< Jeremias 2 >

1 And he said, Thus says the Lord,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 I remember the kindness of your youth, and the love of your espousals,
“Tafi ka yi shela a kunnuwar Urushalima cewa, “‘Na tuna da amincin ƙuruciyarki, yadda kamar amarya kika ƙaunace ni kika kuma bi ni cikin hamada, cikin ƙasar da ba a yi shuka ba.
3 in following the Holy One of Israel, says the Lord, Israel was the holy [people] to the Lord, [and] the first fruits of his increase: all that devoured him shall offend; evils shall come upon them, says the Lord.
Isra’ila tsattsarka ce ga Ubangiji, nunan fari na girbinsa; dukan waɗanda suka cinye ta an same su da laifi, masifa kuwa ta same su,’” in ji Ubangiji.
4 Hear the word of the Lord, O house of Jacob, and every family of the house of Israel.
Ka saurari maganar Ubangiji, ya gidan Yaƙub, dukanku zuriyar gidan Isra’ila.
5 Thus says the Lord, What trespass have your fathers found in me, that they have revolted far from me, and gone after vanities, and become vain?
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Wane laifi ne kakanninku sun same ni da shi, da suka tsaya nesa da ni? Sun bi gumakan banza su kansu suka kuma zama banza da kansu.
6 And they said not, Where is the Lord, who brought us up out of the land of Egypt, who guided us in the wilderness, in an untried and trackless land, in a land which no man at all went through, and no man lived there?
Ba su yi tambaya, ‘Ina Ubangiji, wanda ya fitar da su daga Masar ya bishe su cikin jeji cikin hamada da kwazazzabai ƙasa mai fări da kuma duhu, ƙasar da ba kowa mai ratsa ta ba kowa kuma mai zama a cikinta?’
7 And I brought you to Carmel, that you should eat the fruits thereof, and the good thereof; and you went in, and defiled my land, and made mine heritage an abomination.
Na kawo ku zuwa ƙasa mai albarka don ku ci amfaninta da abubuwa masu yalwar da take bayarwa. Amma kuka zo kuka ƙazantar da ƙasata kuka kuma mai da gādona abin ƙyama.
8 The priests said not, Where is the Lord? and they that held by the law knew me not: the shepherds also sinned against me, and the prophets prophesied by Baal, and went after that which profited not.
Firistoci ba su yi tambaya, ‘Ina Ubangiji ba.’ Waɗanda suke amfani da doka ba su san ni ba; shugabanni suka yi mini tawaye. Annabawa suka yi annabci ta wurin Ba’al, suna bin gumakan banza.
9 Therefore I will yet plead with you, and will plead with your children's children.
“Saboda haka ina sāke tuhumarku,” in ji Ubangiji. “Zan kuma tuhumi’ya’ya’ya’yanku.
10 For go to the isles of the Chettians, and se; and send to Kedar, and observe accurately, and see if such things have been done;
Ku ƙetare zuwa tsibiran Kittim ku gani, ku aika zuwa Kedar ku duba da kyau; ku ga ko an taɓa yin wani abu haka.
11 if the nations will change their gods, though they are not gods: but my people have changed their glory, [for that] from which they shall not be profited.
Akwai wata al’ummar da ta canja allolinta? (Duk da haka su ba alloli ba ne sam.) Amma mutanena sun musayar da ɗaukakarsu da gumakan banza.
12 The heaven is amazed at this, and is very exceedingly horror-struck, says the Lord.
Ku girgiza saboda wannan, ya sammai, ku kuma razana don tsoro mai girma,” in ji Ubangiji.
13 For my people has committed two [faults], and evil ones: they have forsaken me, the fountain of water of life, and hewn out for themselves broken cisterns, which will not be able to hold water.
“Mutanena sun aikata zunubai guda biyu. Sun rabu da ni, ni da nake maɓulɓular ruwan rai, sun kuma haƙa tankunan ruwansu, tankuna ruwan da suka fashe da ba za su iya riƙe ruwa ba.
14 Is Israel a servant, or a home-born slave? why has he become a spoil?
Isra’ila bawa ne, bawa ne ta wurin haihuwa? Me ya sa ya zama ganima?
15 The lions roared upon him, and uttered their voice, which have made his land a wilderness: and his cities are broken down, that they should not be inhabited.
Zakoki sun yi ruri; sun yi masa ruri. Sun lalatar da ƙasarsa; an ƙone garuruwansa aka kuma watse daga ciki.
16 Also the children of Memphis and Taphnas have known you, and mocked you.
Haka ma, mutanen Memfis da Tafanes sun aske rawanin kanka
17 Has not your forsaking me brought these things upon you? says the Lord your God.
Ba kai ne ba ka jawo wa kanka ba ta wurin rabuwa da Ubangiji Allahnka sa’ad da ya bi da kai a hanya?
18 And now what have you to do with the way of Egypt, to drink the water of Geon? and what have you to do with the way of the Assyrians, to drink the water of rivers?
To, me ya sa za ka Masar don shan ruwa daga Shihor? Kuma me ya sa za ka Assuriya don shan ruwa daga Kogi?
19 Your apostasy shall correct you, and your wickedness shall reprove you: know then, and see, that your forsaking me [has been] bitter to you, says the Lord your God; and I have taken no pleasure in you, says the Lord your God.
Muguntarka za tă hukunta ka; jan bayanka zai tsawata maka. Sai ka lura ka kuma gane yaya mugu da kuma ɗaci suke a gare ka sa’ad da ka rabu da Ubangiji Allahnka kuma ba ka tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
20 For of old you have broken your yoke, and plucked asunder your bands; and you has said, I will not serve you, but will go upon every high hill, and under every shady tree, there will I indulge in my fornication.
“Tun da daɗewa ka karya karkiyarka ka kuma tsintsinke sarƙoƙinka; sai ka ce, ‘Ba zan bauta maka ba!’ Tabbatacce, a kan kowane tudu mai tsayi da kuma a ƙarƙashin kowane ɗanyen itace ka kwanta kamar karuwa.
21 Yet I planted you a fruitful vine, entirely of the right sort: how are you a strange vine turned to bitterness!
Na shuka ka kamar zaɓaɓɓen inabi iri mai kyau da kuma wanda za a dogara a kai. Yaya kuma ka juya kana gāba da ni ka lalace, ka zama inabin jeji?
22 Though you should wash yourself with nitre, and multiply to yourself soap, [still] you are stained by your iniquities before me, says the Lord.
Ko da yake ka wanke kanka da sabulu ka yi amfani da sabulu mai yawa, duk da haka har yanzu tabon laifinka yana nan a gabana,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
23 How will you say, I am not polluted, and have not gone after Baal? behold your ways in the burial-ground, and know what you have done: her voice has howled in the evening:
“Yaya za ka ce, ‘Ban ƙazantu ba; ban bi Ba’al ba’? Duba yadda ka yi a cikin kwari; ka ga abin da ka yi. Kai kamar makwaɗaciyar raƙuma ce mai zafin gudu kana gudu nan da can,
24 she has extended her ways over the waters of the desert; she was hurried along by the lusts of her soul; she is given up [to them], who will turn her back? none that seek her shall be weary; at [the time of] her humiliation they shall find her.
kamar jakar jejin da ta saba da hamada, mai busar iska cikin son barbaranta sa’ad da take son barbara wa zai iya hana ta? Jakin da yake nemanta, ba ya bukatar wahalar da kansa; a lokacin barbara za a same ta.
25 Withdraw your foot from a rough way, and your throat from thirst: but she said I will strengthen myself: for she loved strangers, and went after them.
Kada ka yi gudu har ƙafafunka su zama ba takalma maƙogwaronka kuma ya bushe. Amma sai ka ce, ‘Ba amfani! Ina ƙaunar baƙin alloli kuma dole in bi su.’
26 As is the shame of a thief when he is caught, so shall the children of Israel be ashamed; they, and their kings, and their princes, and their priests, and their prophets.
“Kamar yadda akan kunyatar da ɓarawo sa’ad da aka kama shi, haka gidan Isra’ila zai sha kunya, su, sarakunansu da shugabanninsu, firistocinsu da kuma annabawansu.
27 They said to a stock, You are my father; and to a stone, You has begotten me: and they have turned [their] backs to me, and not their faces: yet in the time of their afflictions they will say, Arise, and save us.
Kuna ce wa itace, ‘Kai ne mahaifina,’ ga dutse kuma, ‘Kai ne ka haife ni.’ Sun juye mini bayansu ba fuskokinsu ba; duk da haka sa’ad da suna cikin wahala, sukan ce, ‘Zo ka cece mu!’
28 And where are your gods, which you made for yourself? will they arise and save in the time of your affliction? for according to the number of your cities were your gods, O Juda; and according to the number of the streets of Jerusalem they sacrificed to Baal.
To ina allolin da kuka yi wa kanku? Bari su zo in suna iya cetonku sa’ad da kuke cikin wahala! Gama kuna da alloli masu yawa kamar yadda kuke da garuruwa, ya Yahuda.
29 Therefore do you speak to me? you all have been ungodly, and you all have transgressed against me, says the Lord.
“Me ya sa kuke tuhumana? Dukanku kun yi mini tawaye,” in ji Ubangiji.
30 In vain have I struck your children; you have not received correction: a sword has devoured your prophets as a destroying lion; yet you feared not.
“A banza na hukunta mutanenku; ba su yi gyara ba. Takobinku ya cinye annabawanku kamar zaki mai jin yunwa.
31 Hear you the word of the Lord: thus says the Lord, Have I been a wilderness or a dry land to Israel? therefore has my people said, We will not be ruled over, and will not come to you any more?
“Ku na wannan zamani, ku saurari maganar Ubangiji. “Na zama wa Isra’ila hamada ne ko ƙasa mai babban duhu? Me ya sa mutanena suke cewa, ‘Muna da’yanci mu yi ta yawo; ba za mu ƙara zuwa wurinka ba’?
32 Will a bride forget her ornaments, or a virgin her girdle? but my people has forgotten me days without number.
Budurwa za tă manta da kayan adonta amarya ta manta da kayan adon aurenta? Duk da haka mutanena sun manta da ni, kwanaki ba iyaka.
33 What fair device will you yet employ in your ways, so as to seek love? [it shall] not [be] so; moreover you has done wickedly in corrupting your ways;
Kuna da azanci sosai a bin masoya! Kai, ko mafiya muni cikin mata tana iya koya daga hanyoyinku.
34 and in your hands has been found the blood of innocent souls; I have not found them in holes, but on every oak.
A rigunanku mutane kan sami jinin matalauta marasa laifi, ko da yake ba ku kama su suna fasawa su shiga ba. Duk da haka
35 Yet you said, I am innocent: only let his wrath be turned away from me. Behold, I [will] plead with you, whereas you say, I have not sinned.
kuna cewa, ‘Ba ni da laifi; ba ya fushi da ni.’ Amma zan zartar da hukunci a kanku domin kun ce, ‘Ban yi zunubi ba.’
36 For you has been so exceedingly contemptuous as to repeat your ways; but you shall be ashamed of Egypt, as you were ashamed of Assur.
Don me kuke yawo da yawa haka, kuna ta canjin hanyoyinku? Masar za tă kunyata ku yadda kuka sha kunya a wurin Assuriya.
37 For you shall go forth thence also with your hands upon your head; for the Lord has rejected your hope, and you shall not prosper in it.
Za ku kuma bar wurin da hannuwanku a kanku, gama Ubangiji ya ƙi waɗanda kuka amince da su; ba za ku zama abin taimako a gare su ba.

< Jeremias 2 >