< Esias 1 >

1 The vision which Esaias the son of Amos saw, which he saw against Juda, and against Jerusalem, in the reign of Ozias, and Joatham, and Achaz, and Ezekias, who reigned over Judea.
Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
2 Hear, O heaven, and listen, O earth: for the Lord has spoken, [saying], I have begotten and reared up children, but they have rebelled against me.
Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
3 The ox knows his owner, and the ass his master's crib: but Israel does not know me, and the people has not regarded me.
Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
4 Ah sinful nation, a people full of sins, an evil seed, lawless children: you have forsaken the Lord, and provoked the Holy One of Israel.
Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
5 Why should you be struck [any] more, transgressing more and more? the whole head is pained, and the whole heart sad.
Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
6 From the feet to the head, there is no soundness in them; neither wound, nor bruise, nor festering ulcer [are healed]: it is not possible to apply a plaister, nor oil, nor bandages.
Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
7 Your land is desolate, your cities burned with fire: your land, strangers devour it in your presence, and it is made desolate, overthrown by strange nations.
Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
8 The daughter of Sion shall be deserted as a tent in a vineyard, and as a storehouse of fruits in a garden of cucumbers, as a besieged city.
An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
9 And if the Lord of Sabaoth had not left us a seed, we should have been as Sodom, and we should have been made like Gomorrha.
Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
10 Hear the word of the Lord, you rulers of Sodoma; attend to the law of God, you people of Gomorrha.
Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
11 Of what [value] to me is the abundance of your sacrifices? says the Lord: I am full of whole burnt offerings of rams; and I delight not in the fat of lambs, and the blood of bulls and goats:
Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
12 neither shall you come [with these] to appear before me; for who has required these things at your hands? You shall no more tread my court.
Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
13 Though you bring fine flour, [it is] vain; incense is an abomination to me; I can’t bear your new moons, and your sabbaths, and the great day;
Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
14 [your] fasting, and rest from work, your new moons also, and your feasts my soul hates: you have become loathsome to me; I will no more pardon your sins.
Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
15 When you stretch forth your hands, I will turn away mine eyes from you: and though you make many supplications, I will not listen to you; for your hands are full of blood.
Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
16 Wash you, be clean; remove your iniquities from your souls before mine eyes; cease from your iniquities;
Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
17 learn to do well; diligently seek judgment, deliver him that is suffering wrong, plead for the orphan, and obtain justice for the widow.
Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
18 And come, let us reason together, says the Lord: and though your sins be as purple, I will make them white as snow; and though they be as scarlet, I will make [them] white as wool.
Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
19 And if you be willing, and listen to me, you shall eat the good of the land:
In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
20 but if you be not willing, nor listen to me, a sword shall devour you: for the mouth of the Lord has spoken this.
amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
21 How has the faithful city Sion, [once] full of judgment, become a harlot! wherein righteousness lodged, but now murderers.
Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
22 Your silver is worthless, your wine merchants mix the wine with water.
Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
23 Your princes are rebellious, companions of thieves, loving bribes, seeking after rewards; not pleading for orphans, and not heeding the cause of widows.
Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
24 Therefore thus says the Lord, the Lord of hosts, Woe to the mighty [men] of Israel; for my wrath shall not cease against mine adversaries, and I will execute judgment on mine enemies.
Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
25 And I will bring my hand upon you, and purge you completely, and I will destroy the rebellious, and will take away from you all transgressors.
Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
26 And I will establish your judges as before, and your counselors as at the beginning: and afterward you shall be called the city of righteousness, the faithful mother-city of Sion.
Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
27 For her captives shall be saved with judgment, and with mercy.
Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
28 And the transgressors and the sinners shall be crushed together, and they that forsake the Lord shall be utterly consumed.
Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
29 For they shall be ashamed of their idols, which they delighted in, and they are made ashamed of the gardens which they coveted.
“Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
30 For they shall be as a turpentine tree that has cast its leaves, and as a garden that has no water.
Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
31 And their strength shall be as a thread of tow, and their works as sparks, and the transgressors and the sinners shall be burnt up together, and there shall be none to quench [them].
Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”

< Esias 1 >