< Esias 54 >

1 Rejoice, you barren that bear not; break forth and cry, you that do not travail: for more are the children of the desolate than of her that has a husband: for the Lord has said,
“Ki rera, ya ke bakararriya, ke da ba ki taɓa haihuwa ba; ki ɓarke da waƙa, ki yi sowa don farin ciki, ke da ba ki taɓa naƙuda ba; domin’ya’yan mace mai kaɗaici sun fi na mai miji yawa,” in ji Ubangiji.
2 Enlarge the place of your tent, and of your curtains: fix [the pins], spare not, lengthen your cords, and strengthen your pins;
“Ki fadada wurin tentinki, ki miƙe labulen tentinki da fāɗi, kada ki janye; ƙara tsawon igiyoyinta, ki kuma ƙara ƙarfin turakunta.
3 spread forth [your tent] yet to the right and the left: for your seed shall inherit the Gentiles, and you shall make the desolate cities to be inhabited.
Gama za ki fadada zuwa dama da hagu; zuriyarki za su kori al’ummai su kuma zauna a kufan biranensu.
4 Fear not, because you has been put to shame, neither be confounded, because you was reproached: for you shall forget your former shame, and shall no more at all remember the reproach of your widowhood.
“Kada ki ji tsoro; ba za ki sha kunya ba. Kada ki ji tsoron wulaƙanci, ba za a ƙasƙantar da ke ba. Za ki manta da kunyar ƙuruciyarki ba kuwa za ki tuna da zargin zaman gwauruwarki ba.
5 For [it is] the Lord that made you; the Lord of hosts is his name: and he that delivered you, he is the God of Israel, [and] shall be called [so] by the whole earth.
Gama Mahaliccinki shi ne mijinki, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ne Mai Fansarki; ana ce da shi Allahn dukan duniya.
6 The Lord has not called you as a deserted and faint-hearted woman, nor as a woman hated from [her] youth, says your God.
Ubangiji zai kira sai ka ce ke mace ce da aka yashe ta tana kuma damuwa a ranta, macen da ta yi aure a ƙuruciya, sai kawai aka ƙi ta,” in ji Allahnki.
7 For a little while I left you: but with great mercy will I have compassion upon you.
“Gama a ɗan ƙanƙanen lokaci na rabu da ke, amma da ƙauna mai zurfi zan sāke dawo da ke.
8 In a little wrath I turned away my face from you; but with everlasting mercy will I have compassion upon you, says the Lord that delivers you.
Cikin fushi mai zafi na ɓoye fuskata daga gare ki na ɗan lokaci, amma da madawwamin alheri zan ji tausayinki,” in ji Ubangiji Mai Fansarki.
9 From the time of the water of Noe this is my [purpose]: as I sware to him at that time, [saying] of the earth, I will no more be angry with you, neither when you are threatened,
“A gare ni wannan ya yi kamar kwanakin Nuhu, sa’ad da na rantse cewa ruwan Nuhu ba za su ƙara rufe duniya ba. Yanzu fa na rantse ba zan yi fushi da ke ba, ba zan ƙara tsawata miki kuma ba.
10 shall the mountains depart, nor shall your hills be removed: so neither shall my mercy fail you, nor shall the covenant of your peace be at all removed: for the Lord [who is] gracious to you has spoken [it].
Ko da duwatsu za su girgiza a kuma tumɓuke tuddai, duk da haka madawwamiyar ƙaunata da nake yi miki ba za tă jijjigu ba ba kuwa za a kawar da alkawarin salamata ba,” in ji Ubangiji, wanda ya ji tausayinki.
11 Afflicted and outcast you has not been comforted: behold, I [will] prepare carbuncle [for] your stones, and sapphire for your foundations;
“Ya ke birni mai shan azaba, wadda hadari ya bulale ki ba a kuma ta’azantar da ke ba, zan gina ke da duwatsu turkuwoyis, zan kafa harsashenki da duwatsun saffaya.
12 and I will make your buttresses jasper, and your gates crystal, and your border precious stones.
Zan gina hasumiyarki da jan yakutu, ƙofofinki kuma da duwatsu masu haske, dukan katangarki kuma da duwatsu masu daraja.
13 And [I will cause] all your sons [to be] taught of God, and your children [to be] in great peace.
Ubangiji zai koya wa dukan’ya’yanki maza, da girma kuma salamar’ya’yanki zai zama.
14 And you shall be built in righteousness: abstain from injustice, and you shall not fear; and trembling shall not come near you.
Da adalci za a kafa ke. Zalunci zai yi nesa da ke; ba za ki kasance da wani abin da za ki ji tsoro ba. Za a kawar da duk wani abin banrazana; ba zai yi kusa da ke ba.
15 Behold, strangers shall come to you by me, and shall sojourn with you, and shall run to you for refuge.
In wani ya far miki, ba daga wurina ba ne; duk wanda ya far miki zai miƙa wuya gare ki.
16 Behold, I have created you, not as the coppersmith blowing coals, and bringing out a vessel [fit] for work; but I have created you, not for ruin, that [I] should destroy [you].
“Duba, ni ne wanda na halicci maƙeri wanda yake zuga garwashi ya zama harshen wuta ya kuma ƙera makamin da ya dace da aikinsa. Ni ne kuma na halicci mai hallakarwa ya yi ɓarna;
17 I will not suffer any weapon formed against you to prosper; and every voice that shall rise up against you for judgment, you shall vanquish them all; and your adversaries shall be [condemned] thereby. There is an inheritance to them that serve the Lord, and you shall be righteous before me, says the Lord.
ba makamin da aka ƙera don yă cuce ki da zai yi nasara, za ki kuma mayar da magana ga duk wanda ya zarge ki. Wannan ne gādon bayin Ubangiji, kuma wannan ita ce nasararsu daga gare ni,” in ji Ubangiji.

< Esias 54 >

A Dove is Sent Forth from the Ark
A Dove is Sent Forth from the Ark