< Judges 21 >

1 Now the children of Israel swore in Massephath, saying, No man of us shall give his daughter to Benjamin for a wife.
Mutanen Isra’ila sun riga sun yi rantsuwa a Mizfa cewa, “Ba ɗayanmu da zai ba da’yarsa aure ga mutumin Benyamin.”
2 And the people came to Baethel, and sat there until evening before God: and they lifted up their voice and wept with a great weeping;
Sai mutanen suka tafi Betel, inda suka zauna a gaban Allah har yamma, suna tā da muryoyinsu suna kuka mai zafi.
3 and said, Therefore, O Lord God of Israel, has this come to pass, that today one tribe should be counted [as missing] from Israel?
Suka ce, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, “Me ya sa wannan abu ya faru da Isra’ila? Don me kabila ɗaya daga Isra’ila za tă ɓace a yau?”
4 And it came to pass on the morrow that the people rose up early, and built there an altar, and offered up whole burnt offerings and peace offerings.
Kashegari da sassafe mutane suka gina bagade suka miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.
5 And the children of Israel said, Who of all the tribes of Israel, went not up in the congregation to the Lord? for there was a great oath concerning those who went not up to the Lord to Massephath, saying, He shall surely be put to death.
Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji ba?” Gama an yi rantsuwa cewa duk wanda ya kāsa zuwa taro a gaban Ubangiji a Mizfa lalle a kashe shi.
6 And the children of Israel relented toward Benjamin their brother, and said, To-day one tribe is cut off from Israel.
To, Isra’ilawa suka yi juyayin’yan’uwansu, mutanen Benyamin. “Yau an hallaka kabila daga cikin Isra’ila.
7 What shall we do for wives for the rest that remain? whereas we have sworn by the Lord, not to give them of our daughters for wives.
Yaya za mu ba wa waɗanda suka rage mata, da yake mun riga mun yi rantsuwa a gaban Ubangiji, ba za mu ba su ɗaya daga’ya’yanmu su aura ba?”
8 And they said, What one [man is there] of the tribes of Israel, who went not up to the Lord to Massephath? and, behold, no man came to the camp from Jabis Galaad to the assembly.
Sa’an nan suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji a Mizfa ba?” Sai su gane cewa babu wani daga Yabesh Gileyad da ya zo sansani don taron.
9 And the people were numbered, and there was not there a man from the inhabitants of Jabis Galaad.
Gama da aka yi ƙidaya mutane, sai aka gane cewa babu wani daga mutanen Yabesh Gileyad da yake a can.
10 And the congregation sent there twelve thousand men of the strongest, and they charged them, saying, Go you and strike the inhabitants of Jabis Galaad with the edge of the sword.
Saboda haka sai taron ya umarci jarumai dubu goma sha biyu su je Yabesh Gileyad su karkashe waɗanda suke zaune a can, duk da mata da yara.
11 And this shall you do: every male and every woman that has known the lying with man you shall devote [to destruction], but the virgins you shall save alive: and they did so.
Suka ce musu, “Ga abin da za ku yi. Ku karkashe duk namiji da kowace macen da ta riga ta san namiji.”
12 And they found among the inhabitants of Jabis Galaad four hundred young virgins, who had not known man by lying with him; and they brought them to Selom in the land of Chanaan.
Suka samu a cikin mutanen da suke zaune a Yabesh Gileyad mata ɗari huɗu da ba su taɓa kwana da namiji ba, suka kwashe su zuwa sansani a Shilo a Kan’ana.
13 And all the congregation sent and spoke to the children of Benjamin in the rock Remmon, and invited them to [make] peace.
Sa’an nan dukan taro suka aika wa mutanen Benyamin da suke a Dutsen Rimmon cewa yaƙi ya ƙare, yanzu sai salama.
14 And Benjamin returned to the children of Israel at that time, and the children of Israel gave them the women whom they [had] save alive of the daughters of Jabis Galaad; and they were content.
Saboda haka mutanen Benyamin suka komo a lokacin aka kuma ba su matan Yabesh Gileyad nan da aka bari da rai. Amma matan ba su ishe su duka ba.
15 And the people relented for Benjamin, because the Lord had made a breach in the tribes of Israel.
Mutanen kuwa suka yi juyayi saboda mutanen Benyamin, domin Ubangiji ya yi gibi a cikin kabilan Isra’ila.
16 And the elders of the congregation said, What shall we do for wives for them that remain? for the women have been destroyed out of Benjamin.
Shugabannin taron suka ce, “Da matan Benyamin da aka hallaka, yaya za mu yi da mazan da suka ragu da ba su sami mata ba?”
17 And they said, [There must be] an inheritance of them that are escaped of Benjamin; and [so] a tribe shall not be destroyed out of Israel.
Suka ce, “Dole mutanen Benyamin da suka ragu su sami gādo, domin kada wata kabila a Isra’ila ta ɓace.
18 For we shall not be able to give them wives of our daughters, because we swore among the children of Israel, saying, Cursed [is] he that gives a wife to Benjamin.
Ba za mu iya ba su’yan matanmu su zama matansu ba, da yake mu Isra’ilawa mun riga mun yi wannan rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne wanda ya ba da’yarsa aure ga mutum Benyamin.’
19 And they said, Behold! now [there is] a feast of the Lord from year to year in Selom, which is on the north of Baethel, eastward on the way that goes up from Baethel to Sychem, and from the south of Lebona.
Sai suka tuna, akwai bikin Ubangiji da sukan yi shekara-shekara a Shilo ya yi kusa. Shilo yana arewancin Betel, kudu da Lebona, gabas da hanyar da take tsakanin Betel da Shekem.”
20 And they charged the children of Benjamin, saying, Go and lie in wait in the vineyards;
Saboda haka suka cewa mutanen Benyamin, “Ku je ku ɓuya a gonakin inabi
21 and you shall see; and behold! if there come out the daughters of the inhabitants of Selom to dance in dances, then shall you go out of the vineyards and seize for yourselves every man a wife of the daughters of Selom, and go you into the land of Benjamin.
ku lura. Sa’ad da’yan matan Shilo suka fito waje don su yi rawa, ku fito a guje daga gonakin inabi, kowannenku yă kama wa kansa mata daga cikin’yan matan Shilo, ku tafi ƙasar Benyamin.
22 And it shall come to pass, when their fathers or their brethren come to dispute with us, that we will say to them, Grant them freely to us, for we have not taken every man his wife in the battle: because you did not give to them according to the occasion, you transgressed.
Sa’ad da iyayensu maza ko’yan’uwansu suka kawo mana ƙara, za mu ce musu, ‘Ku yi mana alheri ku bar su, domin ba mu samo musu mata ba lokacin yaƙi, ku kuma marasa laifi ne, tun da yake ba ku ba da’ya’yan matanku gare su ba.’”
23 And the children of Benjamin did so; and they took wives according to their number from the dancers whom they seized: and they went and returned to their inheritance, and built the cities, and lived in them.
Haka mutanen Benyamin suka yi. Yayinda’yan matan suke rawa, kowane mutum ya kama ɗaya ya yi gaba da ita ta zama matarsa. Sa’an nan suka komo ƙasar gādonsu suka sāke giggina garuruwan suka kuwa zauna a cikinsu.
24 And the children of Israel went thence at that time every man to his tribe and his kindred; and they went thence every man to his inheritance.
A lokacin, Isra’ilawa sun bar wurin suka tafi gida zuwa ga kabilansu da zuriyoyinsu, kowane zuwa gādonsa.
25 And in those days there was no king in Israel; every man did that which was right in his own sight.
A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa ya yi abin da ya ga dama.

< Judges 21 >