< Numbers 24 >

1 And when Balaam saw that it pleased God to bless Israel, he did not go according to his custom to meet the omens, but turned his face toward the wilderness.
To, da Bala’am ya ga cewa Ubangiji yana jin daɗin sa wa Isra’ila albarka, bai koma wajen sihiri kamar dā ba, amma ya juya fuskarsa wajen hamada.
2 And Balaam lifted up his eyes, and sees Israel encamped by their tribes; and the Spirit of God came upon him.
Da Bala’am ya duba sai ya ga Isra’ila sun yi sansani kabila, kabila, Ruhun Allah kuwa ya sauko masa,
3 And he took up his parable and said, Balaam son of Beor says, the man who sees truly says,
sai ya yi annabcinsa ya ce, “Maganar Bala’am ɗan Beyor, saƙon mutumin da idanunsa ke gani sarai,
4 he says who hears the oracle of the Mighty One, who saw a vision of God in sleep; his eyes were opened:
maganar mutumin da ya saurari maganar Allah, maganar wanda yake ganin wahayi daga Maɗaukaki, mutumin da ya fāɗi rubda ciki, wanda kuma idanunsa suna a buɗe.
5 How goodly [are] your habitations, Jacob, and your tents, Israel!
“Ina misalin kyan tentunanka, ya Yaƙub, wuraren zamanka, ya Isra’ila!
6 as shady groves, and as gardens by a river, and as tents which God pitched, and as cedars by the waters.
“Kamar kwaruruka suke a shimfiɗe, kamar lambu kusa da rafi, kamar itatuwan aloyes da Ubangiji ya dasa, kamar itatuwa al’ul kusa da ruwaye.
7 There shall come a man out of his seed, and he shall rule over many nations; and the kingdom of Gog shall be exalted, and his kingdom shall be increased.
Ruwa zai kwararo daga bokitinsu; irinsu za su sami ruwa a yalwace. “Sarkinsu zai fi sarkin Agag; mulkinsu zai ɗaukaka.
8 God led him out of Egypt; he has as it were the glory of a unicorn: he shall consume the nations of his enemies, and he shall drain their marrow, and with his darts he shall shoot through the enemy.
“Allah ya fitar da su daga Masar; suna da ƙarfin kutunkun ɓauna. Sun cinye abokan gāban, suka kakkarya ƙasusuwansu; da kibiyoyinsu suka sossoke su.
9 He lay down, he rested as a lion, and as a young lion; who shall stir him up? they that bless you are blessed, and they that curse you are cursed.
Kamar zaki sun laɓe sun kwanta, kamar zakanya, wa zai yi ƙarfin hali yă tashe su? “Bari waɗanda suka albarkace ka, su sami albarka waɗanda kuma suka la’anta ka, su la’antu!”
10 And Balac was angry with Balaam, and clapped his hands together; and Balac said to Balaam, I called you to curse my enemy, and behold you have decidedly blessed [him] this third time.
Fushin Balak ya ƙuna a kan Bala’am. Ya tafa hannunsa, ya ce masa, “Na kira ka don ka la’anta abokan gābana, amma sai ga shi ka sa musu albarka har sau uku.
11 Now therefore flee to your place: I said, I will honor you, but now the Lord has deprived you of glory.
Yanzu ka bar nan ka tafi gida! Na ce zan sāka maka da lada mai kyau, amma Ubangiji ya hana ka samun ladan.”
12 And Balaam said to Balac, Did I not speak to your messengers also whom you sent to me, saying,
Bala’am ya ce wa Balak, “Ban faɗa wa’yan aikan da ka aiko wurina ba cewa,
13 If Balac should give me his house full of silver and gold, I shall not be able to transgress the word of the Lord to make it good or bad by myself; whatever things God shall say, them will I speak.
‘Ko da a ce Balak zai ba ni gidansa cike da azurfa da zinariya, ba zan yi wani abu ko kaɗan saɓanin umarnin Ubangiji Allahna ba, kuma dole in faɗa abin da Ubangiji ya ce ne kawai’?
14 And now, behold, I return to my place; come, I will advise you of what this people shall do to your people in the last days.
Yanzu zan koma wajen mutanena, amma bari in gargaɗe ka game da abin da mutanen nan za su yi wa mutanenka cikin kwanaki masu zuwa.”
15 And he took up his parable and said, Balaam the son of Beor says, the man who sees truly says,
Sa’an nan ya furta saƙonsa. “Maganar Bala’am ɗan Beyor, saƙon mutumin da idanunsa ke gani sarai,
16 hearing the oracles of God, receiving knowledge from the Most High, and having seen a vision of God in sleep; his eyes were opened.
maganar mutumin da ya saurari maganar Allah, wanda yake da sani daga Mafi Ɗaukaka, wanda yake ganin wahayi daga Maɗaukaki, wanda ya fāɗi rubda ciki, wanda kuma idanunsa suna a buɗe.
17 I will point to him, but not now; I bless him, but he draws not near: a star shall rise out of Jacob, a man shall spring out of Israel; and shall crush the princes of Moab, and shall spoil all the sons of Seth.
“Na gan shi, amma ba yanzu ba; na hange shi, amma ba kusa ba. Tauraro zai fito daga Yaƙub; sandan mulki zai fito daga Isra’ila. Zai ragargaje goshin Mowab, kawunan dukan’ya’yan Set.
18 And Edom shall be an inheritance, and Esau his enemy shall be an inheritance [of Israel], and Israel wrought valiantly.
Za a ci Edom da yaƙi; za a ci Seyir, abokiyar gābanta, amma Isra’ila zai ƙara ƙarfi.
19 And [one] shall arise out of Jacob, and destroy out of the city him that escapes.
Mai mulki zai fito daga Yaƙub yă hallaka waɗanda suka ragu a birnin.”
20 And having seen Amalec, he took up his parable and said, Amalec [is] the first of the nations; yet his seed shall perish.
Sai Bala’am ya ga Amalek, ya kuma furta maganarsa. “Amalek yana cikin al’ummai na fari, amma zai zama na ƙarshen da za a hallaka.”
21 And having seen the Kenite, he took up his parable and said, your dwelling-place [is] strong; yet though you should put your nest in a rock,
Sai ya ga Keniyawa, ya kuma furta maganarsa. “Wurin zamanku lafiya yake, an kuma sa sheƙarku a cikin duwatsu;
22 and though Beor should have a skillfully contrived hiding-place, the Assyrians shall carry you away captive.
duk da haka, za a hallaka ku Keniyawa sa’ad da Asshur ya kame ku.”
23 And he looked upon Og, and took up his parable and said, Oh, oh, who shall live, when God shall do these things?
Sai ya furta maganarsa ya ce, “Wayyo, wa zai rayu sa’ad da Allah ya yi haka?
24 And one shall come forth from the hands of the Citians, and shall afflict Assur, and shall afflict the Hebrews, and they shall perish together.
Jiragen ruwa za su zo daga Kittim; za su murƙushe Asshur da Eber, amma su ma za a hallaka su.”
25 And Balaam rose up and departed and returned to his place, and Balac went to his own home.
Sa’an nan Bala’am ya tashi ya koma gidan, Balak kuma ya yi tafiyarsa.

< Numbers 24 >