< Leviticus 21 >

1 And the Lord spoke to Moses, saying, Speak to the priests the sons of Aaron, and you shall tell them [that] they shall not defile themselves in their nation for the dead,
Ubangiji ya ce wa Musa, “Yi magana da firistoci,’ya’yan Haruna maza, ka ce musu, ‘Kada firist yă ƙazantar da kansa saboda wani cikin mutanensa da suka mutu,
2 but [they may mourn] for a relative who is very near to them, for a father and mother, and sons and daughters, for a brother,
sai dai na danginsa na kusa, kamar mahaifiyarsa ko mahaifinsa, ɗansa ko’yarsa, ɗan’uwansa,
3 and for a virgin sister that is near to one, that is not espoused to a man; for these one shall defile himself.
ko’yar’uwarsa da ba tă riga ta yi aure ba, wadda take dogara gare shi, da yake ba ta da miji, saboda ita zai iya ƙazantar da kansa.
4 He shall not defile himself suddenly among his people to profane himself.
Kada yă ƙazantar da kansa saboda mutanen da suke da dangantakar da shi ta wurin aure, ta yin haka zai ƙazantar da kansa.
5 And you shall not shave your head for the dead with a baldness on the top; and they shall not shave their beard, neither shall they make gashes on their flesh.
“‘Kada firistoci su aske kansu ƙwal ko su kwakkwafe gemunsu, ko su tsattsage jikunansu.
6 They shall be holy to their God, and they shall not profane the name of their God; for they offer the sacrifices of the Lord as the gifts of their God, and they shall be holy.
Dole su kasance masu tsarki ga Allahnsu, kada kuma su ɓata sunan Allahnsu. Domin sukan miƙa hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta, abincin Allahnsu, saboda haka sai su kasance da tsarki.
7 They shall not take a woman who is a harlot and profaned, or a woman put away from her husband; for he is holy to the Lord his God.
“‘Ba za su auri matan da karuwanci ya ɓata su, ko waɗanda mazansu suka sake su ba, gama firistoci masu tsarki ne ga Allahnsu.
8 And you shall hallow him; he offers the gifts of the Lord your God: he shall be holy, for I the Lord that sanctify them [am] holy.
An ɗauke su da tsarki, domin suna miƙa abincin Allahnku. An ɗauka su masu tsarki gama Ni Ubangiji, mai tsarki ne, Ni wanda ya mai da ku masu tsarki.
9 And if the daughter of a priest should be profaned to go a whoring, she profanes the name of her father: she shall be burnt with fire.
“‘In’yar firist ta ɓata kanta ta wurin zama karuwa, ta kunyatar da mahaifinta ke nan; dole a ƙone ta da wuta.
10 And the priest that is chief among his brethren, the oil having been poured upon the head of the anointed one, and he having been consecrated to put on the garments, shall not take the mitre off his head, and shall not rend his garments:
“‘Babban firist, wanda yake ɗaya cikin’yan’uwansa wanda aka shafe da mai a kansa, wanda kuma aka naɗa don yă sa rigunan firistoci, kada yă bar gashin kansa buzu-buzu, ko ya kyakketa rigunansa.
11 neither shall he go in to any dead body, neither shall he defile himself for his father or his mother.
Ba zai shiga inda akwai gawa ba. Kada yă ƙazantar da kansa, ko ma ta mahaifinsa ce ko ta mahaifiyarsa.
12 And he shall not go forth out of the sanctuary, and he shall not profane the sanctuary of his God, because the holy anointing oil of God [is] upon him: I [am] the Lord.
An keɓe shi domina, kada yă ƙazantar da kansa, kada kuwa yă ɓata Tentin Sujada ta wurin shiga gidan da gawa take, ko ta mahaifinsa, ko ta mahaifiyarsa ce. Ni ne Ubangiji.
13 He shall take for a wife a virgin of his own tribe.
“‘Dole macen da zai aura ta kasance budurwa.
14 But a widow, or one that is put away, or profaned, or a harlot, these he shall not take; but he shall take for a wife a virgin of his own people.
Ba zai auri matan da mijinta ya mutu, ko macen da mijinta ya rabu da ita, ko macen da ta ɓata kanta ta wurin karuwanci ba, sai dai yă auri budurwa daga cikin mutanensa,
15 And he shall not profane his seed among his people: I [am] the Lord that sanctifies him.
don kada yă ƙazantar da’ya’yansa a cikin mutanensa. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da shi mai tsarki.’”
16 And the Lord spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
17 Say to Aaron, A man of your tribe throughout your generations, who shall have a blemish on him, shall not draw near to offer the gifts of his God.
“Faɗa wa Haruna cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, kada ko ɗaya daga cikin zuriyarka, da yake da lahani yă zo kusa domin yă miƙa hadaya ta ci gare ni.
18 No man who has a blemish on him shall draw near; a man blind, lame, with his nose disfigured, or his ears cut,
Duk mai lahani, ko makaho, ko gurgu, ko mai naƙasa, ko mai wani lahani a jiki;
19 a man who has a broken hand or a broken foot,
ko mai karyayyen ƙafa, ko mai karyayyen hannu,
20 or humpbacked, or blear-eyed, or that has lost his eye-lashes, or a man who has a malignant ulcer, or tetter, or one that has lost a testicle.
ko mai ƙusumbi, ko wada, ko wanda yake da lahani a ido, ko mai cuta mai sa ƙaiƙayi, ko mai kirci, ko wanda aka daƙe, ba zai yi kusa domin yă miƙa hadaya ba.
21 Whoever of the seed of Aaron the priest has a blemish on him, shall not draw near to offer sacrifices to your God, because he has a blemish on him; he shall not draw near to offer the gifts of God.
Ba zuriyar Haruna firist, mai lahanin da zai zo kusa don yă miƙa hadayun da aka yi ga Ubangiji da wuta. Da yake yana da lahani, ba zai zo kusa don yă miƙa abincin Allahnsa ba.
22 The gifts of God [are] most holy, and he shall eat of the holy things.
Zai iya cin abinci mafi tsarki na Allahnsa, haka ma abinci mai tsarki;
23 Only he shall not approach the veil, and he shall not draw near to the altar, because he has a blemish; and he shall not profane the sanctuary of his God, for I am the Lord that sanctifies them.
duk da haka saboda lahaninsa, ba zai yi kusa da labule, ko yă yi kusa da bagade don kada yă ƙazantar da wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji wanda yake mai da su masu tsarki.’”
24 And Moses spoke to Aaron and his sons, and to all the children of Israel.
Sai Musa ya faɗa wannan wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa.

< Leviticus 21 >