< Leviticus 18 >

1 And the Lord spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Speak to the children of Israel, and you shall say to them, I [am] the Lord your God.
“Yi wa Isra’ilawa magana ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ni ne Ubangiji Allahnku.
3 You shall not do according to the devices of Egypt, in which you lived: and according to the devices of the land of Chanaan, into which I bring you, you shall not do; and you shall not walk in their ordinances.
Kada ku yi yadda suke yi a Masar inda da kuke zama, kuma ba a ku yi kamar yadda suke yi a ƙasar Kan’ana inda nake kawo ku ba. Kada ku yi yadda suke yin abubuwa.
4 You shall observe my judgments, and shall keep my ordinances, and shall walk in them: I [am] the Lord your God.
Dole ku kiyaye dokokina kuma ku lura ku bi farillaina. Ni ne Ubangiji Allahnku.
5 So you shall keep all my ordinances, and all my judgments, and do them; which if a man do, he shall live in them: I [am] the Lord your God.
Ku kiyaye farillaina da dokokina, gama mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu. Ni ne Ubangiji.
6 No man shall draw near to any of his near kindred to uncover their nakedness; I [am] the Lord.
“‘Kada wani ya kusaci wani dangi na kusa don yă yi jima’i. Ni ne Ubangiji.
7 You shall not uncover the nakedness of your father, or the nakedness of your mother, for she is your mother; you shall not uncover her nakedness.
“‘Kada ka ƙasƙantar da mahaifinka ta wurin kwana da mahaifiyarka. Ita mahaifiyarka ce; kada ka yi jima’i da ita.
8 You shall not uncover the nakedness of your father's wife; it is your father's nakedness.
“‘Kada ka yi jima’i da matar mahaifinka, wannan zai ƙasƙantar da mahaifinka.
9 The nakedness of your sister by your father or by your mother, born at home or abroad, their nakedness you shall not uncover.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwarka, ko’yar mahaifinka ko’yar mahaifiyarka, ko an haife ta a gida ɗaya da kai ko kuwa a wani wuri dabam.
10 The nakedness of your son's daughter, or your daughter's daughter, their nakedness you shall not uncover; because it is your nakedness.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar ɗanka ko’yar’yarka, wannan zai ƙasƙantar da kai.
11 You shall not uncover the nakedness of the daughter of your father's wife; she is your sister by the same father: you shall not uncover her nakedness.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar matar mahaifinka wadda aka haifa wa mahaifinka; ita’yar’uwarka ce.
12 You shall not uncover the nakedness of your father's sister, for she is near akin to your father.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifinka, ita dangin mahaifinka ne na kusa.
13 You shall not uncover the nakedness of your mother's sister, for she is near akin to your mother.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifiyarka, domin ita dangin mahaifiyarka ce na kusa.
14 You shall not uncover the nakedness of your father's brother, and you shall not go in to his wife; for she is your relation.
“‘Kada ka ƙasƙantar da ɗan’uwan mahaifinka ta wurin kusaci matarsa don ka yi jima’i da ita, ita bābarka ce.
15 You shall not uncover the nakedness of your daughter-in-law, for she is your son's wife, you shall not uncover her nakedness.
“‘Kada ka yi jima’i da matar ɗanka. Ita matar ɗanka ne; kada ka yi jima’i da ita.
16 You shall not uncover the nakedness of your brother's wife: it is your brother's nakedness.
“‘Kada ka yi jima’i da matar ɗan’uwanka; wannan zai ƙasƙanta ɗan’uwanka.
17 The nakedness of a woman and her daughter shall you not uncover; her son's daughter, and her daughter's daughter, shall you not take, to uncover their nakedness, for they are your kinswomen: it is impiety.
“‘Kada ka yi jima’i da mace da kuma’yarta. Kada ka yi jima’i da’yar ɗanta ko’yar’yarta; su danginta ne na kusa. Wannan mugun abu ne.
18 You shall not take a wife in addition to her sister, as a rival, to uncover her nakedness in opposition to her, while she is yet living.
“‘Kada ka auri’yar’uwar matarka ta zama kishiyar matarka ka kuma yi jima’i da ita yayinda matarka tana da rai.
19 And you shall not go in to a woman under separation for her uncleanness, to uncover her nakedness.
“‘Kada ka kusaci mace don ka yi jima’i da ita a lokacin ƙazantar al’adarta.
20 And you shall not lie with your neighbor's wife, to defile yourself with her.
“‘Kada ka yi jima’i da matar maƙwabcinka ka ƙazantar da kanka tare da ita.
21 And you shall not give of your seed to serve a ruler; and you shall not profane my holy name; I [am] the Lord.
“‘Kada ku ba da wani daga cikin’ya’yanku don a yi hadaya wa Molek, gama ba za ku ƙasƙantar da sunan Allahnku ba. Ni ne Ubangiji.
22 And you shall not lie with a man as with a woman, for it is an abomination.
“‘Kada ka kwana da namiji kamar yadda namiji yakan kwana da ta mace, wannan abin ƙyama ne.
23 Neither shall you lie with any quadruped for copulation, to be polluted with it: neither shall a woman present herself before any quadruped to have connexion with it; for it is an abomination.
“‘Kada ka yi jima’i da dabba ka ƙazantar da kanka. Mace ba za tă ba da kanta ga dabba don yă yi jima’i da ita ba; wannan abin ƙyama ne.
24 Do not defile yourselves with any of these things; for in all these things the nations are defiled, which I drive out before you,
“‘Kada ku ƙazantar da kanku da wani daga cikin waɗannan, domin haka al’umman da zan kora a gabanku suka ƙazantu.
25 and the land is polluted; and I have recompensed their iniquity to them because of it, and the land is aggrieved with them that dwell upon it.
Har ƙasar ma ta ƙazantu, saboda haka na hukunta ta saboda zunubinta, ƙasar kuwa ta amayar da mazaunanta.
26 And you shall keep all my statutes and all my ordinances, and you shall do none of these abominations; neither the native, nor the stranger that joins himself with you:
Amma dole ku kiyaye farillaina da kuma dokokina. Kada haifaffe ɗan ƙasa da baƙin da suke zama a cikinku yă yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama,
27 (for all these abominations the men of the land did who were before you, and the land was defiled, )
gama mutanen da suka zauna a wannan ƙasa kafin ku sun aikata dukan waɗannan abubuwa, suka kuma ƙazantu.
28 and lest the land be aggrieved with you in your polluting it, as it was aggrieved with the nations before you.
Kuma in kuka ƙazantar da ƙasar, za tă amayar da ku kamar yadda ta amayar da al’umman da suka riga ku.
29 For whoever shall do any of these abominations, the souls that do them shall be destroyed from among their people.
“‘Duk wanda ya yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama, dole a fid da mutumin daga cikin mutanensa.
30 And you shall keep mine ordinances, that you may not do any of the abominable practices, which have taken place before your time: and you shall not be polluted in them; for I [am] the Lord your God.
Ku kiyaye umarnaina kuma kada yi ku wata al’ada mai banƙyamar da aka yi kafin ku zo kuma kada ku ƙazantar da kanku da su. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”

< Leviticus 18 >