< Esias 62 >
1 For Sion's sake I will not hold my peace, and for Jerusalem's sake I will not rest, until her righteousness go forth as light, and my salvation burn as a torch.
Saboda Sihiyona ba zan yi shiru ba, saboda Urushalima ba zan huta ba, sai adalcinta ya haskaka kamar hasken safiya, cetonta kuma ya haskaka kamar fitila mai haske.
2 And the Gentiles shall see your righteousness, and kings your glory: and one shall call you [by] a new name, which the Lord shall name.
Al’ummai za su ga adalcinki, sarakuna kuma za su ga ɗaukakarki; za a kira ki da sabon suna sunan da bakin Ubangiji zai ambata.
3 And you shall be a crown of beauty in the hand of the Lord, and a royal diadem in the hand of your God.
Za ki zama rawanin daraja a hannun Ubangiji, rawanin sarauta a hannun Allahnki.
4 And you shall no more be called Forsaken; and your land shall no more be called Desert: for you shall be called My Pleasure, and your land Inhabited: for the Lord has taken pleasure in you, and your land shall be inhabited.
Ba za a ƙara ce da ke Yasasshiya ba, ko a kira ƙasarki Kango. Amma za a ce da ke Hefziba ƙasarki kuma Bewula; gama Ubangiji zai ji daɗinki, ƙasarki kuma za tă yi aure.
5 And as a young man lives with a virgin, so shall your sons dwell in [you]: and it shall come to pass [that] as a bridegroom will rejoice over a bride, so will the Lord rejoice over you.
Kamar yadda saurayi kan auri yarinya, haka’ya’yanki maza za su aure ki; kamar kuma yadda ango yakan yi farin ciki da amaryarsa, haka Allahnki zai yi farin ciki da ke.
6 And on your walls, O Jerusalem, have I set watchmen all day and all night, who shall never cease making mention of the Lord.
Na sa matsara a kan katangarki, ya Urushalima; ba za su taɓa yin shiru ba, dare da rana. Ku da kuke kira bisa sunan Ubangiji, kada ku ba kanku hutu,
7 For there is none like you, when he shall have established, and made Jerusalem a praise on the earth.
kuma kada ku ba shi hutu sai ya kafa Urushalima ya kuma mai da ita yabon duniya.
8 For the Lord has sworn by his glory, and by the might of his arm, I will no more give your corn and your provisions to your enemies; nor shall strangers any more drink your wine, for which you has laboured.
Ubangiji ya rantse da hannunsa na dama ta hannunsa kuma mai iko cewa, “Ba zan ƙara ba da hatsinki ya zama abinci ga abokan gābanki ba, baƙi kuma ba za su ƙara shan ruwan inabin wanda kika sha wahala samu ba;
9 But they that have gathered them shall eat them, and they shall praise the Lord; and they that have gathered [the grapes] shall drink thereof in my holy courts.
amma waɗanda suka girbe shi za su ci shi su kuma yabi Ubangiji, waɗanda kuma suka tattara’ya’yan inabi za su sha shi a filayen wurina mai tsarki.”
10 Go through my gates, and make a way for my people; and cast the stones out of the way; lift up a standard for the Gentiles.
Ku wuce, ku wuce ƙofofi! Ku shirya hanya saboda mutane. Ku gina, ku gina babbar hanya! Ku kawar da duwatsu. Ku ɗaga tuta saboda al’ummai.
11 For behold, the Lord has proclaimed to the end of the earth, say you to the daughter of Sion, Behold, your Saviour has come to you, having his reward and his work before his face.
Ubangiji ya yi shela ga iyakokin duniya cewa, “Faɗa wa Diyar Sihiyona, ‘Ga Mai Cetonki yana zuwa! Ga ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa yana raka shi.’”
12 And one shall call them the holy people, the redeemed of the Lord: and you shall be called a city sought out, and not forsaken.
Za a ce da shi Tsattsarkar Mutane, Fansassu na Ubangiji; za a kuma ce da ke Wadda Aka Nema Birnin da Ba Za a Ƙara Yashe ta ba.