< Job 37 >

1 At this also my heart is troubled, and moved out of its place.
“Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
2 Hear you a report by the anger of the Lord's wrath, and a discourse shall come out of his mouth.
Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
3 His dominion is under the whole heaven, and his light is at the extremities of the earth.
Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
4 After him shall be a cry with a [loud] voice; he shall thunder with the voice of his excellency, yet he shall not cause men to pass away, for one shall hear his voice.
Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
5 The Mighty One shall thunder wonderfully with his voice: for he has done great things which we knew not;
Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
6 commanding the snow, Be you upon the earth, and the stormy rain, and the storm of the showers of his might.
Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
7 He seals up the hand of every man, that every man may know his own weakness.
Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
8 And the wild beasts come in under the covert, and rest in [their] lair.
Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
9 Troubles come on out of the secret chambers, and cold from the mountain-tops.
Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
10 And from the breath of the Mighty One he will send frost; and he guides the water in whatever way he pleases.
Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
11 And [if] a cloud obscures [what is] precious [to him], his light will disperse the cloud.
Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
12 And he will carry round the encircling [clouds] by his governance, to [perform] their works: whatever he shall command them,
Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
13 this has been appointed by him on the earth, whether for correction, [or] for his land, or if he shall find him [an object] for mercy.
Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
14 Listen to this, O Job: stand still, and be admonished of the power of the Lord.
“Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
15 We know that god has disposed his works, having made light out of darkness.
Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
16 And he knows the divisions of the clouds, and the signal overthrows of the ungodly.
Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
17 But your robe is warm, and there is quiet upon the land.
Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
18 Will you establish with him [foundations] for the ancient [heavens? they are] strong as a molten mirror.
ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
19 Therefore teach me, what shall we say to him? and let us cease from saying much.
“Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
20 Have I a book or a scribe my me, that I may stand and put man to silence?
Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
21 But the light is not visible to all: it shines afar off in the heavens, as that which is from him in the clouds.
Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
22 From the [north] come the clouds shining like gold: in these great are the glory and honor of the Almighty;
Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
23 and we do not find another his equal in strength: [as for] him that judges justly, do you not think that he listens?
Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
24 Therefore men shall fear him; and the wise also in heart shall fear him.
Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”

< Job 37 >