< Joshua 19 >

1 And the second lot came out for the children of Symeon; and their inheritance was in the midst of the lots of the children of Juda.
Ƙuri’a ta biyu ta fāɗa a kan kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu. Ƙasarsu ta gādo tana cikin yankin Yahuda.
2 And their lot was Beersabee, and Samaa, and Caladam,
Waɗannan su ne wuraren da suka gāda. Beyersheba (ko Sheba), Molada,
3 and Arsola, and Bola, and Jason,
Hazar Shuwal, Bilha, Ezem,
4 and Erthula, and Bula, and Herma,
Eltolad, Betul, Horma,
5 and Sikelac, and Baethmachereb, and Sarsusin,
Ziklag, Bet-Markabot, Hazar-Susa,
6 and Batharoth, and their fields, thirteen cities, and their villages.
Bet-Lebayot da Sharuhen, garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu.
7 Eremmon, and Thalcha, and Jether, and Asan; four cities and their villages,
Akwai kuma Ayin, Rimmon, Eter da Ashan, garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu,
8 round about their cities as far as Balec as [men] go to Bameth southward: this [is] the inheritance of the tribe of the children of Symeon according to their families.
da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da garuruwan nan har zuwa Rama na Negeb (wato, Ba’alat-Beyer). Wannan shi ne gādon kabilar Simeyon bisa ga iyalansu.
9 The inheritance of the tribe of the children of Symeon [was a part] of the lot of Juda, for the portion of the children of Juda was greater than theirs; and the children of Symeon inherited in the midst of their lot.
Daga cikin gādon mutanen Yahuda ne aka fitar da gādon kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu, domin rabon da kabilar Yahuda suka samu ya fi ƙarfin abin da suke bukata. Saboda haka kabilar gādon Simeyon yana cikin harabar Yahuda.
10 And the third lot came out to Zabulon according to their families: the bounds of their inheritance shall be—Esedekgola shall be their border,
Ƙuri’a ta uku ta fāɗa a kan Zebulun bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kai har Sarid.
11 the sea and Magelda, and it shall reach to Baetharaba in the valley, which is opposite Jekman.
Ta nufi yamma zuwa Marala, ta taɓa Dabbeshet, ta wuce zuwa rafin da yake kusa da Yokneyam.
12 And the border returned from Sedduc in a contrary direction eastward from Baethsamys, to the borders of Chaselothaith, and shall pass on to Dabiroth, and shall proceed upward to Phangai.
Daga Sarid, ta juya gabas zuwa harabar Kislot Tabor, ta kuma wuce zuwa Daberat har zuwa Yafiya.
13 And thence it shall come round in the opposite direction eastward to Gebere to the city of Catasem, and shall go on to Remmonaa Matharaoza.
Sa’an nan ta ci gaba, ta yi gabas zuwa Gat-Hefer da Et Kazin; ta ɓulla a Rimmon, ta juya zuwa Neya.
14 And the borders shall come round northward to Amoth, and their going out shall be at Gaephael,
A can ne iyakar ta kewaya zuwa Hannaton, sa’an nan ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.
15 and Catanath, and Nabaal, and Symoon, and Jericho, and Baethman.
Zebulun ta ƙunshi garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu. Garuruwan sun haɗa da Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem.
16 This [is] the inheritance of the tribe of the sons of Zabulon according to their families, [these] cities and their villages.
Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Zebulun ta samu, bisa ga iyalansu.
17 And the fourth lot came out to Issachar.
Ƙuri’a ta huɗu ta fāɗa a kan kabilar Issakar, bisa ga iyalansu.
18 And their borders were Jazel, and Chasaloth, and Sunam,
Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Yezireyel, Kessulot, Shunem,
19 and Agin, and Siona, and Reeroth,
Hafarayim, Anaharat,
20 and Anachereth, and Dabiron, and Kison, and Rebes,
Rabbat, Kishiyon, Ebez,
21 and Remmas, and Jeon, and Tomman, and Aemarec, and Bersaphes.
Remet, En Gannim, En Hadda da Bet-Fazez.
22 And the boundaries shall border upon Gaethbor, and upon Salim westward, and Baethsamys; and the extremity of his bounds shall be Jordan.
Iyakar ta taɓa Tabor Shahazuma da Bet-Shemesh ta kuma ƙarasa a Urdun. Duka-duka garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
23 This [is] the inheritance of the tribe of the children of Issachar according to their families, the cities and their villages.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Issakar ta samu, bisa ga iyalansu.
24 And the fifth lot came out to Aser according to their families.
Ƙuri’a ta biyar ta fāɗa a kan kabilar Asher, bisa ga iyalansu.
25 And their borders were Exeleketh, and Aleph, and Baethok, and Keaph,
Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Helkat, Hali, Beten, Akshaf,
26 and Elimelech, and Amiel, and Maasa, and the lot will border on Carmel westward, and on Sion, and Labanath.
Allammelek, Amad da Mishal. A arewanci kuma iyakar ta taɓa Karmel da Shihor Libnat.
27 And it will return westward from Baethegeneth, and will join Zabulon and Ekgai, and Phthaeel northwards, and the borders will come to Saphthaebaethme, and Inael, and will go on to Chobamasomel,
Sai ta yi gabas zuwa Bet-Dagon, ta taɓa Zebulun da kuma Kwarin Ifta El, ta wuce arewa zuwa Bet-Emek da Neyiyel, ta wuce Kabul a hagu,
28 and Elbon, and Raab, and Ememaon, and Canthan to great Sidon.
ta kai Abdon, Rehob, Hammon da Kana, har zuwa Sidon Babba.
29 And the borders shall turn back to Rama, and to the fountain of Masphassat, and the Tyrians; and the borders shall return to Jasiph, and their going forth shall be the sea, and Apoleb, and Echozob,
Daga nan iyakar ta juya baya zuwa Rama, ta bi ta birnin nan mai katanga na Taya, ta juya ta nufi Hosa, sa’an nan ta ɓulla ta Bahar Rum cikin yankin Akzib,
30 and Archob, and Aphec, and Raau.
Umma, Afek da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.
31 This [is] the inheritance of the tribe of the sons of Aser according to their families, the cities and their villages.
Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Asher ta samu bisa ga iyalansu.
32 And the sixth lot came out to Nephthali.
Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.
33 And their borders were Moolam, and Mola, and Besemiin, and Arme, and Naboc, and Jephthamai, as far as Dodam; and their goings out were Jordan.
Iyakarsu ta kama daga Helef, daga babban itacen Mamre nan da yake a Za’anannim, ta wuce Adami Nekeb da Yabneyel zuwa Lakkum, ta kuma ƙarasa a Urdun.
34 And the coasts will return westward by Athabor, and will go out thence to Jacana, and will border on Zabulon southward, and Aser will join [it] westward, and Jordan eastward.
Iyakar kuma ta juya yamma ta cikin Aznot-Tabo ta ɓulla a Hukkok. Ta taɓa Zebulun a kudu, Asher a yamma, da kuma Urdun a gabas.
35 And the walled cities of the Tyrians, Tyre, and Omathadaketh, and Kenereth,
Biranen da suke da katanga su ne Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,
36 and Armaith, and Areal, and Asor,
Adama, Rama, Hazor,
37 and Cades, and Assari, and the well of Asor;
Kedesh, Edireyi, En Hazor,
38 and Keroe, and Megalaarim, and Baetthame, and Thessamys.
Yiron, Migdal El, Horem, Bet-Anat da Bet-Shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.
39 This [is] the inheritance of the tribe of the children of Nephthali.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.
40 And the seventh lot came out to Dan.
Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
41 And their borders were Sarath, and Asa, and the cities of Sammaus,
Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,
42 and Salamin, and Ammon, and Silatha,
Shalim, Aiyalon, Itla,
43 and Elon, and Thamnatha, and Accaron;
Elon, Timna, Ekron,
44 and Alcatha, and Begethon, and Gebeelan,
Elteke, Gibbeton, Ba’alat,
45 and Azor, and Banaebacat, and Gethremmon.
Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,
46 And westward of Hieracon the border [was] near to Joppa.
Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.
47 This [is] the inheritance of the tribe of the children of Dan, according to their families, these [are] their cities and their villages: and the children of Dan did not drive out the Amorite who afflicted them in the mountain; and the Amorite would not suffer them to come down into the valley, but they forcibly took from them the border of their portion.
(Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
48 And the sons of Dan went and fought against Lachis, and took it, and struck it with the edge of the sword; and they lived in it, and called the name of it Lasendan: and the Amorite continued to dwell in Edom and in Salamin: and the hand of Ephraim prevailed against them, and they became tribute to them.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
49 And they proceeded to take possession of the land according to their borders, and the children of Israel gave an inheritance to Joshua the son of Naue among them,
Sa’ad da aka gama raba gādon ƙasar bisa ga ƙuri’a. Sai Isra’ilawa suka ba Yoshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikinsu,
50 by the command of God, and they gave him the city which he asked for, Thamnasarach, which is in the mount of Ephraim; and he built the city, and lived in it.
yadda Ubangiji ya umarta, suka ba shi garin da ya ce a ba shi, Timnat Serad a ƙasar tudu ta Efraim. Ya kuma gina garin ya zauna a can.
51 These [are] the divisions which Eleazar the priest divided by lot, and Joshua the [son] of Naue, and the heads of families among the tribes of Israel, according to the lots, in Selo before the Lord by the doors of the tabernacle of testimony, and they went to take possession of the land.
Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin kabilan iyalan Isra’ila suka rarraba ta hanyar jefa ƙuri’a a Shilo a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. Da haka suka yi suka gama rarraba ƙasar.

< Joshua 19 >