< Numbers 10 >

1 And the Lord spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Make to yourself two silver trumpets: you shall make them of beaten work; and they shall be to you for the purpose of calling the assembly, and of removing the camps.
“Ka ƙera kakaki guda biyu na azurfa, ka kuma yi amfani da su don kira taron jama’a wuri ɗaya, don kuma ka riƙa sanar da su lokacin tashi daga sansani.
3 And you shall sound with them, and all the congregation shall be gathered to the door of the tabernacle of witness.
Sa’ad da aka busa su biyu, dukan jama’a za su taru a gabanka a ƙofar Tentin Sujada.
4 And if they shall sound with one, all the rulers even the princes of Israel shall come to you.
In ɗaya ne kaɗai aka busa, sai shugabannin kabilan Isra’ila, su taru a gabanka.
5 And you shall sound an alarm, and the camps pitched eastward shall begin to move.
Sa’ad da aka ji karar busar kakaki, sai sansanin da yake a gabashi, su kama hanya.
6 And you shall sound a second alarm, and the camps pitched southward shall move; and you shall sound a third alarm, and the camps pitched westward shall move forward; and you shall sound a fourth alarm, and they that encamp toward the north shall move forward: they shall sound an alarm at their departure.
A kara ta biyu, sansanin da yake a kudanci, su kama hanya. Busan kakaki zai zama alama ta kama hanya.
7 And whenever you shall gather the assembly, you shall sound, but not an alarm.
In don a tara jama’a ne, sai a busa kakaki, amma ba da irin alama ɗaya ba.
8 And the priests the sons of Aaron shall sound with the trumpets; and it shall be a perpetual ordinance for you throughout your generations.
“’Ya’yan Haruna, firistoci ne, za su busa kakaki. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla gare ku da kuma tsararraki masu zuwa.
9 And if you shall go forth to war in your land against your enemies that are opposed to you, then shall you sound with the trumpets; and you shall be had in remembrance before the Lord, and you shall be saved from your enemies.
Duk lokacin da za ku tafi yaƙi a ƙasarku, in akwai waɗansu da suke matsa muku, za ku yi amfani da waɗannan kakaki ta wurin hura su, alama ce, cewa za a je yaƙi. Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, yă cece ku daga maƙiyanku.
10 And in the days of your gladness, and in your feasts, and in your new moons, you shall sound with the trumpets at your whole burnt offerings, and at the sacrifices of your peace-offerings; and there shall be a memorial for you before your God: I [am] the Lord your God.
Haka ma in kuna cikin jin daɗinku, musamman lokacin da kuke bukukkuwanku, kamar Bikin Sabon Wata da dai kowane Bikinku, za ku hura waɗannan kakaki lokacin da kuke miƙa hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama, za su kuma zama muku abin tunawa a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
11 And it came to pass in the second year, in the second month, on the twentieth day of the month, the cloud went up from the tabernacle of witness.
A rana ta ashirin ga wata na biyu, a shekara ta biyu, sai girgijen ya tashi daga tabanakul na Shaida.
12 And the children of Israel set forward with their baggage in the wilderness of Sina; and the cloud rested in the wilderness of Pharan.
Sai Isra’ilawa suka tashi daki-daki daga Hamadar Sinai, suna tafiya daga wuri zuwa wuri, har sai da girgijen ya tsaya a Hamadar Faran.
13 And the first rank departed by the word of the Lord by the hand of Moses.
Suka kama hanya, a wannan lokaci, bisa umarnin Ubangiji, ta wurin Musa.
14 And they first set in motion the order of the camp of the children of Juda with their host; and over their host [was] Naasson, son of Aminadab.
Ɓangarorin sansanin Yahuda suka fara tashi, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Nashon ɗan Amminadab ne shugaba.
15 And over the host of the tribe of the sons of Issachar, [was] Nathanael son of Sogar.
Netanel ɗan Zuwar ne shugaban ɓangaren kabilar Issakar,
16 And over the host of the tribe of the sons of Zabulon, [was] Eliab the son of Chaelon.
Eliyab ɗan Helon kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Zebulun.
17 And they shall take down the tabernacle, and the sons of Gedson shall set forward, and the sons of Merari, who bear the tabernacle.
Sa’an nan aka saukar da tabanakul ƙasa, Gershonawa da mutanen Merari da suke ɗauke da shi suka kama hanya.
18 And the order of the camp of Ruben set forward with their host; and over their host [was] Elisur the son of Sediur.
Sai ɓangarori sansanin Ruben suka biyo, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Elizur ɗan Shedeyur ne shugaba.
19 And over the host of the tribe of the sons of Symeon, [was] Salamiel son of Surisadai.
Shelumiyel ɗan Zurishaddai ne shugaban ɓangaren kabilar Simeyon,
20 And over the host of the tribe of the children of Gad, [was] Elisaph the son of Raguel.
Eliyasaf ɗan Deyuwel kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Gad.
21 And the sons of Caath shall set forward bearing the holy things, and [the others] shall set up the tabernacle until they arrive.
Sai Kohatawa suka kama hanya, ɗauke da kayayyaki masu tsarki, domin kafin su kai wurin da za a kafa sansani, a riga an kafa tabanakul.
22 And the order of the camp of Ephraim shall set forward with their forces; and over their forces [was] Elisama the son of Semiud.
Biye da waɗannan kuma sai ɓangaren sansanin kabilar Efraim suka biyo bisa ga ƙa’ida da aka yi, aka kuma umarta. Elishama ɗan Ammihud ne shugaba.
23 And over the forces of the tribes of the sons of Manasse, [was] Gamaliel the [son] of Phadassur.
Gamaliyel ɗan Fedazur ne shugaban ɓangaren kabilar Manasse,
24 And over the forces of the tribe of the children of Benjamin, [was] Abidan the [son] of Gadeoni.
Abidan ɗan Gideyoni kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Benyamin.
25 And the order of the camp of the sons of Dan shall set forward the last of all the camps, with their forces: and over their forces [was] Achiezer the [son] of Amisadai.
A ƙarshe, a matsayi masu gadin bayan dukan ɓangarori, sai ɓangaren sansanin Dan suka tashi bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ne shugaba.
26 And over the forces of the tribe of the sons of Aser, [was] Phageel the son of Echran.
Fagiyel ɗan Okran ne shugaban ɓangaren kabilan Asher,
27 And over the forces of the tribe of the sons of Nephthali, [was] Achire the son of Aenan.
Ahira ɗan Enan kuma shi ne shugaban kabilar Naftali.
28 These [are] the armies of the children of Israel; and they set forward with their forces.
Wannan shi ne tsarin tafiyar ɓangarorin Isra’ilawa, sa’ad da sukan kama hanya.
29 And Moses said to Obab the son of Raguel the Madianite, the father-in-law of Moses, We are going forward to the place concerning which the Lord said, This will I give to you: Come with us, and we will do you good, for the Lord has spoken good concerning Israel.
Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamidiyane surukinsa, “Yanzu fa, muna shirin tashi ne daga nan, domin mu tafi inda Ubangiji ya ce, ‘Zan ba ku.’ Ka zo tare da mu, za mu kuwa yi maka alheri, gama Ubangiji ya yi wa Isra’ilawa alkawari abubuwa masu kyau.”
30 And he said to him, I will not go, but [I will go] to my land and to my kindred.
Ya amsa, ya ce “A’a, ba zan tafi ba; zan koma ƙasata da kuma wurin mutanena.”
31 And he said, Leave us not, because you have been with us in the wilderness, and you shall be an elder among us.
Amma Musa ya ce, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu. Ka san inda ya kamata mu kafa sansani a hamada, za ka kuma zama idanunmu.
32 And it shall come to pass if you will go with us, it shall even come to pass that in whatever things the Lord shall do us good, we will also do you good.
In ka zo tare da mu, za mu raba duk abin alherin Ubangiji ya ba mu tare da kai.”
33 And they departed from the mount of the Lord a three days' journey; and the ark of the covenant of the Lord went before them a three days' journey to provide rest for them.
Saboda haka suka kama hanya daga dutsen Ubangiji, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji ya ja gabansu a waɗannan kwanaki uku, don yă samo musu masauƙi.
34 And the cloud overshadowed them by day, when they departed from the camp.
A duk lokacin da suka tashi daga sansani, girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
35 And it came to pass when the ark set forward, that Moses said, Arise, O Lord, and let your enemies be scattered: let all that hate you flee.
Duk kuma sa’ad da akwatin ya kama hanya, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji! Ka sa maƙiyanka su warwatse; masu ƙinka kuma su gudu a gabanka.”
36 And in the resting he said, Turn again, O Lord, the thousands [and] tens of thousands in Israel.
Duk sa’ad da akwatin ya sauka kuma, sai Musa ya ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubban da ba a iya ƙidayawa na iyalan Isra’ila.”

< Numbers 10 >