred, according to their divisions, according to the houses of their families, according to the number of their names, according to their polls, every male from twenty years old and upward, every one who goes forth with the host,
Daga zuriyar Naftali. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
43 the numbering of them of the tribe of Nephthali, was fifty-three thousand and four hundred.
Jimillar maza daga mutanen Naftali kuwa 53,400 ne.
44 This is the numbering which Moses and Aaron and the rulers of Israel, being twelve men, conducted: there was a man for each tribe, they were according to the tribe of the houses of their family.
Waɗannan su ne mazan da Musa da Haruna, tare da shugabanni goma sha biyun nan na Isra’ila suka ƙidaya, kowa a madadin iyalinsa.
45 And the whole numbering of the children of Israel with their host from twenty years old and upward, every one that goes out to set himself in battle array in Israel, came to
Dukan Isra’ilawan da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, an ƙidaya su bisa ga iyalansu.
46 six hundred thousand and three thousand and five hundred and fifty.
Jimillar kuwa ita ce mutum 603,550.
47 But the Levites of the tribe of their family were not counted among the children of Israel.
Ba a dai ƙidaya zuriyar Lawi tare da saura kabilan ba.
48 And the Lord spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa cewa,
49 See, you shall not muster the tribe of Levi, and you shall not take their numbers, in the midst of the children of Israel.
“Ka tabbatar ba ka ƙidaya mutanen Lawi ko kuma ka haɗe su tare a ƙidayan sauran Isra’ilawa ba.
50 And do you set the Levites over the tabernacle of witness, and over all its furniture, and over all things that are in it; and they shall do service in it, and they shall encamp round about the tabernacle.
A maimakon haka sai ka naɗa Lawiyawa su lura da tabanakul Shaida, wato, kan dukan kayayyaki da kuma kome da yake na wuri mai tsarki. Za su ɗauko tabanakul da dukan kayayyakinsa; za su lura da shi, su kasance kewaye da shi.
51 And in removing the tabernacle, the Levites shall take it down, and in pitching the tabernacle they shall set it up: and let the stranger that advances [to touch it] die.
Duk sa’ad da za a gusar da tabanakul, Lawiyawa ne za su saukar da shi; kuma duk sa’ad da za a kafa shi, Lawiyawa ne za su yi haka. Duk wani dabam da ya je kusa da shi za a kashe shi.
52 And the children of Israel shall encamp, every man in his own order, and every man according to his company, with their host.
Sauran Isra’ilawa za su zauna ƙungiya-ƙungiya, kowane mutum a ƙungiyarsa daidai bisa ga ƙa’idarsa.
53 But let the Levites encamp round about the tabernacle of witness fronting it, and [so] there shall be no sin among the children of Israel; and the Levites themselves shall keep the guard of the tabernacle of witness.
Amma Lawiyawa za su kafa sansaninsu kewaye da tabanakul na Shaida. Don kada fushi yă fāɗo a kan al’ummar Isra’ilawa. Hakkin Lawiyawa ne su kula da tabanakul na Shaida.”
54 And the children of Israel did according to all that the Lord commanded Moses and Aaron, so did they.
Isra’ilawa suka yi duk waɗannan kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.

< Numbers 1 >