< Leviticus 2 >

1 And if a soul bring a gift, a sacrifice to the Lord, his gift shall be fine flour; and he shall pour oil upon it, and shall put frankincense on it: it is a sacrifice.
“‘Sa’ad da wani ya kawo hadaya ta gari ga Ubangiji, hadayarsa za tă zama gari mai laushi ne. Zai zuba mai a kai, yă sa turare a kansa
2 And he shall bring it to the priests the sons of Aaron: and having taken from it a handful of the fine flour with the oil, and all its frankincense, then the priest shall put the memorial of it on the altar: [it is] a sacrifice, an odour of sweet savor to the Lord.
yă kai wa’ya’yan Haruna maza waɗanda suke firistoci. Firist zai ɗiba gari mai laushin a tafin hannu da kuma man, tare da dukan turaren, yă ƙone wannan a sashen tunawa a kan bagade, hadaya ce da aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
3 And the remainder of the sacrifice shall be for Aaron and his sons, a most holy portion from the sacrifices of the Lord.
Sauran hadaya ta garin zai zama na Haruna da’ya’yansa; sashe mafi tsarki ne na hadayar da aka yi ga Ubangiji ta wuta.
4 And if he bring as a gift a sacrifice baked from the oven, a gift to the Lord of fine flour, [he shall bring] unleavened bread kneaded with oil, and unleavened cakes anointed with oil.
“‘In kuka kawo toyayyen hadayar gari da aka yi daga matoya, zai ƙunshi gari mai laushi, toyayye ba tare da yisti ba, gauraye kuma da mai, ko kuwa ƙosai da aka yi ba tare da yisti ba, aka kuma kwaɓa da mai.
5 And if your gift [be] a sacrifice from a pan, it is fine flour mingled with oil, unleavened [offerings].
In an toya hadaya ta garinku a kasko, sai a yi shi da gari mai laushi haɗe da mai, ba kuwa da yisti ba.
6 And you shall break them into fragments and pour oil upon them: it is a sacrifice to the Lord.
A gutsuttsura shi, a zuba mai a kansa, hadaya ce ta hatsi.
7 And if your gift be a sacrifice from the hearth, it shall be made of fine flour with oil.
In hadayarku ta hatsin da aka dafa ne a tukunya, sai a yi shi da gari mai laushi da kuma mai.
8 And he shall offer the sacrifice which he shall make of these to the Lord, and shall bring it to the priest.
A kawo hatsin da aka yi da waɗannan abubuwa ga Ubangiji; a ba wa firist wanda zai ɗauka yă kai bagade.
9 And the priest shall approach the altar, and shall take away from the sacrifice a memorial of it, and the priest shall place it on the altar: a burnt offering, a smell of sweet savor to the Lord.
Zai fid da sashen tunawa daga hadaya ta gari, yă ƙone shi a kan bagade kamar hadayar da ka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
10 And that which is left of the sacrifice [shall be] for Aaron and his sons, most holy from the burnt offerings of the Lord.
Sauran hadaya ta garin za tă zama ta Haruna da’ya’yansa; sashe mafi tsarki ne na hadayun da aka yi ga Ubangiji ta wuta.
11 You shall not leaven any sacrifice which you shall bring to the Lord; for [as to] any leaven, or any honey, you shall not bring of it to offer a gift to the Lord.
“‘Kowace hadaya ta garin da kuka kawo ga Ubangiji, dole a yi shi ba tare da yisti ba, gama ba za ku ƙone wani yisti, ko zuma a cikin hadayar da aka yi ga Ubangiji ta wuta ba.
12 You shall bring them in the way of fruits to the Lord, but they shall not be offered on the altar for a sweet smelling savor to the Lord.
Za ku iya kawo su ga Ubangiji kamar hadaya ta’ya’yan fari, amma ba za a miƙa su a bagade kamar turare mai ƙanshi ba.
13 And every gift of your sacrifice shall be seasoned with salt; omit not the salt of the covenant of the Lord from your sacrifices: on every gift of yours you shall offer salt to the Lord your God.
A sa gishiri a dukan hadayunku na hatsi. Kada a rasa sa gishirin alkawari na Allahnku a hadayunku na hatsi, a sa gishiri a dukan hadayunku.
14 And if you would offer a sacrifice of first fruits to the Lord, [it shall be] new grains ground [and] roasted for the Lord; so shall you bring the sacrifice of the first fruits.
“‘In kuka kawo hadaya ta gari na’ya’yan fari ga Ubangiji, sai ku miƙa ɓarzajjen kawunan sabon hatsin da aka gasa a wuta.
15 And you shall pour oil upon it, and shall put frankincense on it: it is a sacrifice.
A sa mai da turare a kansa, hadaya ce ta hatsi.
16 And the priest shall offer the memorial of it [taken] from the grains with the oil, and all its frankincense: it is a burnt offering to the Lord.
Firist zai ƙone sashe na ɓarzajjen hatsin da kuma mai, tare da turare don tunawa, gama hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.

< Leviticus 2 >