< Judges 17 >

1 And there was a man of mount Ephraim, and his name was Michaias.
To, wani mutum mai suna Mika daga ƙasar tudu ta Efraim
2 And he said to his mother, The eleven hundred pieces of silver which you took of yourself, and [about which] you cursed me, and spoke in my ears, behold, the silver [is] with me; I took it: and his mother said, Blessed [be] my son of the Lord.
ya ce wa mahaifiyarsa, “Shekel dubu ɗaya da ɗari ɗaya na azurfa da aka ɗauka daga gare ki wanda kuma ji kin furta la’ana a kai, azurfan yana wurina; ni ne na ɗauka.” Sa’an nan mahaifiyarsa ta ce, “Ubangiji yă albarkace ka ɗana!”
3 And he restored the eleven hundred pieces of silver to his mother; and his mother said, I had wholly consecrated the money to the Lord out of my hand for my son, to make a graven and a molten [image], and now I will restore it to you.
Sa’ad da ya mayar da azurfa dubu ɗaya da ɗari ɗaya na shekel wa mahaifiyarsa, sai ta ce, “Na ba da azurfata ga Ubangiji don ɗana yă sassaƙa sura yă kuma yi zubin gunki. Zan mayar maka.”
4 But he returned the silver to his mother, and his mother took two hundred pieces of silver, and gave them to a silversmith, and he made it a graven and a molten image; and it was in the house of Michaias.
Saboda haka ya mayar da azurfan wa mahaifiyarsa, ita kuwa ta ɗauki azurfa ɗari biyu na shekel ta ba wa maƙeri, wanda ya mai da su sura da kuma gunki. Aka kuwa sa su a gidan Mika.
5 And the house of Michaias [was] to him the house of God, and he made an ephod and theraphin, and he consecrated one of his sons, and he became to him a priest.
To, wannan mutum Mika yana da ɗakin gumaka, ya yi efod da waɗansu gumaka, ya kuma naɗa ɗaya daga cikin’ya’yansa firist nasa.
6 And in those days there was no king in Israel; every man did that which was right in his own eyes.
A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa yana yin abin da ya ga dama.
7 And there was a young man in Bethleem of the tribe of Juda, and he [was] a Levite, and he was sojourning there.
Wani saurayi Balawe daga Betlehem a Yahuda, wanda yake zama cikin zuriyar Yahuda,
8 And the man departed from Bethleem the city of Juda to sojourn in whatever place he might find; and he came as far as mount Ephraim, and to the house of Michaias to accomplish his journey.
ya bar garin ya tafi neman inda zai zauna. A hanyarsa ya zo gidan Mika a ƙasar tudu ta Efraim.
9 And Michaias said to him, Whence come you? and he said to him, I am a Levite of Bethleem Juda, and I go to sojourn in any place I may find.
Mika ya ce masa, “Daga ina kake?” Ya ce, “Ni Balawe ne daga Betlehem a Yahuda, ina kuwa neman wurin zauna ne.”
10 And Michaias said to him, Dwell with me, and be to me a father and a priest; and I will give you ten pieces of silver by the year, and a change of raiment, and your living.
Sa’an nan Mika ya ce masa, “Ka zauna tare da ni ka zama mini mahaifi da firist, zan kuwa ba ka azurfa goma na shekel a shekara, tufafinka da kuma abincinka.” Sai Balawen ya tafi.
11 And the Levite went and began to dwell with the man; and the young man was to him as one of his sons.
Saboda haka Balawen ya yarda ya zauna tare da shi, ɗan saurayin kuwa ya zama kamar ɗaya daga cikin’ya’yansa.
12 And Michaias consecrated the Levite, and he became to him a priest, and he was in the house of Michaias.
Sa’an nan Mika ya naɗa Balawen, saurayin kuwa ya zama masa firist ya kuma zauna a gidansa.
13 And Michaias said, Now I know that the Lord will do me good, because a Levite has become my priest.
Mika ya ce, “Yanzu na san cewa Ubangiji zai yi mini alheri, da yake Balawen nan ya zama firist nawa.”

< Judges 17 >