< Leviticus 17 >

1 And the Lord spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Speak to Aaron and to his sons, and to all the children of Israel, and you shall say to them, This is the word which the Lord has commanded, saying,
“Yi magana da Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji ya umarta.
3 Every man of the children of Israel, or of the strangers dwelling among you, who shall kill a calf, or a sheep, or a goat in the camp, or who shall kill it out of the camp,
Duk mutumin Isra’ilan da ya yanka sa, ɗan rago ko akuya a sansani ko waje da shi
4 and shall not bring it to the door of the tabernacle of witness, so as to sacrifice it for a whole burnt offering or peace-offering to the Lord to be acceptable for a sweet smelling savor: and whoever shall kill it without, and shall not bring it to the door of the tabernacle of witness, so as to offer it as a gift to the Lord before the tabernacle of the Lord; blood shall be imputed to that man, he has shed blood; that soul shall be cut off from his people.
a maimakon kawo shi a matsayin hadaya ga Ubangiji a gaban tabanakul na Ubangiji, za a ɗauki wannan mutum a matsayi mai laifin zub da jini, ya zub da jini, kuma dole a raba shi da mutanensa.
5 That the children of Israel may offer their sacrifices, all that they shall kill in the fields, and bring them to the Lord to the doors of the tabernacle of witness to the priest, and they shall sacrifice them as a peace-offering to the Lord.
Wannan ya zama haka saboda Isra’ilawa su kawo wa Ubangiji hadayun da suke yi a filaye. Dole su kawo su ga firist, wato, ga Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, su miƙa su a matsayin hadayun salama.
6 And the priest shall pour the blood on the altar round about before the Lord by the doors of the tabernacle of witness, and shall offer the fat for a sweet smelling savor to the Lord.
Firist zai yayyafa jinin a bagaden Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, yă kuma ƙone kitsen kamar ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
7 And they shall no longer offer their sacrifices to vain [gods] after which they go a whoring; it shall be a perpetual statute to you for your generations.
Kada kuma su ƙara yin hadayunsu ga gumaka masu siffar bunsurai waɗanda suka bauta wa. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a gare su wa tsararraki masu zuwa.’
8 And you shall say to them, Whatever man of the children of Israel, or of the sons of the proselytes dwelling among you, shall offer a whole burnt offering or a sacrifice,
“Faɗa musu, ‘Duk wani mutumin Isra’ila ko wani baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya miƙa hadaya ta ƙonawa ko sadaka
9 and shall not bring it to the door of the tabernacle of witness to sacrifice it to the Lord, that man shall be destroyed from among his people.
kuma bai kawo shi a ƙofar Tentin Sujada don yă miƙa shi ga Ubangiji ba, dole a raba wannan mutum da mutanensa.
10 And whatever man of the children of Israel, or of the strangers dwelling among you, shall eat any blood, I will even set my face against that soul that eats blood, and will destroy it from its people.
“‘Duk mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya ci wani jini, zan yi gāba da wannan mutum wanda ya ci jinin, za a kuma raba shi da mutanensa.
11 For the life of flesh is its blood, and I have given it to you on the altar to make atonement for your souls; for its blood shall make atonement for the soul.
Gama ran halitta yana a cikin jinin, kuma na ba da shi gare ku don kafara a kan bagade, jini ne yake kafara saboda ran mutum.
12 Therefore I said to the children of Israel, No soul of you shall eat blood, and the stranger that abides among you shall not eat blood.
Saboda haka na ce wa Isra’ilawa, “Babu waninku da zai ci jini, babu wani baƙon da yake zama a cikinku da zai ci jini.”
13 And whatever man of the children of Israel, or of the strangers dwelling among you shall take any animal in hunting, beast, or bird, which is eaten, then shall he pour out the blood, and cover it in the dust.
“‘Duk wani mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinku wanda ya ji wa wani dabba ko tsuntsu wanda ake ci ciwo, dole yă tsiyaye jinin yă rufe shi da ƙasa,
14 For the blood of all flesh is its life; and I said to the children of Israel, You shall not eat the blood of any flesh, for the life of all flesh is its blood: every one that eats it shall be destroyed.
domin ran kowace halitta yana cikin jini. Shi ya sa na ce wa Isra’ilawa, “Kada ku ci jinin wani halitta, domin ran kowace halitta yana cikin jinin; duk wanda ya ci shi dole a fid da shi.”
15 And every soul which eats that which has died of itself, or is taken of beasts, either among the natives or among the strangers, shall wash his garments, and bathe himself in water, and shall be unclean until evening: then shall he be clean.
“‘Kowa, ko haifaffe ɗan ƙasa ko baƙo, da ya ci wani abin da aka sami a mace, ko naman jeji ya yayyage, dole yă wanke rigunansa, yă kuma yi wanka, zai kuma ƙazantu har yamma; sa’an nan zai tsarkake.
16 But if he do not wash his garments, and do not bathe his body in water, then shall he bear his iniquity.
Amma in bai wanke rigunansa ya kuma yi wanka ba, alhaki zai kasance a kansa.’”

< Leviticus 17 >