< Lamentations 3 >

1 ALEPH. I am the man that sees poverty, through the rod of his wrath upon me.
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 He has taken me, and led me away into darkness, and not [into] light.
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 Nay, against me has he turned his hand all the day.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 He has made old my flesh and my skin; he has broken my bones.
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 BETH. He has built against me, and compassed my head, and brought travail [upon me].
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 He has set me in dark places, as them that have long been dead.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 He has builded against me, and I can’t come forth: he has made my brazen [chain] heavy.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 GIMEL. Yes, [though] I cry and shout, he shuts out my prayer.
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 DALETH. He has built up my ways, he has hedged my paths;
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 he has troubled me, [as] a she-bear lying in wait: he is to me [as] a lion in secret places.
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 He pursued [me] after I departed, and brought me to a stand: he has utterly ruined me.
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 HE. He has bent his bow, and set me as a mark for the arrow.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 He has caused the arrows of his quiver to enter into my reins.
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 I became a laughing stock to all my people; and their song all the day.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 VAU. He has filled me with bitterness, he has drenched me with gall.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 And he has dashed out my teeth with gravel, he has fed me with ashes.
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 He has also removed my soul from peace: I forgot prosperity.
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 Therefore my success has perished, and my hope from the Lord.
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 ZAIN. I remembered by reason of my poverty, and because of persecution my bitterness and gall shall be remembered;
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 and my soul shall meditate with me.
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 This will I lay up in my heart, therefore I will endure.
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 HETH. [It is] the mercies of the Lord, that he has not failed me, because his compassions are not exhausted. Pity [us], O Lord, early [every] month: for we are not brought to an end, because his compassions are not exhausted.
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 [They are] new every morning: great is your faithfulness.
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 The Lord is my portion, says my soul; therefore will I wait for him.
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 TETH. The Lord is good to them that wait for him: the soul which shall seek him
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 [is] good, and shall wait for, and quietly expect salvation of the Lord.
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 TETH. [It is] good for a man when he bears a yoke in his youth.
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 He will sit alone, and be silent, because he has borne [it] upon him.
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 JOD. He will give [his] cheek to him that smites him: he will be filled full with reproaches.
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 For the Lord will not reject for ever.
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 CHAPH. For he that has brought down will pity, and [that] according to the abundance of his mercy.
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 He has not answered [in anger] from his heart, though he has brought low the children of a man.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 LAMED. To bring down under his feet all the prisoners of the earth,
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 to turn aside the judgment of a man before the face of the Most High,
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 to condemn a man [unjustly] in his judgment, the Lord has not given commandment.
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Who has thus spoken, and it has come to pass? the Lord has not commanded it.
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Out of the mouth of the Most High there shall not come forth evil and good.
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 MEM. Why should a living man complain, a man concerning his sin?
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 NUN. Our way has been searched out and examined, and we will turn to the Lord.
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 Let us lift up our hearts with [our] hand to the lofty One in heaven.
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 We have sinned, we have transgressed; and you have not pardoned.
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 SAMECH. You has visited [us] in wrath, and driven us away: you has slain, you has not pitied.
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 You have veiled yourself with a cloud because of prayer, that I might be blind,
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 and be cast off. AIN. You have set us [alone] in the midst of the nations.
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 All our enemies have opened their mouth against us.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 Fear and wrath are come upon us, suspense and destruction.
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 Mine eye shall pour down torrents of water, for the destruction of the daughter of my people.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 PHE. Mine eye is drowned [with tears], and I will not be silent, so that there shall be no rest,
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 until the Lord look down, and behold from heaven.
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 Mine eye shall prey upon my soul, because of all the daughters of the city.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 TSADE. The fowlers chased me as a sparrow, all mine enemies destroyed my life in a pit without cause,
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 and laid a stone upon me.
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 Water flowed over my head: I said, I am cut off.
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 KOPH. I called upon your name, O Lord, out of the lowest dungeon.
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 You heard my voice: close not your ears to my supplication.
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 You drew near to my help: in the day wherein I called upon you you said to me, Fear not.
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 RECHS. O Lord, you has pleaded the causes of my soul; you has redeemed my life.
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 You have seen, O Lord, my troubles: you have judged my cause.
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 You have seen all their vengeance, [you have looked] on all their devices against me.
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 CHSEN. You have heard their reproach [and] all their devices against me;
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 the lips of them that rose up against me, and their plots against me all the day;
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 their sitting down and their rising up: look you upon their eyes.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 You will render them a recompense, O Lord, according to the works of their hands.
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 THAU. You will give them [as] a covering, the grief of my heart.
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 You will persecute them in anger, and will consume them from under the heaven, O Lord.
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.

< Lamentations 3 >