< Job 35 >
1 And Elius resumed and said,
Sai Elihu ya ce,
2 What is this that you think to be according to right? who are you that you have said, I am righteous before the Lord?
“Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
3 I will answer you, and your three friends.
Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
4 Look up to the sky and see; and consider the clouds, how high [they are] above you.
“Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
5 If you have sinned, what will you do?
Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
6 and if too you have transgressed much, what can you perform?
In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
7 And suppose you are righteous, what will you give him? or what shall he receive of your hand?
In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
8 Your ungodliness [may affect] a man who is like to you; or your righteousness a son of man.
Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
9 They that are oppressed of a multitude will be ready to cry out; they will call for help because of the arm of many.
“Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
10 But none said, Where is God that made me, who appoints the night-watches;
Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
11 who makes me to differ from the four-footed beasts of the earth, and from the birds of the sky?
wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
12 There they shall cry, and none shall listen, even because of the insolence of wicked men.
Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
13 For the Lord desires not to look on error, for he is the Almighty One.
Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
14 He beholds them that perform lawless deeds, and he will save me: and do you plead before him, if you can praise him, as it is [possible] even now.
Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
15 For he is not [now] regarding his wrath, nor has he noticed severely any trespass.
Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
16 Yet Job vainly opens his mouth, in ignorance he multiplies words.
Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”