< Job 11 >

1 Then Sophar the Minaean answered and said,
Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 He that speaks much, should also hear on the other side: or does the fluent speaker think himself to be righteous? blessed [is] the short lived offspring of woman.
“Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
3 Be not a speaker of many words; for is there none to answer you?
Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
4 For say not, I am pure in my works, and blameless before him.
Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
5 But oh that the Lord would speak to you, and open his lips to you!
Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
6 Then shall he declare to you the power of wisdom; for it shall be double of that which is with you: and then shall you know, that a just recompence of your sins has come to you from the Lord.
yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
7 Will you find out the traces of the Lord? or have you come to the end [of that] which the Almighty has made?
“Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
8 Heaven [is] high; and what will you do? and there are deeper things than those in hell; what do you know? (Sheol h7585)
Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
9 Or longer than the measure of the earth, or the breadth of the sea.
Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
10 And if he should overthrow all things, who will say to him, What have you done?
“In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
11 For he knows the works of transgressors; and when he sees wickedness, he will not overlook [it].
Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
12 But man vainly buoys himself up with words; and a mortal born of woman [is] like an ass in the desert.
Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
13 For if you have made your heart pure, and lift up [your] hands towards him;
“Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
14 if there is any iniquity in your hands, put if far from you, and let not unrighteousness lodge in your habitation.
in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
15 For thus shall your countenance shine again, as pure water; and you shall dive yourself of uncleanness, and shall not fear.
shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
16 And you shall forget trouble, as a wave that has passed by; and you shall not be scared.
Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
17 And your prayer [shall be] as the morning star, and life shall arise to you [as] from the noonday.
Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
18 And you shall be confident, because you have hope; and peace shall dawn to you from out of anxiety and care.
Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
19 For you shall be at ease, and there shall be no one to fight against you; and many shall charge, and make supplication to you.
Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
20 But safety shall fail them; for their hope is destruction, and the eyes of the ungodly shall waste away.
Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”

< Job 11 >