< Leviticus 1 >

1 And the Lord called Moses again and spoke to him out of the tabernacle of witness, saying, Speak to the children of Israel, and you shall say to them,
Ubangiji ya kira Musa ya yi masa magana daga cikin Tentin Sujada ya ce,
2 If [any] man of you shall bring gifts to the Lord, you shall bring your gifts of the cattle and of the oxen and of the sheep.
“Yi magana da Isra’ilawa ka ce musu, ‘Duk sa’ad da waninku ya kawo hadaya ga Ubangiji, ku kawo hadayarku ta dabba daga garkenku ta shanu ko kuwa daga tumakinku.
3 If his gift be a whole burnt offering, he shall bring an unblemished male of the herd to the door of the tabernacle of witness, he shall bring it as acceptable before the Lord.
“‘In hadaya ta ƙonawar daga shanu ne, sai yă miƙa namiji marar lahani. Dole yă kawo shi a ƙofar Tentin Sujada don yă zama yardajje ga Ubangiji.
4 And he shall lay his hand on the head of the burnt offering as a thing acceptable for him, to make atonement for him.
Zai ɗibiya hannunsa a kan hadaya ta ƙonawar, za a kuwa karɓa a madadinsa don a yi kafara dominsa.
5 And they shall kill the calf before the Lord; and the sons of Aaron the priests shall bring the blood, and they shall pour the blood round about on the altar, which [is] at the doors of the tabernacle of witness.
Zai yanka ɗan bijimin a gaban Ubangiji, Haruna kuwa da’ya’yansa maza firist, za su kawo jinin su kuma yafa shi a kan bagaden a kowane gefe a mashigin Tentin Sujada.
6 And having flayed the whole burnt offering, they shall divide it by its limbs.
Zai feɗe hadaya ta ƙonawar, yă yayyanka shi gunduwa-gunduwa.
7 And the sons of Aaron the priests shall put fire on the altar, and shall pile wood on the fire.
’Ya’yan Haruna maza waɗanda suke firistoci za su hura wuta a bagade, su kuma shirya itace a kan wutar.
8 And the sons of Aaron the priests shall pile up the divided parts, and the head, and the fat on the wood on the fire, [the wood] which is on the altar.
Sa’an nan’ya’yan Haruna maza waɗanda suke firistoci za su shirya gunduwa-gunduwar haɗe da kan da kuma kitsen a kan itace mai cin wuta wanda yake a kan bagaden.
9 And the entrails and the feet they shall wash in water, and the priests shall put all on the altar: it is a burnt offering, a sacrifice, a smell of sweet savor to the Lord.
Zai wanke kayan cikin da kuma ƙafafun da ruwa, firist ɗin kuwa zai ƙone dukan waɗannan a kan bagade. Hadaya ce ta ƙonawa, hadaya ce kuma wadda aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
10 And if his gift [be] of the sheep to the Lord, or of the lambs, or of the kids for whole burnt offerings, he shall bring it a male without blemish.
“‘In hadaya ta ƙonawar daga garke ne, ko na tumaki, ko na awaki, zai miƙa namiji ne marar lahani.
11 And he shall lay his hand on its head; and they shall kill it by the side of the altar, toward the north before the Lord, and the sons of Aaron the priests shall pour its blood on the altar round about.
Zai yanka shi a gefen arewa na bagaden a gaban Ubangiji,’ya’yan Haruna firistoci kuwa za su yayyafa jinin dabbar a bagaden a kowane gefe.
12 And they shall divide it by its limbs, and its head and its fat, and the priests shall pile them up on the wood which is on the fire, on the altar.
Zai yanka shi gunduwa-gunduwa, firist kuwa zai shirya su haɗe da kan, da kuma kitsen a kan itace mai cin wutar da yake a kan bagade.
13 And they shall wash the entrails and the feet with water, and the priest shall bring all the [parts] and put them on the altar: it is a burnt offering, a sacrifice, a smell of sweet savor to the Lord.
Zai wanke kayan cikin da kuma ƙafafun da ruwa, firist ɗin kuwa zai ƙone dukan waɗannan a kan bagade. Hadaya ce ta ƙonawa, hadaya ce kuma wadda aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
14 And if he bring his gift, a burnt offering to the Lord, of birds, then shall he bring his gift of doves or pigeons.
“‘In hadaya ga Ubangiji ɗin, hadaya ta ƙonawa ta tsuntsaye ce, zai miƙa kurciya ko’yar tattabara.
15 And the priest shall bring it to the altar, and shall wring off its head; and the priest shall put it on the altar, and shall wring out the blood at the bottom of the altar.
Firist zai kawo ta bagade, yă murɗe wuyan tsuntsun yă ƙone shi a kan bagade; zai tsiyaye jininsa tsuntsun a gefen bagaden.
16 And he shall take away the crop with the feathers, and shall cast it forth by the altar toward the east to the place of the ashes.
Amma zai ɗauki kayan cikin tsuntsun da gashin yă zubar da su a gefen bagaden a wajen gabas a wurin zuba toka.
17 And he shall break it off from the wings and shall not separate it, and the priest shall put it on the altar on the wood which is on the fire: it is a burnt offering, a sacrifice, a sweet smelling savor to the Lord.
Zai tsaga shi biyu a tsaka, amma ba zai raba shi ba. Firist ɗin zai ɗibiya shi a bisa itacen da yake bisa bagaden, yă ƙone shi. Hadaya ce ta ƙonawa, hadaya ce kuma wadda aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.

< Leviticus 1 >