< Esias 43 >

1 And now thus says the Lord God that made you, O Jacob, and formed you, O Israel, Fear not: for I have redeemed you, I have called you [by] your name; you are mine.
To, fa, ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicce ka, ya Yaƙub, shi da ya siffanta ka, ya Isra’ila, “Kada ka ji tsoro, gama na fanshe ka; na kira ka da suna; kai nawa ne.
2 And if you pass through water, I am with you; and the rivers shall not overflow you: and if you go through fire, you shall not be burned; the flame shall not burn you.
Sa’ad da kuka bi ta ruwaye, zan kasance tare da ku; sa’ad da kuka bi ta koguna, ba za su kwashe ku ba. Sa’ad da kuke tafiyata cikin wuta, ba za tă ƙone ku ba; harsunan wutar ba za su ƙone ku ba.
3 For I am the Lord your God, the Holy One of Israel, that saves you: I have made Egypt and Ethiopia your ransom, and [given] Soene for you.
Gama ni ne Ubangiji, Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, Mai Cetonku; na bayar da Masar don fansa, Kush da Seba a maimakonku.
4 Since you became precious in my sight, you have become glorious, and I have loved you: and I will give men for you, and princes for your life.
Da yake ku masu daraja da kuma girma ne a idona, saboda kuma ina ƙaunarku, zan ba da mutane a maimakonku, al’umma kuma domin ranku.
5 Fear not; for I am with you: I will bring your seed from the east, and will gather you from the west.
Kada ku ji tsoro, gama ina tare da ku; zan kawo yaranku daga gabas in kuma tattara ku daga yamma.
6 I will say to the north, Bring; and to the south, Keep not back; bring my sons from the [land] afar off, and my daughters from the ends of the earth;
Zan ce wa arewa, ‘Ku miƙa su!’ Ga kudu kuma, ‘Kada ku riƙe su.’ Kawo’ya’yana maza daga nesa’ya’yana mata kuma daga iyakar duniya,
7 [even] all who are called by my name: for I have prepared him for my glory, and I have formed him, and have made him:
kowa da ake kira da sunana, wanda aka halitta saboda ɗaukakata, wanda na siffanta na kuma yi.”
8 and I have brought forth the blind people; for [their] eyes are alike blind, and they that have ears are deaf.
Jagoranci waɗanda suke da idanu amma suke makafi, waɗanda suke da kunnuwa amma suke kurame.
9 All the nations are gathered together, and princes shall be gathered out of them: who will declare these things? or who will declare to you things from the beginning? let them bring forth their witnesses, and be justified; and let them hear, and declare the truth.
Dukan al’ummai su taru mutane kuma su tattaru. Wane ne a cikinsu ya yi faɗar wannan ya kuma yi mana shelar abubuwan da suka riga suka faru? Bari su kawo shaidunsu don su tabbatar cewa sun yi daidai, don waɗansu su ji su kuma ce, “Gaskiya ne.”
10 Be you my witnesses, and I [too am] a witness, says the Lord God, and my servant whom I have chosen: that you may know, and believe, and understand that I am [he]: before me there was no other God, and after me there shall be none.
“Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “bawana kuma wanda na zaɓa, saboda ka sani ka kuma gaskata ni ka kuma fahimci cewa ni ne shi. Kafin ni babu allahn da aka siffanta, ba kuwa za a yi wani a bayana ba.
11 I am God; and beside me there is no Saviour.
Ni kaɗai, ni ne Ubangiji, kuma in ban da ni babu wani mai ceto.
12 I have declared, and have saved; I have reproached, and there was no strange [god] among you: you are my witnesses, and I am the Lord God,
Na bayyana na ceci na kuma furta, Ni ne, ba wani baƙon allah a cikinku. Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “cewa ni ne Allah.
13 even from the beginning; and there is none that can deliver out of my hands: I will work, and who shall turn it back?
I, kuma tun fil azal ni ne shi. Babu wani da zai amshi daga hannuna. Sa’ad da na aikata, wa zai iya sauyawa?”
14 Thus says the Lord God that redeems you, the Holy One of Israel; for your sakes I will send to Babylon, and I will stir up all that flee, and the Chaldeans shall be bound in ships.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, “Saboda ku zan aika Babilon in kawo dukan Babiloniyawa kamar masu gudun hijira, a cikin jiragen ruwa waɗanda suke taƙama da su.
15 I am the Lord God, your Holy One, who have appointed for Israel your king.
Ni ne Ubangiji, Mai Tsarkin nan, Mahaliccin Isra’ila, Sarkinku.”
16 Thus says the Lord, who makes a way in the sea, and a path in the mighty water;
Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya yi hanya ta cikin teku, hanya ta cikin manyan ruwaye,
17 who brought forth chariots and horse, and a mighty multitude: but they have lain down, and shall not rise: they are extinct, as quenched flax.
wanda ya ja kekunan yaƙi da dawakai, mayaƙa da kuma ƙarin mayaƙa tare ya kwantar da su a can, ba kuwa za su ƙara tashi ba, ya kashe hayaƙi daga lagwani,
18 Remember you not the former things, and consider not the ancient things.
“Ku manta da abubuwan da suka riga suka faru; kada ku yi tunanin abin da ya riga ya wuce.
19 Behold, I [will] do new things, which shall presently spring forth, and you shall know them: and I will make a way in the wilderness, and rivers in the dry land.
Duba, ina yi abu sabo! Yanzu yana faruwa; ba ku gan shi ba? Ina yin hanya a cikin hamada rafuffuka kuma a cikin ƙeƙasasshiyar ƙasa.
20 the beasts of the field shall bless me, the owls and young ostriches; for I have given water in the wilderness, and rivers in the dry land, to give drink to my chosen race,
Namun jeji suna girmama ni, diloli da mujiyoyi ma haka, domin na tanada musu ruwa a hamada da rafuffuka a ƙeƙasasshiyar ƙasa, don a ba da abin sha ga mutanena, zaɓaɓɓuna,
21 my people whom I have preserved to tell forth my praises.
mutanen da na yi saboda kaina don su furta yabona.
22 I have not now called you, O Jacob; neither have I made you weary, O Israel.
“Duk da haka ba ku kira bisa sunana ba, ya Yaƙub, ba ku gajiyar da kanku saboda ni ba, ya Isra’ila.
23 You have not brought me the sheep of your whole burnt offering; neither have you glorified me with your sacrifices. I have not caused you to serve with sacrifices, neither have I wearied you with frankincense.
Ba ku kawo mini tumaki don hadaya ta ƙonewa ba, balle ku girmama ni da hadayunku. Ban nawaita muku da hadaya ta gari ba balle in gajiyar da ku da bukatar turare.
24 Neither have you purchased for me victims for silver, neither have I desired the fat of your sacrifices: but you did stand before me in your sins, and in your iniquities.
Ba ku saya wani turaren kalamus domina ba ko ku gamshe ni da kitsen hadayunku. Amma kun nawaita ni da zunubanku kuka kuma gajiyar da ni da laifofinku.
25 I, [even] I, am he that blots out your transgressions for mine own sake, and your sins; and I will not remember [them].
“Ni kaɗai ne na shafe laifofinku, saboda sunana, ban kuma ƙara tunawa da zunubanku ba.
26 But do you remember, and let us plead [together]: do you first confess your transgressions, that you may be justified.
Ku tunashe ni abin da ya riga ya wuce, bari mu yi muhawwara wannan batu tare; ku kawo hujjarku na nuna rashin laifinku.
27 Your fathers first, and your princes have transgressed against me.
Mahaifinku na farko ya yi zunubi; masu magana a madadinku suka yi mini tayarwa.
28 And the princes have defiled my sanctuaries: so I gave Jacob [to enemies] to destroy, and Israel to reproach.
Saboda haka zan kunyata manyan baƙi na haikalinku, zan tura Yaƙub ga hallaka Isra’ila kuwa yă zama abin dariya.

< Esias 43 >